Showing 87001 words to 90000 words out of 270744 words
da wuri mu fita".
Sam Aseef ɗin bai kula shi ba, ya rungume Heartbeat tasa suna kashe juna da shagwaɓa, su gabaɗaya ma sun mance a ina suke, har lokacin sai kuka take zuba mashi, shi ma ya biye mata suna wannan aiki dai da suka saba, wanda already kun san halinsu idan suka haɗu, shagwaɓa babu kama hannun yaro.
"Aseef wai ba zaka barta sai mun fita daga ɗakin ba?".
Ko ajikinsa, babu tsoro ko ɗigo a tattare da shi, cikin kwanciyar hankali ya ce "Kai Areef kasan tun yaushe ban yi kissing nata bane? Kai ba zaka bar mutun ya sakata ya wala ba, Allah ba zanzo ba sai na gama kissing nata har na ƙoshi".
Girgiza kai Areef ɗin ya yi tare da nufarsu, Aseef sai ya sa an yi masu kisan walaƙanci sannan hankalinsa zai kwanta, ban da iskanci ma irin tasa, ana ta rai waye kuma yake ta wani kiss? Ya bari su rayu mana, daga baya ayi komai, yana ganin yanda komai yake ƙoƙarin lalace masu, ga shi har yanzu basu ma san ina Lion yake ba tukunna. Yana zuwa ya ja hannun Akilar yana faɗin "Idan kika biyewa Aseef duk sai mun mutu kamar dabbobi a nan, ke daɗi masoyi ko?".
Janyota Aseef ɗin ya sake yi yana faɗin "Wai kai ka bari mana, ka sani ne ko kiss na karshe zan yi mata, idan bamu kai ga fita ba aka kashe mu kamar yanda aka kashe sauran fa? Ni ka barni na yi abinda zan yi Hai........" Bai rufe baki ba suka fara jin jijjigar ginin ɗakin, alamar suma ruguje ɗakin ake son yi da su a ciki, tamkar yanda aka yi wa su Mark kenan.
Ihu Aseef ɗin ya kurma tare da shagwaɓe murya yana faɗin "Wayyo Areef mun shiga uku, shikenan zamu mutu ba tare da Heartbeat ta haifa mani baby's ba, wayyo ni Aseef naga ta kai'na".
Wani irin harara Areef ɗin ya wurga mashi. Aseef ɗin nan mugun ɗan rainin wayo ne wlh, ji yanda yake kukan shagwaɓa kamar ba yanzu ya gama jibgan karti maza a waje ba!.
❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥
*KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔
ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*.
*KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA,
INFECTION KILLER,
COLACCA,
SAI KAYAN GYARA PAGE.
KACA KACA.
YALLAGWADA.
JIGIDA.
RUWA RUWA.
BANI BANI.
WOMEN JELL BATA BATA.
DAFIN KAXA.
TANTABARA.
XABUWA.
CICCIƁI.
AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER
09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH,
BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*.
❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥
https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S
❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥
TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️
❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋)
*Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581*
E15
Date: 25/4/2024
Wani irin harara Areef ɗin ya wurga mashi. Aseef ɗin nan mugun ɗan rainin wayo ne wlh, ji yanda yake kukan shagwaɓa kamar ba yanzu ya gama jibgan karti maza a waje ba!.
"Areef yanzu me abin yi, ni fa wlh bana son na mutu". Ko kallon arziki Areef ɗin bai yi mashi ba, bare ya sa ran zai amsa mashi, hannun Akilar kawai ya ja suka nufi kofar fita da gudun gaske, da ya ga ba zata iya gudun bama, sai ya ɗauketa cak, shi kuma Aseef ɗin yana tsaye yana zuba kukan shagwaɓa.
Bayan Areef ya fita da Akila sun tsaya a waje ne, sai ya sauketa tare da dafa kansa yana faɗin "Dama na sani ai, Aseef our heartbeat kuma our headache, wato da gaske yana tsaye a cikin ɗakin kenan? Ya zan yi dole naje na lallaɓa shi ya fito, Heartbeat ki jirani a nan". Ya kai karshen maganar tare da juyawa da sauri ya koma cikin ɗakin.
Gabaɗaya bangon ɗakin sai ruguzowa yake yi, amma Aseef yana tsaye yana zuba kukan shagwaɓa, shi dole sai Areef ya zo ya rike hannunsa shi ma, a kan me zai kama hannun Akila kawai, wato yanzu sun fi son Akila a kan shi kenan? Shi ne fushin da yake yi.
Da sauri Areef ɗin ya dawo cikin ɗakin, hannunsa ya zo ya riko yana faɗin "Shikenan muje to". Bubbuga kafa ya fara yi yana faɗin "Yanzu ka dai'na sona, sai da ka fitar da Heartbeat shi ne ni zaka ce nazo daga baya, Allah ba zan yarda ba, ni babu in da zanje, kawai ka barni na mutu tun da kun dai'na sona........". Bai kai karshen maganar ba bangon ɓangaren hagu ta ruguzo. A dubu ɗari ya rungumi Areef ɗin yana faɗin "Wayyo daddyna, wayyo my Lion, na shiga uku zamu mutu, Areef ka ceceni bana son mutuwa".
Gabaɗaya kan Areef ya kulle, wai shin Aseef ɗin nan wani irin mutun ne? Yanzu ka ganshi cikakken jarumi, anjuma kuma ya koma shagwaɓaɓɓe na kin karawa, ji yanda yake kukan baya son ya mutu, ya zo su fita kuma ya ce bai san wannan ba, shi ya yi fushi saboda an fara fitar da AKILA, yanzu kenan an daina son shi.
Shi ma Areef ɗin rungume shi ya yi yana rarrashinsa a kan ya yi hakuri su tafi to. Bai kai ga rufe baki ba kamar daga sama ya ji Aseef ɗin ya sunkuce shi, ya ɗaga shi sama sun yi waje a guje. Suna fita ɗakin ya rufta mai gabaɗaya.
Bai sauke ɗan uwan nasa a ko'ina ba sai a kusa da Akila dake tsaye tana faman sharar kwallah. Mamaki ya hana Areef ɗin yin wani kataɓus, yau kuma ko a ina Aseef ya samo karfin ɗaukarsa kamar ɗan baby kuma oho? Abin mamaki baya karewa.
Shi kuwa Aseef ɗin yana sauke Areef ɗin sai ya faɗa jikinsa yana mai cigaba da kukan shagwaɓarsa kamar ba shi ne yanzun nan ya gwada wata zazzafar jarumta ba.
Ture shi Areef ɗin ya yi ya nufi wajen su Dr Salman yana faɗin "Heartbeat dama kayanki ne, kin fi kowa sanin halinsa a yanzu, sai ku fama, ki rarrashe shi, ni bari na nemo maku hanyar fita daga wannan bakin kazamin gidan, ku fita, idan ya so zamu biyoku daga baya". Ya kai karshen maganar dai'dai lokacin da ya karisa wajen Dr Salman.
Matsowa Akilar ta yi ta faɗa jikin Aseef ɗin tana mai cigaba da zuba mashi kuka babu kakkautawa. Rungumeta sosai ya yi tare da dai'na nashi kukan ya hau rarrashinta, ta tsorata sosai baiwar Allah, ta sha wahala, duk ta fita a hayyacinta, a haka ma fa dan tana matsayin jika ga Queen ɗin kenan, ba dan haka ba, da sai yaya? Taga kaɗan daga cikin abubuwan da Rimsha ta gani, a gaban idanunta aka fasa cikin wasu mutane biyu aka ɗebi wasu abubuwa, a gaban idanunta aka shanya gawa kamar busasshen kifi, a gaban idanunta aka yi abubuwa da dama, ita ma dan Allah yasa tana da tsawon kwana ne, da ita ce a kan layi yanzu, ba dan zuwansu Aseef ba, to da ba makawa ba zata kai gobe ba.
Areef kuwa magana ya fara yi da Dr Salman a kan ko ya san wani abin dangane da gidan nan. Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Na shafe shakaru sama da talatin da uku a nan, amma har yau ba zan iya ce maka ga takamaimen abin da suke yi ba bayan kashe mutane da ɗibar jini da wasu sassa na jikin ɗan adam, sannan har yau ban taɓa ganin gini na farko ko kuma na karshe na wannan gida ba, sai dai kuma, na san da akwai wata hanya da Duna ya taɓa gaya mani, ya ce ko bayan sun ɗauke shi, idan zan iya na bi wannan hanya zan tsira daga wannan gida, sai dai kuma hanyar tana da haɗari, sannan tana da nisa sosai, kuma a karshen hanyar da kawai kofa da zata fitar da kai waje gabaɗaya, bayan hanyar da su Rimsha suka fita, wannan ita ce hanya ta biyu ta sirri a cikin gidan, sannan ya ce mani idan har ina tafiya a kan wannan hanya, to kada na juya baya, komai zan ji na tafi kawai, abin da yasa ban fita ba, saboda komai ya kare mani, ina jin ko nafita bani da kowa a duniya, kuma ya ce hanyar tana da tsawo sosai, so ba zan iya doguwar tafiya ba, ni kaɗai ne kuma, dan a lokacin, sun ɗauki mai taimaka mani ɗin, wato Mustapha, shi ne mai taimakona dama, to sun rabani da shi, sun mayar da shi cikinsu, suna can suna ƙoƙarin juyar da shi izuwa nasu, a halin yanzu ma ina ga sun mayar da shi ɗaya daga cikinsu ɗin, wannan dalili yasa na ce gara na cigaba da zama a nan ɗin kawai har ranar da rai zata yi halinta".
Shiru Areef ɗin ya yi yana jinjina wannan al'amari na Dr Salman, abin gwanin ban tausayi, shekara ɗai ɗai har talatin da uku a cikin wannan bakin azzalumin gidan? Gaskiya Queen ta azabar da bawan Allah nan, ko da ace iya ajiye shi kawai ta yi, bata yi mashi komai ba, wlh masifar da yake gani wanda suke aikatawa kawai ya isa ya kashe shi idan da kwanansa ta kare, Allah sarki, da Allah ya ƙaddara kwanansa na gaba, shi ne har ya kawo iyanzu duk da irin masifu da yake gani, Allah ne kawai zai bi masu hakkinsu, dan kome aka yi wa Queen a yanzu, wlh ba'a biya ko mutun ɗaya abin da ta yi mashi ba, yanzu a kalla ba'a akasaraba wannan Daular Mutuwar ta haura shekaru hamsin da kafata, sai Allah ne kaɗai zai iya kiyaste rayukan da aka salwantar a cikinta, ya ilahi ya lillahi.
Rugujewar sauran ɗakunan dake gefe da gefensu ne ya dawo da Areef ɗin daga duniyar tunanin da ya afka, da mamaki ya ɗago kai yana bin ɗakunan da kallo, sai rugujewa suke yi tamkar waɗan da ake jijjigewa. Anya lafiya kuwa? Areef ɗin ya tambayi kansa. Aseef kuwa kara kankame Akila dake kankame da shi gam ya yi, saboda tsoro, ta tsorata ne da ganin yanda gine ginen suke jijjigowa da kansu, sai ruguzowa suke yi, tamkar katafila ce take watsi da su.
"Aseef let's go, saboda ina ganin gabaɗaya ruguje arean nan ake son yi, so tsayawarmu a nan babban haɗari ne, ka kawo Heartbeat ta tafi da su baba ta hanyar da ya gaya mani yanzu, zamu cin masu a hanya idan mun gane a in da Lion yake". Cewar Areef kenan.
Kankameta ya kara yi yana faɗin "No Areef su baba ɗin su je kawai, ita Heartbeat tana nan tare da ni". "Aseef ba da wasa nake yi ba, kada ka yi ka salwantarwa da yarinyar nan rayuwa, ka barta ta bisu". "Nima ai Areef bada wasa nake yi ba, babu in da zata je, muna tare da ita".
Dr Salman ne ya sa baki ta hanyar cewa "Jikana da ka bari mun yi abin da ɗan uwanka ya ce, dan wannan gida ya wuci tunaninka".
"Baba ni fa ba zan rabu da Heartbeat ba, ai dama ta ce zata soni komai wuya komai daɗi, kuma idan ma aka bata zaɓi a kan mutuwa, to zata zaɓi mu mutu a tare, dan haka kunga ita already a shirye take da ta mutu a tare da ni, please kada ku dame mu, ko ba haka ba Heartbeat?". Tana daga kwance a saman kirjinsa ta amsa mashi da cewa "Haka ne, a tare zamu mutu".
Girgiza kai kawai Areef ya yi, waɗan nan sun yi nisa, sam ba zasu ji kira ba, idan ka biyewa Aseef sai ya sanyaka hawan ruwa ba na jini ba.
Tsananin jijjigar da gine ginen wajen suke yi ne yasa suka dawo cikin hayyacinsu, da sauri Aseef ɗin ya riko hannunta tare da raba jikinsu, cikin hanzari ya nufi su Dr Salman ɗin yana faɗin "Wayyo Areef menake ji da gani haka? Kada fa waɗan nan gine gine dukka su faɗo mana a kanmu, ya kamata mu gudu, dan ni dai gaskiya ban shirya mutuwa a yanzu ba, sai na sami magaji tukun nan........" Bai gama rufe baki ba gine ginen suka fara ruguzowa tamkar waɗan da karapila take jijjigewa.
Cikin hanzari da zafin nama suka yi maza suka fara ƙoƙarin barin wajen. Dr Salman ne ya nuna masu hanya, a in da suka bi ta wata kofa dake ta yamma. Suna tafiya da sauri sauri, gine ginen ɗakunan bayansu na rugujewa kamar ba lafiya ba.
Ganin Ayla zata basu matsala ne yasa Areef ya sauke jakar bayansa, a in da ya dawo da jakar ta gaba, sannan ya goya Aylar a bayansa, dan ba karya ta galabaita iya galabaita, ta sha bakar wahala, da kyar baiwar Allah take iya jan kafafunta, hakan kuma zai sanya har gine ginen su ruguzo a kansu ba tare da sun fita daga wajen ba, shi ne yasa Areef ɗin ya goyata, shi ma Aseef goya Akila a bayansa ya yi.
Sun yi tafiya mai nisa kafin su cikaro da wani ɗaki, ƴan mata guda uku ne rufe a cikin ɗakin, buɗe masu kofa Aseef ya yi, duk da basu san su ba, amma sun taimaka masu. Haka suka cigaba da tafiya, duk wani ɗaki da zasu gani, in dai da akwai mutane a ciki, to sai sun buɗewa mutanen, su ce su biyo bayansu, tun suna su kaɗan, har suka kai kusan su 40 a wannan tafiya tasu, har a lokacin kuma basu cinma wannan hanya da Dr Salman yake son nuna masu ba, wanda kuma ta nan ne kawai za su bi su fita.
A can gida kuma, abubuwa sai ƙoƙarin rikece masu yake yi, yau da wani irin azababben zazzaɓi Rimsha ta tashi, ga tsananin ciwon kai, tun safe take zuba barcin wahala, har misalin karfe 4, shi ma sai da gwaggo ta ga barcin ya yi yawa, sannan ne ta tasheta.
Tana tashinta sai kuma me? Wani sabon tashin hankali suka afka, dan kuwa Rimshar tana tashi ta fara tambayar gwaggon wacece ita? Babbar magana. Zaro idanu waje sosai gwaggon ta yi, idanuwan nata tamkar za su faɗi kasa, cike da mamaki a samar fuskanta ta ce "Rimsha ni yau kuma kike tambaya wacece ni?".
Wani irin harara ta watsawa gwaggon da waɗan nan dara daran fararen Sleeping eyes ɗin nata, ta ɗauki tsawon a kallah minti biyar kafin ta amsa mata da "E mana wacece ke? Kin wani zo ki zaunawa mutane a waje".
Shiru gwaggon ta yi, ta rasa me zata sake ce da Rimshar. A haka Brr Naurat ta shigo ta samesu. Da mamaki take tambayarsu lafiya suka yi wani cirko cirko da idanu haka.
Nisawa gwaggo ta yi tare da gyara zamanta, sannan ta ce "Mummy wai Rimsha ce take cewa bata sanni ba yau kuma".
Murmushi kaɗan Brr ta saki tana faɗin "To kin dai san halin masu ciki, wata kila yau kuma da irin halin da ta tashi kenan, ai sai ki rabu da ita ki kama wani abin ko? Idan lokacin da ta dawo dai'dai ya yi, sai ki zo ki yi mata maganar da dama zaki yi mata ɗin". Ta kai karshen maganar tare da zama a gefen bed ɗin.
Hakika dukkansu basu ɗauki zancen Rimsha na cewa da ta yi bata sannu ba da mahimmanci, gani suke yi dukka shirmene da kuma laulayin ciki, ita kuma ba wani shirme, har ga Allah da gaske take yi, bata sansu ba, gabaɗaya ƙwaƙwalwarta an ɗauke shi ne aka kifa shi, ta mance da komai na rayuwarta, da kuma kowa, ita kanta ma ta mance da ita wacece. Tashin sense!!.
Komawa ta yi ta kwanta tana wani irin ɓata rai tare da ɗaure fuska sosai. Daga gwaggon har Brr Naurat ɗin babu wanda ya sake kulata a cikin ɗakin, da haka barci ya sake yin awon gaba da ita, yau tun da ta yi sallar asuba, bata sake yin wani sallah ba, dan ita kanta bata san wacece ita ba bare ta san cewa ita musulmace ko Kristar, wannan shi ne tashin hankali, to meyasameta kuma? Wanene ya juyar mata da tunani? Meyasa aka yi mata hakan?. Ku kasance da Alkalamin FATEEMA ZAHRA MUSA, PRINCESS TEEMA, alkalamina ne kawai zai iya warware maku wannan cankwakiyar.
Hira Brr Naurat da gwaggo suka fara zubawa, ita kuma Rimsha ta mayar da barci. Baki ɗauke da sallama Jehan ta shigo cikin ɗakin.
Saman bed ɗin ta haye tare da tada kai da laps na gwaggo, da kallo ɗaya zaka yi mata kasan cewa tana cikin tsananin damuwa, har ƴar rama ta yi, ta yi wani fiki fiki da ita, tamkar ba Jehan D.P.O kuma jarumarmu ba.
Shafa kanta gwaggon ta fara yi tana faɗin "Babyn daddynta waye kuma ya taɓo mani ke?".
Tamkar jira take yi a yi mata tambaya, sai kawai ta sa kuka, hawaye wani na bin wani, Allah mai iko, yai Jehan ce take kuka da hawayenta? A lallai abu ya yi tsamari.
"Subhanallahi, Jehan lafiya kike kuka?". Cewar gwaggon. Brr Naurat ma dai abin da ta tambaya kenan, lafiya take kuka?.
Cikin kuka ta fara magana kamar haka "Gwaggo ko na kira number Yah Areef bata shiga, kuma yau tsawon kwanaki fa basu dawo ba, babu wani zancensu ma, ni na rasa ya zan yi, wlh kirjina ciwo yake yi mani, please gwaggo ki ce ya dawo, ba zan iya ba..........." Kasa karisa maganar ta yi, saboda wani kuka daya kubce mata. Soyayya muguwar wasa, ta yi mata mummunar kamu, Allah sarki baiwar Allah, ba zata iya jurar rashin shi a kusa da ita ba.
Rarrashinta gwaggo ta fara yi, yau ga uwar miji tana rarrashin matan ɗanta a kan matar tana