Showing 207001 words to 210000 words out of 255288 words

Chapter 70 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1399

cika saboda anan sarki ke sallah da sauran dattijan gari,
Mahaifin jibrin da yawa daga cikin makwabtan su suna acikin sahun da suke kusan gaba, gaba,
Bayan an idar da sallah jama,a suna kokarin wuce wane sukaji wani bawan Allah mai zakin harshe yana cewa don Allah a,dakata ,
Akwai daurin aure ga wanda Allah yaba ikon tsayawa,
Hakan yasa jama,a da dama suka dan dakata don su sheda wanan daurin auren, da akai shela,
Mahaifin Jibrin tare da, malam Abdulsamad suka matso kusa da liman nan shima Mahaifin su maryam tare da sauran yan uwan shi har su, mijin mahaifiyar ta da ya aikawa yana son yazo ciin gari a yau,
Yakuma zo din duk suna gurin su malam A, A da su KB wanda shima yazo garin saboda matar shi da take dauke da tsohon cikki,
Anan ka gudanar da shardan aure kamar yadda aka sharida wa musulumi, ci, da sha da sutura,,
Sanarwa kawai sukaji mai fada na fadin cewa an daura auren Yusuf da maryam akan sadaki naira dubu hamsi, kacal,
Inda mahaifin Jibrin din ya gabatar da kudin a hannun waliyin auren maryam din watau mijin mahaifiyar ta da malam aminin shi,
Ba,a dauki wani lokaci ba wasu mutane suka gane ko auren wa akadaura a lokacin,
Ciki har da A,A dasu KB da sauran abokan hurdan Yusuf din,
Ba,karamin mamaki mutanen da suka halarci daurin auren sukayi ba don basu da wani masaniya akan zancen auren, shi,,,,,,


ZEEE MAKAWA YALWA,
[4/28, 5:40 PM] β€ͺ+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
8⃣3⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA,
YAURI

YA,Allah, Ya Rahaman Ya Rahimee, Ya Maliki, Ya Salam, Ya Fattahu, Ya Haiyyu, Ya Kaiyyumu, Ya Malikil, Mulku,Zullani Wal,ikiram,
Allah kasa mudace ya,Allah kasa mugama da duniyan mu lafiya, Allah ka rahama muna,πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘

Kiran layin wayan shi yake yi a gagauce tun bayan minti goma sha da suka wuce,
Amma layin baya shiga sam switch, off suke cewa tun dazu,
Ba halin shi bane hakan sam rufe waya don haka yake mamakin abinda ke faruwa,
Layin Jibrin ne yakira don ya ji ko Yusuf din lagiya yake ya kashe duk layin wayan shi,
Kira guda layin Jibrin din yashiga sallama tare da yar raha kamar yadda,suka,saba,
Amma wqnan karon Jibrin din kawai keyi shi KB yaki mayar, mai da martani kamar yadda,suka saba,
Sosai abin yabashi mamaki don ba irin haka suka,saba yi a tsakanin su ba,
Kai ina mutumin yashigane wai duk wayoyin shi a kashe tun dazu,?
Au Yusuf kakw magana gaskiya ban da masaniya don dai jiya yana hanyar shi ta,dawowa kano mukayi magana, dashi,
Amma yanzun nake son daga nan mosque in wuce gidan shi in mai sannu da zuwa,
Ke nan kana da labarin auren shi kai ko ?
Ban fahince ka ba in Jibrin wanda tambayar ta KB tazo mai wani iri,
Aure ?
Wayai aure kake nufi wai ?
Ansa yabashi dace wa wai kaima kana nufin kace min baka da labari,
Bayan mahaifinka ne yai waliyin auren da aka daura mai a massalacin jumma,a dazun nan,
Mamaki kwarai Jibrin din yayi sai kuma ya kama tambaban ko da wace ce aka daura auren,

Zaune yake a gidan inuwan wani ice dake cikin gidan man nashi can gefe guda , yana kallon duk wani mai shige da fice a haraban gidan man,
Mutun biyune saman wata tsohuwan mashin suzuki blue,
Tunda Mr Emanuel ya hango su ya daure fuskan shi,
Saboda suna daga cikin masu zuwa gurin shi yawon maula,
Hakan yasa yana hangosu ya daure fuskan shi saboda yana bakin cikin irin wanan halaiyan na irin mutanen nan masu yawon maula,
Gaisuwa,sukafara dashi tare da tambayar lafiyan jikin sh,
Daya daga cikin mutanen ne kecewa Mr Emanuel din wanda ya,daure fuskan shi tamau, don kada su ji dadin rokin shi,
Mutumin yace ashe yaro ya yi aure shine muka ce bari muzo muyi ma murna,
Mr Ema yace cikin kada kan shi wa ?
Ummmmm, Ummm ba yalo namu bane,
Shiru mutanen sukayi sai zuwa can gudan yace yaron kane mana wanda ya musulunta kwanakin baya,
A,a yana kada kai alaman bashi bane, cikin daurewa fuska,
Mutumin ya dage da cewa shine fa wanda akecewa Yusuf Joseph,
Gaban tsohon ne yaba ba da damm, saboda bai taba zaton haka daga dan nashi ba,
Indan ko har hakane plan din su akan Yusuf din ya rushe ke nan,
Don tun da har yaji cewa anyi aure tsakanin shi da diyan musulmai, yasan cewa mawuyacin abu ne, kuma ya dawo cikin su ,
Don haka bai tsaya sauraren wani abinda zasu ce ba yadogara sandar shi ya mike tsaye,
Fuuuu yabar gurin batare da ya tsaya takan mutanen ba,
Inda haushi yakama su don su azaton su zasu samu kyauta a gurin shi,

Kusan kowa da yadace ace ya kirashi a lokacin da ake bukata samun shi a layin amma layi. Nashi yana a kashe duk wanda yakira shi bai samun shi,
A hankali yake saukowa a matakalan jirgin inda yake saye cikin bakar corth da wandon su,
Bai riko komai ba a hannun shi sai wata yar karamar briefcase da ke rike a hannun shi,
Enoc ne ya iso don taron maigidan nashi wanda yadan dade bai shigo Lagos din ba,
Cikin farin ciki suka gaisa inda yake mai sannu da zuwa a cikin mutunci,
Sun isa gida lafiya inda yasamu gidan shi lafiya lau kamar yana aciki ko yaushe,
Wanka ya fada ya tare da dauro alwala, bayan yafito ne yai sallah tare da mikewa zuwa falo don yaci abinci,
Cibi uku kawai yayi sai yaji karan wayan Enoc wanda matar shi takira a lokacin,
Sai a lokacin wayar shi da take a kulle tun jiya tafado mai arai,
Briefcase din shi ce yasa a miko mai yaciro wayan a ciki,
Sakon nai da miscalls ke ta baiyyana a cikkn wayan nashi a lokacin da ya kunna ta,
Sakon da yafi daukan mai hankali a,lokacin shine wanda akace idan yabude waya yakirashi pls KB da Jibrin,
Cikin sauri yafara dialing din nomban Jbrin din amma busy yake,
Don haka yakira na KB kb wanda yana gida tare da matar shi ya dauki wayan cikin fada yace, duk da sallaman da Yusuf ke mai cikin taushin harshe,
Kaga daman kun,na wayan, yanzu ko ko angwanci baka fara ba amma ka fara kashe waya,
Murmurs shi yaiwa KB din kawai batare da yasan ko may yake nufi da zancen shi ba,
Yusuf yace kai anfada maka cewa kowa irin kane daga yin aure kakoma baka son zama gurin aiki,
Na bincika ko kana Abuja ance min katafi kwantagora ai,
KB ya din ce au dama sai jiya kaso ka fada min cewa zakai aure ko,?
Aure inji Yusuf din wanda ya tambaya cikin mamaki,
Kai kaidai kila sai na fada wa Jibrin cewa aima rukiya akan wanan auren da sha ma kai, Yusuf din ke fadawa KB din hakana,
Jin called din Jibrin da yayi ya shigo yasa shi katse layin KB din don sam bai fahinci abokin nashi ba yau,
YJibrin yace ango kasha mai,,,,,
Hmmm yace kawai da ya ji abinda jibrin din ya fada,mai,
Zancen ku gudane da KB din yau ashe yanzu ya bugo min waya ba wani abin da yake iya cewa sai zancen aure,
Jibrin yakira Yusuf cikin wani irin soft voice saida Yusuf din yagane cewa something serious zaice mai,
Ya akayi ne man inji Yusuf din ya tambaya cikin taushi,
Kana inane yanzu inji Jibrin yana tambayar Yusuf din?
Ina Lagos yace a,takaice kawai, batare da ya wani zaci komai ba,
Shitt inji jibrin din abin yaba Yusuf mamaki don yasan cewa ba halin jibrin bane hakan,?
Man wai wacece ka aura ne pls,?
Jibrin din ya,sakowa Yusuf tambayan da yaji ta a bazata,
Ban fahince kaba fa inji Yusuf din yacewa Jibrin din,
Jibrin yace to be serious yau andaura ma aure a massalacin Jumma,a ,
What's cikin wani irin murya da har sai da ta razana Jibrin din,
Gaakiya inji Jibrin yace a bisa wakilcin mahaifina da malam Abdulsamad
WARA,FA,A,NAHU, MANKANAN ALLIYAN,, Yusuf yace a lokaci guda,
Yai shiru can yace HASBUNALLAHU WA,NI,IMAL, WA,AKIL
Jibrin yace wai kana nufin baka da labari Yusuf ko may wai ?
A hankali cikin wata irin murya karara yace wlh banda labarin wanan zancen,
Don ban masan anyi ba ni,
Kit, ya kashe wayan ga sanyin AC a falon amma wani irin zufa ne yaji ya karyo mai a goshin shi,
A hankali yadan rike gefen kujerar da yake a zaune inda ya fara hawan steps din da zai sada shi da dakin shi a hankali,
Tafiya yakeyi kamar mai ko yon tatata, don da kyat ya ke iya daga kafan shi zuwa saman,
Saman gadon shi yafada jagwal kamar wanda kwai ya fashewa acikki,
Aure, Aure ? To da wacece haka da har ban sani ba ,
Idon shi ya mayar ya rufe a hankali, Aisha, no no
Sadiya never yace cikin juya kan shi,
Maryam maryam yakar furta wa a fili, sai yace sam ba,zata yarda ai muna aure a haka ba,
Don har yanzu bawai ta yarda da shi bane ai balle a daura masu aure,
Ina ba ita bace saboda sam hakan baima yu,yuwa ai don shi yanzu maryam tafi karfin shi zai barwa aminin shi kuma ogan shi,
Wanda yakewa kwadayin shiga musulunci very soon,
Who the he'll is she. ?,,,

Maryam ta zaune gurin da ta idar da sallah tayi addu,an fatan alheri dakuma neman kariya agurin Allah,
Tana jin muryan Anty Dije da yaran ta afolo suna magana akan wai abinci yayi yaji yau,
Ita dai batace komai ba saboda damuwan dake damun ta a cikin zuciyar ta,
Sallaman matan gidan su suka ji sai kuma abayan su baba matan guda tana dauke da kwandon goro a kan ta,
Γ€nty Dije ce eace ke cewa mama kune tafe da ranan nan haka lafiya dai ko ga ku da kwandon goro, mana,
Marya wace take saye da hijabin ta har kasa saidai fuskan ta ya koma wani dan fayau , da shi,
Har kasa takai tagaida su daya bayan daya,,
A hankali ta mike tsaye daniyar barin falon don bata san ko may yakawo su ba,
Muryan baba yaji yana ce mata ta dakata, kada ta tafi tukun,
Komawa tayi gurin da ta tashi takara dan zaunawa a wanan karon,
Saidai atakure take gaban ta nadan faduw kadan kadan,
Ungo nan maryam inji mijin mahaifiyar ta wanda ke gefen baba sam maryam bata san cewa dashi akazo ba sai yanzu,
Da sauri tadago kai don taga ko may ye yake cewa wai ta karba,
Kudine amma acikin envelop suke dan nawan karba tayi kamar yadda ya umurce ta da ta karba wai,,
A hankali takai hannun ta takarbi kudin babane yai gyaran murya yana cewa Alhamdullahi,
Maryam maryam din jin ankira sunan ta tadan dago kanta ta kalle shi a hankali,
Ya ce karbi wanan rike tukun,
Ta mika hannu a hankali ta karbi kudin hannun mahaifin ta,
Yace to madallah ina Dije anty tace na,am baba yace Sadakin maryam ne nan na mika mata,
Daga maryam har Anty dije cikin wani irin tashin hankali hankali suke kallon baba, din,
Ba dai kr azaune ya na gyada kai, yace kwarai kuwa don dazun nan aka daura wa maryam din aure da yaron nan,,,
Dammm gaban maryam din ya harba a lokaci guda dakin taga yana juya mata a lokaci guda kunnuwan ta yai mata wani kara tsuuuuu daga haka bata kara sanin inda take ba,
Da,sauri Anty da kishiryar maman ta sukayo kanta ,
Ruwa masu sanyi a ka watsa mata, ajikin ta har zuwa kan ya hankan yasa ta sauke wani irin ajiyan zuciya mai karfi,
Da sauri ts bude idon ta da suke a rufe tana tambayar baba ni bani maryam ka daurawa aure,
Anty tace mata cikin kulawa, maryam kwantar da hankalin ki don baba ya tafi,
Hannun Anty din maryam takamo tana cewa, Anty mafarki nakeyi ko, ?
Ya baba zai mun haka anty komai nawa daban baba ke mun,
Da sauri anty dije ta kwabe mata baki tana cewa,
Baki da hankali ko kuwa babane kike nufin cewa bai son ki ko kuwa,
Kuka wi, wi, wi maryam tasa a lokacin ta kwanta bisa kafadan anty
Duk da Anty najin kukan har kasan zuciyar ta amma sai ta kyale maryam din a jikin ta koda hakan zai iya sa taji dan relief,

Mahaifin Jibrin dattijon,
yar shi ta,bashi shawaran daya kira don yaji ko may ke gudana,
A hankali Yusuf ya jawo wayan shi don ya kira, dattijon,,
Sai da yatabbatar da cewa yanzu dattijon ya dawo gida da ga massalaci,
Mahaifin jibrin din yana zaune ya jawo tiren abincin shi a gaban shi don yaci,
Hannun shi ya fara wanke yayin da kiran Yusuf ya shigo wayan nashi,
Cikin sauri mahaifin Jibrin din ya dauko waya, ya karba kiran,
Gaisawa suka fara yi a cikin mutunci nan yake tambayar Yusuf ko yana ina me yanzu,
Yusuf din yabashi ansa da cewa yana Lagos ne ai ,
Tau inji mahaifin jibrin din wanda ke kokarin bude kulan abincin dake gaban shi,
Kamshin mashanu ya na tashi wanda yasa dattijo dan lumshe idon shi,.
Yaushe zaka dawo inji mahaifin jibrin din Yusuf ya ba shi ansa da cewa
Sai nan da kwanaki don yazo yin wasu aiyukane idan yagama zai shigo,
A zaton shi dattijon zai mai bayani akancewa ga yadda maganan take ,
Amma sai kawai yaji yana mashi fatan Alheri a rayuwa tare da fatan gamawa lafiya,


ZEEE MAKAWA YALWA
[4/28, 5:40 PM] β€ͺ+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
8⃣4⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAURI

Barka da jumma,a yan uwa Allah ya sada mu da alherin dake cikin wanan ranan,,,,,,,,,,
RAMADAN KAREEMπŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘


Kwance yake saman tafkeken gadon shi mai cin kusan mutun biyar,
Barci yake son yi saboda jikin shi akwai a gajiya, amma yakasa saboda tunanen da yasha mai gaba,
Kara juyawa yayi ko zai samu barcin yazo mai amma ina yakasa
Mikewa yayi daga kwanciyar dayake ya sauko da kafafuwan shi kasa a hankali,
Anty Dije ce ta fado mai arai agurin ta zai samu amsar damuwar shi,
Kan shi yadaga a hankali ya kalli agogon dakin goma saura nadare don haka baya son ya takura mata,
Balle ma matar aure ce duk kiran da zai mata da ranane ko kuma idan tana da magana itace kan kirashi da dare,
Gurin window dakin ya nufa inda ya yaye labule ya zuge glass din a hankali,
Wani irin fresh air ne ya shigo dakin a lokacin maidadi ya bude hancin shi ya shaki iskan ya dan lumshe idon shi,
Ya dan kai wani lokaci agurin tsaye yana kallon yan motocin dake wucewa a titin jefi,jefi,
Tsayin mintoci yana tsaye a gurin har na,wani lokaci sai kuma ya maida window yarufe kamar yadda yake da farko,
Bathroom ya shiga inda watsa ruwa da kuma dauro alwala, don yai sallah nafila kafin ya kwanta,
Wanan nafilan da yayi yasa shi samun relief mai sosai
Don yayi barci mai nauyi har da mafarkin wata,zukekiyar yarinya tana shayar dashi wani abu mai dadi a cikin cup din tankagaram mai daukan ido,
A daidai lokacin da yake kokarin dago kan shi ya kallo fuskan yarinyar sai kawai yaji wayar shi tana kuka acikin daren,
Cikin jin haushin wanda duk ya katse mai wanan mafarki mai dadi da shiga rai da yake yi, ya farka,
Hannu ya mika daidai gurin da wayan shi ke caji ya dauko wayar acikin kasala don duk jikin shi a mace yake jin shi,
Samuel ne ke kiran shi da sauri ya duba time karfe biyu da wani abu na dare,
Cikin sauri ya mustsike idon shi, babu abin da ya fado mai a rai kamar Dady shi,
Don har gobe yana mutuwar son mahaifin shi a rayuwar shi,
Fatan shi Allah ya nufi dad din shi da musulunta a rayuwar, shi,
Yana daukar wayan muryan Samuel din ne cikin daga murya yake cewa,
Brother Dad baia lafiya tunda rana yadawo daga filling station,
Yana kiran sunan ka yana cewa ,Na, lie, Joseph no, go, marry, just like that, yana ta shan giya, ko na karbe, sai ya ansa ya sha,,
Yanzu dai gashi har ta kai, jikin shi duk ya sake bai masan inda yake ba ga jikin tsufa,
Yusu ya ji wani irin zafin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login