Showing 1 words to 3000 words out of 321579 words

Chapter 1 - Kurkukun Kaddarata Takun Karshe Complete Hausa Novel

??ࡱ?>?? D?!????????????? ?
?
? ?
?
?????????????????? ? !?!?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????!U

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?F?!WordDocument????1?B0Table?????????<Data
???????????????????? P?f?5KSKS?1?B????????????6?6?6?6?6?6? ???6?t<t<t<t<J<`< l<t<v<$?8?a;*??6?6J<J<?6?6?6?6t<?;??6?;t<?6t<?;?6t<t<?6?6 ?^`????^Normal d??,CJmH sH nHtH_HOJPJQJ^JaJhA`????hDefault Paragraph Font$mH sH nHtH_HOJPJQJ^J?i`????? Normal Table0:V 4?4?l4?4?la?6 $mH sH nHtH_HOJPJQJ^J(k`????(No List ??@?'?N8r??`?????  ,?7
I?k>??jBISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM

KURKUKUN ?ADDARA TAKUN ?ARSHE =?%?
LABARI DA RUBUTAWA HAFSAT BATURE MUHAMMAD '?

Kada ku manta da ni, Ina barar addu'ar ku, Aduk lokacin da ku ka buWe document Win nan, ku taya ni da addu'a, Ko wace kalace indai ta fatan Alkhairi ce Inaso, Sannan Littafin nan Na kuWine, da gumina na rubuta shi, Kada ki Wauki ha??in wani akanki/ka, In kasan baka Biya ba, Ka hanzarta biya ka karanta halal din ka=?M?

GargaWi da jan Kunne kar a kuskura A canzamun wani abu na Littafin nan, ko da harafi ne ta kowace siga ban amince Ayi amfani da shi ba, ina da lawyer na da kuma wadanda zasu kwatar min ha??ina, ku ji tsoron Allah, kuma kuji ta6a hakkin da bana ku ba =?M?


GA ME BUKATAR MALLAKAR KURKUKUN ?ADDARA COMPLETE 1,2,3,4, ZAI BIYA NEW PRICE DIN SHI NA YANZU 700 NE VIA FIRST BANK, ACCOUNT NUMBER 3196407426 ACCOUNT NAME BATURE HAFSAT MUHAMMAD, ZA'A TURO SHAIDAR BIYA TA WHATSAPP A TUNTU6I NUMBOBIN NAN KAITSAYE=?G?

08103884440 KO 08169856268.




=?%?=؋?=؞? &?=ؔ?=؞?>???

~<><><><><><><><><><><><><><>< DAGA ALKALAMIN HAFSAT BATURE MUHAAD
'?~




~___________________________________~




Sheikh Imam Malik Shahararren malamin addinin musulunci ne, kuma babban alkalin Kotun Musulunci, Haifaffen jihar jos ne, wayayyen malamin addinin musulun ci ne kuma dan boko maiji da kanshi, ga wadatar arziki da Allah ya yi mashi, sheikh Imam ya yi suna wajen yin adalci, rukon amana tausayi da jin?ai, yana da ?warewa ta fannin shari'ar musulunci, mutunne shi mai tsastsauran ra'ayi akan addininsa, kuma kaifi Waya ne In ya furta magana baya canza ta, da dama mutane masu aikata mugayen laifuka suna jin tsoron shari'ar sheikh Imam Malik saboda sun san Halinsa baya kar6ar Cin hanci, dole mutun Ya kar6i hukunci dai dai da abunda ya shuka ko Wan uban wanene, sannan yana da zuciya idan ranshi ya 6aci, sai dai duk da hakan Yana da sau?in kai ga wanda ya iya zama da shi.

Matarsa Ta farko Malama Fatima Batool wadda ta kasance Yar uwarsa diyar wan mahaifinsa mazaunin Sudan, Auren zumunci iyayensu suka haWa su, Kuma cikin Ikon Allah jininsu ya haWu soyayya mai karfi ta shiga tsakaninsu har takai su ga yin aure, Sunyi zama Na amana saboda Ra'ayinsu yazo Waya, Yaji dadin zama da ita saboda kyawawan halayenta, tanayi mashi biyayya sau da kafa, A lokacin data samu ciki yayi murnar da bazata misaltu ba, baya gajiya dayi mata addu'a akan Allah ya sauke ta Lafiya, bayan data haihu ne ta koma ga Mahaliccinta yayin da tabar masa Yar jinjiran da ta haifa masa, Shiekh Imam Yaji rasuwar ta, duk irin juriyarshi da tawakkalinsa sai da ya zubda ?walla saboda babban rashin da yayi.

Rainon yarsa ya koma hannun gwaggwansa kanwar Mahaifiyarsa, A lokacin iyayensa duk basa araye, itace ta kula masa da Yarsa Har ta dan fara tasawa.

daga bisani Kawunsa na sudan ya bashi auren kanwar Matarsa Aunty Laura, a wani zuwa da yai sudan kai masu ziraya, A lokacin sheikh imam baida niyar ?ara aure saboda bai warke daga radadin rasa matarsa da yayi ba, amma saboda aunty laura ta kasance Jinin Malama Batool yasa shi amincewa da aurenta.


Bayan auransu da wata daya Rainon Aisha ya dawo hannun Aunty laura, ta rike ta da amana kamar yar cikinta, tana bala'en Son Aisha, saboda jininta ce ita uwa uba kamanninta sak dana Yayarta Malama Batool, saboda yadda take bata kulawa ba zaka taba gane ba yarta bace sai an fada maka.

hakika sheikh imam malik yayi namijin kokarin gurin tarbiyantar da rayuwar yarsa, ya tsaya mata tsayin daka don ta nemi duniyarta da lahirarta, gaba daya halayanta da dabi'unta irin nashi ne, abu daya da bata Wauko na shi ba shine Zuciya, tana da tsantsar hakuri kamar Mahaifiyarta Malama Batool, hausawa sukace kyan Wa ya gaji ubansa itama hakan ta ke Aisha tagaji mahaifinta da kuma mahaifiyarta malama Batool.


Sheikh Imam ya Waura mata burin duniya, Bai taba son wata aba kamar yarda yaso Aisha ba, ita kadai ce ?a daya tilo da Allah ya albarkace shi da ita, Babu irin gatan da sheikh Imam bai yi mata ba.

Aishatu macace mai cikar kamala, mai tsantsar kamun kai, samun matashiya mai irin baiwar ilmin da Allah ya bata zaiyi wuya a fadin duniyar nan, ta haddace alkur'ani mai girma tun tana da shekara goma sha uku a duniya, mutane dayawa suna yabonta saboda kyautatawarta a gare su, kyawawan dabi'unta da halayanta abin koyi ne ga duk wata ya mace, kuma burin kowani namiji ne ya mallaki mace kamarta.

duk wani abu da zai sabama Mahaliccinta gudun shi takeyi, tana da jin?ai da son taimako bata gajiya da hidimtawa addininta.

Abun burgewa iyaye mata da matan aure suna karuwa da ita, also she's a role model for young women.

tun tana yar matashiyarta take koyawa a islamiyar Mahaifinta mai suna madarasatul Fatima Batool dake a kusa da gidan su, tana yin wa'azi ta kuma yi da'awa ga waWanda basuyi imani ga Allah ba, ta dalilin Aisha, Sheikh imam malik Ya samu daukaka fiye da zaton shi, ta kare mashi martabarshi da kirmarshi ta kuma daukaka darajar shi a idon duniya, sau dayawan lokutta baya sanin tayi wani abun, sai dai akira shi awaya ko azo har gida ayi mashi godiya akan alkhairin da Aisha tayi, yai ta mamaki farin ciki ya cika shi, sai ya kirata ya tambayeta me tayi tukunna take fada masa Alherin da take samu a gurin Gasar karatul al'qur'ani da wadanda mutane suke bata kyauta saboda dadin wa'azinta da suke ji, dama A duk lokacin da ta kawo mashi kudin don ya dauki wani abu baya kar6a, kudinne take tarawa in suka taru dayawa da su take amfani gurin tallafawa marasa karfi, tana yawan ziyartar asibitoci, gidajen yari, da gidajen marayu ta basu tallafin kayan abinci da suturu in kuma bata da kudin da zata basu zatayi masu wa'azine da nasiha mai ratsa zuciya, shiyasa sheikh imam ya ke bala'en ji da Aisha, yana matukar son Yar shi, itama bata da abu mafi soyuwa dayawuce Mahaifinta, tana yi mashi biyayya sau da kafa, batason bacin ran mahaifinta, tana kokarin yin duk wani abu da zai faranta ran shi.


Dangantar da ke a tsakanin Benazir da Ayshah da Dr shureim ta samo asali ne tun daga kan Iyayen su Maza, Sheikh Imam malik baida amini daya wuce Alhaji ubaid Wadata sun kasance makwabtan junane, Gidansu Yana a jikin na juna, Akwai zumunci mai karfi a tsakanin Iyalansu, atare suka taso tun kuruciya, kasantuwar Alhaji ubaid Dalibin Mahaifin sheikh Imam ne agurinsa yake Waukar karatun addini kafin Allah yayi masa rasuwa, Alhaji Ubaid dan babban Gidane, Family dinsu yayi shura A jihar, saboda Arzikin Mahaifin su marigayi Alhaji mu'azzam wanda akeyiwa lakabi da wadata babban dan kasuwane a zamaninsa.

Benazir da Aisha ?awayen junane kuma aminnai tun kuruciya, atare suka taso kuma atare su ka yi primary da secondry a makarantar Sheikh Imam Malik wadda Har Islamiya ake koyawa a cikin ta, abun da zai Waure ma kai, kwata kwata halin Aisha dana Benazir baizo daya ba, sun sha banban, Benazir tana da girman kai, rashin kunya kuma bata iya shigar mutunci ba, duk suturar da zata sanya sai ta matse jikin ta.

Sarai Sheikh Imam yasan da Halin Benazir Ya kuma san Gado tayi agurin Hajiya layla, mutane suna yawan kawo mashi tsegumi akan ya raba yar shi da Benazir In ba haka ba zata bata masa tarbiyar ?a, Bai ta6a Waukar maganarsu ba, saboda Shi ya yarda da tarbiyar daya ba Aisha yasan bazata ta6a bari Benazir ta rinjaye ta ba, sai dai ita ta rinjayi Benazir gurin karkato da hankalin ta don ta shiryu, bayan hakan Yayi Wa Benazir farin sani, Yasan Bata Jin magana kuma bata da kunya sai dai ita din ba Yar iska bace, bata shaye shaye, bata bin maza, Rashin Wa'arta abaki ne da kuma yanayin Shigarta, sai kuma yawon gantali da take fita a kowani dare ne sai taje Night club, gata yar hana biki maraici, kuma zabaya ce a fagen rawa, amma Sheikh bai ta6a gigin raba ?awancen su ba, saboda yana son duk wani abu da Aisha ke so.

bayan haka baya son abunda zai raba zumuncinsu da makwabtan shi.

Wadannan dalilan ne suka sa Shiekh imam Ya amince ma ?awancen Aisha da Benazir, Amma sai da ya gindaya mata sharudda akan bai lamunta tadinga fita yawo ba, kulle ya ke mata daga makaranta sai gida, In har zasu hadu da Benazir sai dai tazo gidan su, Ko kuma In Aunty laura zataje gidan gurin Hajiya layla ta tafi da ita, sai kuma in sun haWu a school, amma sam bai yarda ta dinga bin Benazir suna fita yawon gantali ba bayan haka ya hanata kula kowani saurayi saboda akwai wanda yake burin ta aura har sa'insa su ke yi da Aunty laura akan ya hana Aisha kula samari ita ta rasa gane ma manufarsa akan Aisha kamar ba yar cikinsa ba, maganganu marasa dadi take fada masa bai ta6a biye mata ba.


Aunty laura wayayyiyar macace Yar boko kwararriya ta fannin business, ta inda suka sha banban da Imam ita tana da karancin addini akai, kwata kwata halinta ba irin na yayarta mariganya Batool bane, shiyasa basu jituwa da sheikh imam malik, sa'insa suke da junansu saboda ta tsani yadda yake zafafawa akan addini kuma A ganinta kullan da ya ke yi ma Aisha takura ce.

shi kuma yanayi ne saboda Farin jinin da Allah yayi mata, Babban abunda Ke ci mashi tuwo a ?warya yadda wasu mazan basa iya kau da maitarsu akan Aisha, saboda Dirin da Allah yayi mata, tun tana ?an?anuwarta wani irin dirin jiki ne da ita mai jan hankali, duk taku daya idan tayi sai jikin ya girgiza koda kuwa ta sanya dogon hijabi ajikinta ne sai shatun dirinta Ya bayyana wani irin farin jinin samari gare ta kuma mafi akasarinsu ba don Allah suke son ta ba sai don kwaWayin Surar ta.

wannan dalilinne yasa shi tsananta mata tsaro ko fita za ta yi dole ta sanya dogon hijab da ni?ab, daga makaranta sai gida makarantar ma shi ke kai su da kanshi In an tashi ya dauko su ita da Benazir, wani sa'in In aikin yayi mashi yawa ko zaiyi zaman shari'a Aunty Laura ce ke dawainiyar kaisu wani lokaci in ta samu damar dauko su daga school in an tashe su sai ta saci hanya takai su Shopping mall tayi masu siyayyar kayan amfanin su na mata.

Awata rana ne Aisha tana a zaune kan darduma sai ga Benazir ta shigo gidan da rawar jiki ta shigo har dakinta ta ruko hannunta da farin ciki take fada mata tazo taga Uncle musa da Yaya shureim sun dawo Nigeria, kasantuwar su dukansu A lokaci ba mazauna Nigera bane, Shi Alhaji musa harkar kasuwancin shi yakeyi a kasashen ketare yayin da Shureim ke karatu a kasar egypt can gurin ammin su ya ke da zama.

da fara'a Aisha tace meyasa bata fata mata ba, Benazir tace kawai tana son tayi suprising dinta ne, cike da farin ciki tace ta jira ta a falo zata shirya, Benazir na fita daga dakin Aisha ta soma shirya kanta cikin abaya, sai ga Aunty laura ta fito daga daki ta iske Benazir zaune kan sofa, da fara'a suka gaisa da juna har ta tambaye ta meya sanyata farin ciki nan take fada mata yaya shureim da Uncle musa ne suka dawo Nigeria shine ta zo don ta fada ma Aisha, washe baki aunty laura tayi tana fadin Ah lallai manya manyan baki, shine ba'a fada min ba? tana cikin magana sai ga Aisha ta fito sanye da dogon hijab hada nikab akan fuskarta.

fuska adaure Aunty laura tace kefa matsalata dake kenan, kamar kinfi kowa tsoron Allah, kullum cikin nikab, yanzu nan da gidan makwabtan namu sai kin saka hijab da nika..." a karshe ta korata daki tace taje ta sako Mayafi..da damuwa tace ita bazata iya ba, saboda hijab mutuncin ya mace ne, bayan haka baba ya hanata fita ba hijabi har ta soma janyo mata aya, aunty Laura ta mike rai a6ace taja hannunta suka koma daki, adole saida ta tursasa ma Aisha ta saka Wani guntun veil a kafadarta, baiwar Allah duk sai taji ba dadi ganin yadda abaya din ta Wame jikinta, dirinta nan nata mai jan hankali ya bayyana muraran musamman ta gurin mazaunanta sun fito rudu rudu..

ahaka Banezir taja hannunta suka tafi gidansu, shigarsu keda wuya ta gate din adai dai Lokacin Alhaji musa Yana atsaye gaban dankareriyar motarsa ya dauki wankan shadda hannunsa ruke da waya, kallo daya da Aisha tayi mashi saida gabanta ya fadi saboda ?warjinin dake gare shi, wata irin kirar jiki gare shi irin ta yan dambe.

Benazir ce ta gabatar mata da Uncle dinta, duk irin izzar Alhaji musa da yayi tozali da Aisha saida Ya rasa nutsuwarsa saboda shi irin mazan nan ne masu kwadayin mace mai kyawun sura, sanin da yayi mata tuntana karamarta yanzu kuma ta girma, wani irin kallo yadinga binta da shi harya kasa amsa gaisuwar da ta ke yi mashi, A lokacin rudewa Aisha tayi saboda bai kwanta mata arai ba, musamman da ta ga hakoransa ya sanya masu Gold-plated teeth..

ita kanta Benazir ta lura da yanayin da ya shiga. Hakan yasa taja hannun Aysha suka nufi cikin gidan, Uncle musa yabi bayanta ta da kallo yanayin yadda take tafiya jikinta na girgiza ba karamin tayar masa da maitar sha'awarsa tayi ba, kuma tun daga lokacin ya kudiri aniyar saiya mallake ta.

Bayan sun shiga babban falon gidan, anan suka iske Hajiya layla tare da Alhaji ubaid suna zantawa tsakaninsu, bayan sun gaishe dasu hajiya layla tace su shiga ciki su gaida shureim..

Tun da Allah Ya Halicci Aishatu Bintu Imam bata ta6a ganin mutumin daya kwanta mata aranta ba, da kallo Waya ta fada tarkon son shi sai akan dr shureim yanayin da suka same shi adakin shi yana zaune kan darduma Ya buWe al'kurni yana karatu cikin nutsastsiyar Muryarsa ba karamin jan hankalin ta yayi ba, tayi mamakin girman daya ?ara tsawon shekaru a lokacin rabon shi da Nigeria.

Sai da yakai aya, cikin sanyin murya yace masu su shigo yaga sun yi tsaye bakin kofar dakinsa, Jan hannunta Benazir tayi suka zukunna agaban dardumarsa ta gabatar masa da aminiyarta yar makwabtansu diyar sheikh Imam, ganin kamar bai gane ba don tun suna kanana Yabar Nigeria, Aisha ta gaishe da shi tare da yi mashi bangajiyar tafiya, da murmushi akan fuskarshi ya amsa mata, abunda bata sani ba Dr shureim yasan da zamanta, Yana yawan sauraron kira'arta da take yawanyi a taron musabaka, wanda mutane ke yaWa videon a social media amma saboda miskilancinshi sai ya nuna kamar bai gane ta ba.

sun Wan jima Yana jan su da fira, lokacin da ta tashi tafiya dr shureim ne ya yi mata rakiya tare da Benazir har kofar gidansu, saida suka ga shigarta kafin suka koma gidan su.

a daren ranar Alhaji musa Ya kira Benazir ya soma tambayarta dangane da Aisha, ko tana da tsayayyan da zata aura"? Benazir tayi mamakin tambayoyinsa saboda tasan Uncle din nata mugun miskiline bai cika shiga sabgar da bata shi ba, In fact mata basa agaban shi bata kawo komai aranta ba ta fada masa komai dangane da Aisha, Hankalinsa ba karamin kwanciya yayi ba jin cewa bata kula samari, fargabansa daya Sheikh Imam malik saboda basa ga maciji.

A bangaren Aisha tun bayan data koma gida tunanin dr shureim Ya hana zuciyarta sukuni, Kwana take da shi aranta, haka zalika in tana koyama dalibanta karatu wasu lokuttan shagala take da tunaninsa har sai daliban su ankarar da ita.

ta bayan fage Uncle musa ya fara ba Banezir makudan kudi masu auki don suje yin siyayya da Aisha, kuma yace mata baya son Aishar ta sani, Benazir bata ta6a fada mata Uncle musa ne ke bata kudi ba, Sai ma in ta tambayeta ina take samun kudi sai tace dr shureim ne ya bata, hakan ya sa ta saki jiki duk da bata da kwadayin abun duniya tayi azan yaya shureim yana son ta ne shiyasa yake ba Benazir kudi don suyi siyayya.


kusan kullum sai Aunty laura tayi masu hanyar fita daga gidan batare da sanin Shiekh Imam ba, don suje Mall suyi siyayya harma da yawon buWe ido koda Aisha ta nuna bata son fita Aunty laurace ka tursasa mata in ta turje sai ta fashe mata da kuka tana fadin bata mata biyayya saboda ba ta Wauketa uwa, don taga ita bata haihuwa, in ta fadi hakan jiki na rawa Aisha take bin Umarninta.

Tun bata sake ma Uncle musa in suka haWu harta fara sabawa da shi, tana matukar girmama shi tanayi mashi kallon Uncle dinta.

Haka zalika shakuwa mai karfi ta shiga tsakaninta da dr shureim, Benazir tayi mamaki saboda sanin da tayi ma Aisha bata Kula maza sai gashi dr shureim ya ciri tuta, sun saba da juna, Benazir ta sanya masu ido sosai, Ta fahimci dukansu suna son juna, ita Aisha Kunya ce ta hana ta furta mashi Kalmar so, yayin da shi kuma miskilanci ne Ya hana shi bayyana mata, bayan haka Yana jin nauyin yayi soyayya da Aisha saboda yanayi mata kallon Kanwarsa.


A duk lokacin da Benazir taso Ta bugi cikin shureim don ya fada mata In yana son Aisha sai yace mata shi babu soyayya atsakaninsu kallon kanwa ya ke yi mata, haka In ta bugi cikin Aisha don taji in tana son ya shureim sai tace mata ita fa ba son shi ta ke yi ba, kawai tana yi mashi kallon yayanta ne saboda zumuncin dake a tsakaninsu, In Benazir zata shekara tana tambayarsu amsa daya suke bata.

Bayan da suka kammala Secondry School, Alhaji Ubaid ya sama masu admission a wata Jami'a dake a birnin hagen na kasar Jamus batare da sanin sheikh Imam Malik ba sai daga bisani ya same shi har gida ya sanar da shi.


shiekah Imam bai nuna amincewarshi ba, Yace shi bazai bari yarsa ta tafi uwa duniya karatu ba, duk Universities din dake a Kasar har sai an fita waje neman ilmi? Alhaji ubaid ya ce yayi hakuri da bai nemi shawarar shi ba ya tashi ya yanke hukunci dama


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login