Showing 30001 words to 33000 words out of 270744 words
adduo'i take yi tare da askar har tsawon good 30 mins. Sannan ta shafa tare da mikewa ta dawo kusa da su.
Suna ƙoƙarin matsa mata, dan ta zauna a tsakiyarsu, sai ta wuce ta zauna a saman bedside drawer.
"Momma ki dawo saman bed mana?". Cewar Areef. Girgiza kai ta yi tana faɗin "Bari na zauna a nan, zan fi jin daɗin ganin fuskokinku da kyau". "To shikenan ai muma a wajen zamu fi jin daɗin ganinki our pleasure".
Murmushi ta ɗan yi kafin ta ce "Son lafiya kuwa?". Ta yi maganar tana kallon Lion.
Shiru ya ɗan yi na ƴan mintoci da ba su biyu ba, kafin ya amsa mata da "Nothing mum".
Dawo da kallonta a kan Areef ta yi, girgiza mata kai ya yi yana nuna mata alamar shi fa Lion haka yake da rashin magana, dan haka kada ta wahalar da kanta ma wajen yin tunanin ko dai wani abin ne yake damunsa, haka Allah ya yi shi. Jinjina kai ta yi alamar gansuwa.
"Son ya daddyn naku yake? Kun duba shi kuwa?". Ta sake tambayarsu
Sai a lokacin ya ɗago da dara daran idanuwansa a kanta. Allah sarki soyayya, hakika Gwaggo tana tsananin son Dr har gobe, duk wannan abin da ya yi mata a baya, amma ta kasa samun natsuwa a yanzu dan yana cikin wani hali, ba zata iya sharesa yana cikin ciwo ba.
Sam bata bawa Lion mamaki ba, dan dama a yanayin tarihin soyayyarsu, ya san fin hakan ma Gwaggo zata aikata, hakan ce ma tasa ya kula da lafiyar Daddyn nasu, ashe fitar da ya yi ɗazun, zuwa ya yi ya bashi kula tare da allurai, dan yasan confirm sai gwaggon ta tambayesu, ga shi kuwa ta kasa hakuri sai da ta tambaya.
Jinjina mata kai ya yi yana faɗin "Yeah mum, na kula da shi". "Kai Dr ne?" Ta tambaya tana dawo da kallonta a kan Areef. "No mum, but na yi karatun a wajen daddyn".
Ji ta yi tamkar ta ce musu zata je ta duba shi da kanta, zata bashi kulawa a matsayinta na Dr, sai kuma ta share, ta danne tare da kawar da zancen da cewa. "To shikenan ya kamata ku ci abinci ku kwanta ku huta ko?".
Jinjina mata kai ya yi tare da faɗin "Where is Meesha?".
Sai a lokacin ma ta tuna ashe babu kowa a gidan sai ita kaɗai, su Rimshan duk sun bi iyayensu, sai a lokacin kuma ta tuna ashe a labarin da Jehan ta bata, Rimsha matar Lion ɗin ne, ashe auren ta zo rabawa zancen ta sauya, sai yanzu ta tuna komai, lallau kuwa.
"Son dama kai ne mijin Siha na ko?". Ta tambayi tana kallon shi.
Bai amsa mata ba, kuma bai sake ɗagowa ya kalleta ba. Areef ne ya amsa mata da e.
Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Ban ji motsinsu ba, kila sun bi su yaya babba ?".
Nan ma shiru Lion ya yi yana kallon kasa, bai sake yin magana ba.
Areef yana ƙoƙarin sake yin magana Aseef ya katse su da cewa "Kai momma har da Heartbeat ta bi su?".
Jinjina mashi kai ta yi tana faɗa mashi ai dukka suka tafi. Mikewa zaune ya yi yana faɗin "Wlh i can't believe it! A kan me zata je wani waje kuma bata gaya mani ba? Ni wlh ba zai yi wu ba, gaskiya dole na je na ɗaukota!".
Murmushi gwaggon ta yi tana faɗin "Yau dai sai ka hakura ka barta da iyayenta, murna take yi na ganin kakanta da sauran ƴan uwa, nima ba dan murnar ganinku ta fi yawa ba, ai da ba zan zauna a nan ba!".
Kuka ya saka mata yana faɗin "Allah momma ni ba zan yarda ba, dole sai ta dawo yau, kuma sai na yi punishing nata, dama da safe ta yi mani laifi".
Dariya kaɗan gwaggon ta yi dan ta ɗauka wasa yake yi, bata san halin ɗan nata ba, bata san rigimarsa ba, ai yau idan ba dawo mashi da Akila aka yi ba, to ba zaman lafiya, wannan kuka ya rinƙa yinta kenan har washegari.
Waya Lion ya ɗauka ya fara kiran number Mark. Bugu ɗaya ya ɗauka. A takaice ya ce ya kawo masu abinci cikin ɗaki, sosai Mark ɗin ya yi mamaki, dan ya jima rabonsa da ya kawowa Lion ɗin abinci, sai dai ya girka kawai.
After some minutes Mark ya shigo masu da abinci kala kala, a saman carpet ya jere masu.
"Momma let's eat". Cewar Lion ɗin, ya yi maganar tare da miƙewa ya isa ga abincin.
Make kafaɗa Aseef ya yi yana faɗin shi wlh ba zai ci ba, dole sai Akila ta dawo. Da kyar gwaggo ta rarrasheshi ya sauko, shi ko Lion ko a jikinsa, Areef ma dai bai wani kula shi ba, dan suma dukkansu kusan hakan suke ji. Shi Areef baya jin zai iya barci ba tare da ya kalli face ɗin Jehan ba, shi kuwa Lion barcin ne ma kwata kwata ba zai iya ba idan ba tare da Meesha ba, dan sun saba kwana gado guda da ita a cikin jirgin ruwa, Areef dai Allah ya taimaka dama bai taɓa kwana da ita ɗaki ɗaya ba. Shi kam Aseef na shi ai kun sani dama na daban ne, yanda suke kashe juna da love da shagwaɓa ko wani dare shi da Heartbeat nasa, yau kawai ta gudu ta barshi, ai ba zata saku ba........... E KAM BA ZATA SAKU BA, AMMA KUMA TA TAFI ƊIN😂YO ME RUWA NA NI? KO YA KUKACE MASU KARATU? ME RUWANMU? AI NAMU IDO.
A tare suka fara cin abincin suna hira sama sama, Areef ya fi sakewa ya biyewa gwaggo suna zuba hira, shi kuma Aseef sai wani kumbure kumbure yake yi, shi a dole ran maza ya ɓaci, Akila ta bijire umarnin miji. Lion kuwa ba sai na faɗa ba, kun sani, magana ce baya so.
A ɓangaren su Rimsha kuwa. Bayan sun isa gidan Abba ne daddynta ya ganta, faɗa sosai ya fara yi masu akan me za su baro mazajensu, su biyo su?. Kuka ta sakawa daddyn nata sosai, kuka ta gaske mai sauti da iya karfinta.
Nan take kowa ya fara tambayarta lafiya kuwa? Me ya sameta take kuka?.
Cikin kuka ta fara magana da iya gaskiyarta, tana yi tana kara sautin kukan nata. "Daddy wlh bana son yaya Saif, ni ba zan zauna da shi ba, ba zan sake zuwa in da yake ba, ba ruwana da shi, ba zan sake zuwa gidansa ba, dan girman Allah daddy kada kace na koma can, wlh zan mutu, ni bana son shi....." BABBAR MAGANA.
Bata gama rufe baki ba Akila ta karɓi zancen da cewa "Wlh nima daddy bana son heartbeat, ni kawai na dawo gidanmu, wlh ba zan koma ba".
Yau ga ikon Allah su daddy suna gani, sun ma rasa abin faɗe.
Jehan ce ta katse su da cewa "Ku da dama kuke sonsu kenan, ai ni dama tun ainahi bana son shi, daddy ne kawai ya wani kakaba mani shi, kuma wlh yanzu ba ni babu shi, ya san in da dare ya yi mashi". To fa, yau ga ikon god.
Ɗaure fuska sosai daddyn ya yi zai fara magana kenan Brr Naurat ta riga shi da cewa "To shikenan tun da baku son su, ku je ciki ku ku ci abinci, sai ku kwanta ku yi barci, da safe sai mu yi maganar ko". Brr Naurat akwai saurin gane abubuwa, ta gane me matsalarsu, dama ita da kanta ta yi danasanin labarin da gwaggon ta bayar a gabansu, ta san dama hakan zata iya biyowa baya, ta zan za su guji mazan nasu, dan za su yi tunanin irin abin da ya faru da gwaggon, abin da Dr William ya yi mata na cin amanar soyayyarsu, za su yi tunanin suma haka su Lion ɗin za su yi masu, tun da duk Turawan ne. TO FA BABBAR MAGANA, E DAMA DOLE ZA SU JI HAKAN AI, SABODA YANDA DR WILLIAM YA NUNAWA GWAGGON TSANTSAR SO DA KAUNA, DAGA BAYA YA CI AMANARTA, AI DOLE SU RIMSHA SU KARAYA, BARE MA ITA RIMSHA DA DAMA LION BAI TAƁA CEWA YANA SONTA BA, KUNGA KUWA AI DOLE TA GUDU DAN TA RUFAWA KANTA ASIRI, KADA TA FAƊA IRIN TARKON GWAGGO, SUN MANTA LAIFIN WANI BAYA SHAFAN WANI, SUN MANTA KOWA DA IRIN HALINSA, AMMA BA ZA KU GA LAIFINSU BA, SUNA A KAN GASKIYARSU NE❤️
Daddyn Rimsha ne ya ce "Mum zamu wuce dasu gidana na nan Kd, dama a gyare yake, nan gidan ya yi mana kaɗan, gobe da safe zamu zo". To Brr Naurat ɗin ta amsa mashi da shi, sannan ta kira shi gefe a in da ta gaya mashi kada ya yi wa su Rimsha tsawa ko faɗa a kan cewa da suka yi ba su son mazajensu, ya kyalesu zuwa gobe idan sun zo, ita zata yi magana da su. Okey ya amsa tare da yi wa su Abba sallama ya kwashesu, Rimsha, Jehan, da kuma Akilar, sai mum, suka wuce gidan nasa.
Daddyn Anaya ma, ya koma gidansa da iyalansa, saura su Abbi, daddyn jelly sai Abban, Aunty ma tana nan, ita kuma Hjy Hadiza tana gida. Sune suka kwana a gidan Abba tare da Brr Naurat, kwana suka yi suna ta zuba hira.
Su daddyn Rimsha kuwa, bayan sun isa gida, abinci daddy ya fita ya sawo musu, suka ci suka kammala, ko wacce ta yi wanka ta yi shirin kwanciya, da yake gidan yana da matuƙar girma, ga yelwar ɗakuna da abubuwan more rayuwa, sai kowacce ta wuce daɗinta daban, ita kuma mum ta bi daddy abinta, dan suna bala'in kewar juna.
Duniya dukka sun yi barci Rimsha da Akila sun kasa yin barci, kuka yarannan suke yi tamkar za su mutu, tun hawaye na fita, har ya dai'na fita, yanda suka ga rana, haka suka ga dare, ba barci, amma duk da haka sun ki yarda ko kiran mazan nasu a waya su yi, kashe wayar tasu ma suka yi, Lion ya nemi number Rimsha a kashe, shi ma Aseef ya kira Akila a kashe, ga shi gwaggo ta hanasu zuwa su ɗauki matan nasu, ta ce yau su hakura, haka suma suka kwanta cikin kaɗaici da kewar matan nasu.
Ita kuwa Jehan wlh ko a jikinta, barci ta yi har da manta a wani duniyar take, shar zuciyarta, ta bar Areef da kwana kallon hotonta bawan Allah.
KAI JAMA'A YARANNAN SU RIMSHA SUNA SHA'ANINSU WLH, WAI YAU RIMSHA CE ZATA CE BATA SON LION?🤔😂 A LALLAI KUWA, AKWAI KALLO GOBE, GA SHI DAI KWANA ƊAYA KAWAI TA KASA HAKURA, SAI KUKA TAKE YI, INA GA KUMA ANYI SATI? INA GA SAI GADON ASIBITI ZA'A WUCE DA ITA😂AMMA KUMA SUNA DA GASKIYA, SU TSARE KANSU, KADA ABIN DA YA FARU DA GWAGGO YA FARU DA SU, INA GEFE NI DAI!!! JEHAN KUMA ƳAR DUNIYA, KO A JIKINTA😂 KAI LITTAFIN TRIPLETS AKWAI ƳAN AIR WLH😂 SU HEARTBEAT MA DAI AN KASA BARCI😂 KO YA ZA SU YI GOBE IDAN SUKA FITO DADDYNSU YA KALLI IDANUNSU A KUMBURE SABODA KUKA? ME ZA SU CE IDAN AKA TAMBAYESU A KAN HAKAN?😂!!!.
❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥
*KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔
ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*.
*KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA,
INFECTION KILLER,
COLACCA,
SAI KAYAN GYARA PAGE.
KACA KACA.
YALLAGWADA.
JIGIDA.
RUWA RUWA.
BANI BANI.
WOMEN JELL BATA BATA.
DAFIN KAXA.
TANTABARA.
XABUWA.
CICCIƁI.
AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER
09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH,
BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*.
❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥
https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S
❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥
TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️
❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋)
*Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581*
E6
Washegari, kasancewar mum ta san babu kayan abinci a gidan, sai bata yi ƙoƙarin tashi ta haɗa masu breakfast ba, ta bari su je gidan Abba or restaurant su karya, kwata kwata ma bata fito daga daɗin daddyn ba, suna a tare manne da juna abinsu, su kuwa su Rimsha, sun ci uban kuka tamkar ransu zai fita, idanu sun kunbura luhu luhu, har wani ja suka yi ta kasar fatar idanun, Jehan ƴar gwaggo kuwa, ko a jikinta, bayan ta tashi ta yi sallar asuba, sake mayar da barcinta ta yi, hankalinta a kwance.
A ɓangaren Lion kuwa, kwana ya yi bai yi barci ba, ya kwana yana tunani tare da nazari a kan zantukan gwaggo, shi ma dai Areef bai yi barcin ba, ya nutsa cikin tunaninsa a kan maganar. Abin da ya ɗaure wa Areef kai har ya sanya shi cikin tunani shi ne, meyasa Josephine zata tsanesu? Bayan kuma ita ce ta kula da mahaifiyarsu a lokacin da take ɗauke da cikinsu? Idan da tana son kashe su, ai da tun suna cikin cikin mahaifiyar tasu zata kashe su, amma bata yi hakan ba, ta kula da su sosai, sai daga baya za'ace masu ta nemi hallakasu? Anya kuwa akwai gaskiya a wannan lamari? To meyasa Dr William ya tsaneta? Meyasa ya koreta daga gidansa, bayan kuma har TRIPLETS ɗin suka ɗan yi wayo a tare suka gansu a matsayin mata da miji da Dr William ɗin? Wannan abin akwai ɗaure kai, ya saka Areef a cikin damuwa sosai, ya sanya shi shiga cikin yanayi mara dadi, ga kewar Jehan ɗinsa, abubuwa sun haɗe mashi bawan Allah!!.
Shi kuma Lion kalma ɗaya zuwa biyu ne suke mashi yawo a cikin ƙwaƙwalwasa, na farko, cewa da gwaggon ta yi TRIPLETS nata biyu daga ciki kamanninsu ɗaya, kuma dukkansu biyun blue eyes ke garesu, shi kuma ɗayan idanunsa daban, to shi dai Lion yasan su TRIPLETS da Dr William ya haifa, dukkansu idanuwansu daban daban, babu wanda idanunsu yake iri ɗaya, Areef ash eyes, Aseef brown eyes, shi kuma Lion ɗin blue eyes, kuma duk cikinsu shi kaɗai ne yake kama da Dr William kamar yanda gwaggon ta faɗa, to ya aka yi hakan ta faru?! Ina blue eyes na ɗayan?! Meyasa kuma bai yi kama da Dr William or Lion ɗin ba?! Wannan abin ya tsaya mashi a rai over, idan ya yi tunanin to ko dai ɗaya daga cikinsu Areef ba TRIPLETS nasa bane, sai kuma yaga hakan sam ba zai yi wu ba, duba da yanda suke jin bugun zuciyar juna, sannan suna da kwari da kunama, ga kuma uban shakuwa da take a tsakaninsu na wuce misali, kai bama zai taɓa yiwuwa ace ɗaya daga ciki ba cikon TRIPLETS bane! Hakan sam ba zai yiwuba! Dole dai da akwai abin da ya saɓa, kuma dole Josephine da Dr William ne za su faɗa menene ya saɓa ɗin!!. Abu na biyu da yake ta jujjuyawa a cikin ƙwaƙwalwasa kuwa, ya aka yi su Dr William suka koma Kristen? Kamkar basu taɓa musulta ba, kuma a labarin da gwaggon ta bada, har karatun Alkur'ani mai girma sun iya sosai, to ya aka yi suka canza? Canzawa mai ban mamaki haka? Ina Cherish take? Me ya rabata da su Josephine? Ina take lokacin da gwaggon zata dawo Nigeria? Waɗan nan sune tunanin da suka hana Lion runtsawa, ya rasa amsarsu, ya nutsar da brain nasa yana neman amsa cikin nutsuwa.......... NI KO NA CE AI KAI ƘWAƘWALWARKA DA BASIRARKA TA GADO CE, KA GAKI BASIRA BA KARYA, DOLE MA KA BANKAƊO GASKIYA IDAN KA SAKA KANKA, BA ABIN DA ZAMU CE MAKA FACE ALL THE BEST OUR LION!!.
Hakika kuma ya shiga damuwa na rashin Rimsha a kusa da shi, shi ne ma yasa tunanin da yake na neman amsar ta kasa gudu, ya kasa samun amsa da wuri, saboda rashin Meesha a kusa da shi babbbar barazana ce ga nutsuwarsa, hankalinsa ya rabu kaso uku, kaso biyu yana kan tunanin Meesha, ɗaya kuma tunanin su Josephine, da Rimsha na kusa, wata kila a daren zai iya bankaɗo menene gaskiya, dan ya yi alkawarin bama zai tambayi daddynsa ba, saboda yana ganin kamar daddyn ba zai gaya mashi gaskiya ba, ya ce da kansa zai bankaɗo komai da komai.
AFTER SOME HOURS.
Da misalin karfe 9 na safe, shirye cikin wando jeans mai matukar bala'in kyau, black color, da polo t-shirt fara kal, Lion ya fito daga cikin bedroom nasa, hannunsa na ɗaure da TRIPLETS watch, still sarkan nan tana wuyarsa, ya ɗaure gashin kansa a bayan wuya, sai tashin daddaɗa kuma zazzafar kamshi yake yi, ya yi matuƙar kyau sosai, sai dai da kallo ɗaya zaka yi mashi, kasan bai sami damar yin barci daren jiya ba, dan idanunsa sun yi wani kal da su, tamkar wanda bashi da lafiya, fuskarsa ta yi wani fayau da shi.
Bedroom na daddyn Rimsha in da gwaggo take ya nufa. Kasa kasa tamkar bai yi magana ba ya yi sallama, tare da shiga ciki. Areef na zaune a bakin bed nata, ita kuma gwaggon tana zaune a saman bedside drawer suna zuba hira, shi kuma Aseef yana can yana zuba barci, bai tashi ba, dan daren jiya bai yi barci sosai ba.
A tare gwaggon da Areef ɗin suka amsa mashi sallamarsa, karisowa cikin ɗakin ya yi, yana taku cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, tamkar baya son taka kasa, da alama jikinsa duk a mace yake. Gefen Areef ya zo ya zauna yana tambayar gwaggo ya ta kwana?.
Sai murmushi take yi ta amsa mashi da lafiya lou ta kwana, Areef ne ya fara ɗaga mashi gaisuwa, a takaice ya amsa da lafiya tare da miƙewa ya ce da gwaggon yana zuwa, zai je unguwa.
"A'a zauna ina son yin magana da kai!". Okey ya amsa mata tare da gyara zama. Shi kuma