Showing 354001 words to 357000 words out of 359620 words
ana kissing na yaya ne?". Girgiza mishi kai ta yi kafin ta ce "Ba'a yi, amma kai special ne, dan haka close your eyes ka gani".
Dan ya gwadata kuma ya tabbatar da abin da take faɗa, shin zata yi ko ba zata yi ba, sai ya runtse idanun nasa.
Ɗan ɗagowa ta yi a in da ta kara tsawonta tare da dafa cinyarsa ta saƙalo wuyarsa da hannunta ɗaya, runtse idanu ta yi kafin ta matso da face nata daf da tashi, zuciyarta tamkar zata fashe ta fito waje saboda tsananin tsoro, amma haka ta daure ta ɗaura lips nata a saman nasa. Wani irin dogon numfashi ya ja wanda sai da ya sanya ta buɗe idanunta, kankame jikinta ta yi waje guda tana jin tamkar ba zata iya ba, amma saboda ta kure shi sai ta daure, a hankali ta fara shan lips nasa na kasa.
Bai san time ɗin da a sukwane ya waro idanunsa waje ba, ta datse nata idanun gam tana kissing nasa cikin kwanciyar hankali. Kasa jurewa ya yi a zafafe ya kankameta sosai a jikinsa tare da juyawa suka koma saman bed ɗin da kyau. Bai taɓa zaton da gaske zata aikata abin da ta faɗa ba, duba da ita mace ce mai tsare mutuncinta over, fiye da tunanin mai tunani, abin da bai sani ba shi ne, dan ta san shi mijinta ne yasa, ba dan haka ba, wlh ko kusa ko alama, wani ma ya kawo mata zancen banza ba sai ta zubar mishi da hakwara ba, tana da kula da kanta over, shi ne abin shi ma ya ɗaure mishi kai, a koda yaushe yana yi mata addu'a sosai idan ya yi sallah, yana sanya mata albarka tare da fatan alkhairi na irin ƙoƙarin tsare mutuncinta da take yi, hakan yasa ma kullum sonta yake mugu mugun karuwa a ransa. Idan ka dubi rayuwar Jehan ta fiskar ilimi da basira, zaka fahimci ita mace ce da duk wani namiji a duniya zai yi burin ya sami irinta, ba ita kaɗai ba, duk ƴaƴan Nawazuddeen, saboda mum ta yi iyaka bakin ƙoƙarinta wajen basu tarbiya ba karya.
Zura harshensa ya yi cikin bakinta, ya fara bata nashi salon. Tun ba'a je ko'ina ba ta nemi ta gudu, amma ina ta makaro, dan kuwa riketa gam ya yi tare da fara shafa wasu sassa na jikinta, fara kokarin ambatar sunansa ta yi, amma ina bai amsa ba. Nan take idanuwansa suka sauya launi. Cikin fitar hanyaci ya kamo breast nata ta saman rigar tata. Wani irin numfashi mai wuyar fassaruwa ya fara sakar mata. Nan take tsoro ya kamata ta fara kiran sunansa da karfi karfi. Amma ina bai amsa mata ba.
Ganin yana ƙoƙarin cire mata kayan jikinta ne yasa ta dakarkare ta gabza mishi cizo a hannu, ko kaɗan bai ji komai ba, tamkar ba shi ta ciza ba. Kuka ta fara yi mishi tana bubbuga shi a kan dan Allah ya kyaleta. Duk abin da take yi na rakin yana jinta, dan bai zurfafa da yawa ba bare ya fita a hayyacinsa, da gangan ya barta ta yi ta yi yaga iya gudun ruwanta.
Can kuma wani tunani ya faɗo mishi, idan har ya yi mata hakan kuma zata fara gudun shi, ɗan sakin jikin da ta yi da shi ma zata janye. Tuna hakan ne yasa ya matso da bakinsa kusa da kunnenta. Raɗa ya fara yi mata a hankali yana faɗin "Wato har yanzu baki daina rigimar ba ko? To na kyaleki, amma kuma ai ke kika fara ko?". Yana magana yana goge mata hawaye. "Bana son wannan kukan sam my baby, ki daina kin ji ko? Yana taɓa mini zuciya sosai".
Ko sannu bata ce mishi ba har ya gama goge mata hawayen tare da gyara mata rigarta da ya fara kokarin cirewa. Sumbata ya kai mata a kumatu kafin ya ce to ta tashi ta je ta yi wanka, dan ya san abin da zata ce kenan. Ya kai karshen maganar tare da sauka daga kanta.
Runtse idanuwanta ta yi tare da mikewa zaune, wani irin sabon azababen kaunarsa take ji yana ratsata. Jiki ba kwari ta miƙe ta kwashe kayan abincin ta nufi waje. Da kallo ya bita har ta fita kafin ya koma ya kwanta tare da kifawa ya jawo pillow ya rungume tamkar ita ya runguma.
AFTER ONE DAYS.💋
A ɓangaren Aseef da Akila kuwa, yau za su je wajen Ammie, sai murna Akila take yi, shi ma sai tayata yake yi. Amma fa kamar yanda kuka sani ne, an sha dirama a wajen yin wanka, ya ce shi dai lallai sai ya yi mata wankar nan, ita kuma ta ce a'a, daga karshe dai suka yi yarjejeniya a kan idan suka dawo da daddare zasu yi tare, haka ta amince mishi, sai dai shi kuma ya kudurci niyar tun da yau Lion zai shigo, tabbas idan suka dawo da daddare sai ya yi dis virgin nata, Allah yau ba zai kyaleta ba, amma bai bari ta gane ma ya yi niyar yin hakan ba, ya dai kyaleta a kan idan suka dawo da daddare za su yi wanka a tare, shi kaɗai ya barwa kansa sanin abin da ya shirya mata. Zata gane shayi ruwa ne, za kuma ta gane annabi ya faku.
Haka suka shirya cike tab da kula da juna suka nufi gidan Ammie, Areef ya so su je tare, amma sai ya ce su je kawai dan akwai wani surprise da ya shiryawa daddyn Rimsha anjuma kaɗan, idan bakin sun iso zai zo tare da daddyn da kuma Jehan. Da haka suka yi sallama da su, suka wuce wajen Ammie.
A ɓangaren Lion da Rimsha kuwa, abin ba'a magana, yanzu ya zamana anytime suna manne da juna, ko tana kwance a jikinsa saman faffaɗar kirjinsa, ko kuma ta tada kai da cinyarsa, yana aiki a laptop tana taɓa mishi saje, idan ta cika damun shi da yawa, sai ya ture laptop ɗin ya jawota jikinsa, daga nan zai fara romancing nata cikin taka tsantsan.
Na'urat tana samun kulawa over daga wajensu, suna matuƙar kaunar tsohuwar, dan fa kowa ya san Brr mutuniyar kirkice over, duk wanda ya ji tarihinta sai ya kaunaceta. Alex da Mark sun yi muguwar sabo, sun zama kamar wasu twins, har waya da Anaya Alex yana yi, su gaisa, sai dai bai san cewa Anayar ƴar yayansa Hassan wato Azharuddin ba ne, shi ma dai Mark har yanzu bai san alaƙar dake a tsaninsa da su Rimsha ba, shi dai yaga an ɗauko Naurat, tun da Lion bai yi mishi wani karin bayani ba, sai ya yi shiru shi ma, kuma sam bai tambayi Alex ɗin ba, dan baya shiga abin da bai shafe shi ba, kowa ya sani dan ma soyayyar Anaya tasa ya ɗan canza har yake iya magana mai ɗan tsawo da mutanen, ban da haka ai shi kamar robot ma yake. Rayuwarsa gwanin birgewa, baya shiga harkar kowa, idan kuma ka shiga tasa, to zaka yi danasani.
RIMSHA
Zaune take saman sofa daga ita sai wasu shegun kayan shan iska, wandon ɗan guntu wanda ko rabin santala santalan cinyoyinta bai kai ba, sai riga zuwa iya cibiya, daga ta sama hannun vest rigar yake da shi, ta sako gashin nan har gadon baya, hannunta na rike da wayarsa tana latsawa, da alama chatting take yi ko da daddynta, ko Areef or Aseef. Sai zuba murmushi take yi kyawawan dimples nata suna ta lotsawa.
Tamkar daga sama ta ji ya zuro hannunsa ta bayanta izuwa saman shafaffen cikinta da tamkar bata taɓa zuba mishi abinci ba. Sake jiki ta yi ta kwanta a saman faffaɗar kirjinsa tana mai kara faɗaɗa murmushinta.
Matso da ɗan bakinsa saitin kunnenta ya yi yana faɗin sun kusa shiga Nigeria me zata bashi?. Ajiye wayar a gefe ta yi tare da juyowa ta shige jikinsa da kyau tana faɗin "Me kake so?". Shafa kanta izuwa bayanta ya fara yi, sanye yake da wando three cuter da polo t-shirt, shi ma bai ɗaure gashin kansa ba.
A kunne ya raɗa mata abin da yake so tamkar wani nayi musu laɓe. Ɗan zaro idanu ta yi waje kafin ta ce "To shikenan na yarda, amma kuma ai ina....". Bai bari ta karisa maganar ba ya ɗaura latsa ɗaya a saman lips ɗin nata tare da ɗaukarta cak suka wuce gado.
Saƙalo wuyarsa ta yi a in da suka kwanta tare, rumfa ya yi mata da faffaɗar kirjinsa yana kallon cikin kwayar idanunta, while ita kuma tana kallon wuyansa. Daga saman cibiyarta ya fara kissing nata har zuwa saman wuyarta, lumshe idanu ta yi tare da sanya hannu ta fara shafa mishi kyakkyawan gashin kansa.
Romancing nata ya fara yi son ransa, bata hana shi ba, sai hawaye da take yi. Har sai da ya samu ɗan sauki sauki sannan ya kyaleta. Ɗaukarta ya sake yi suka nufi pool dake cikin jirgin, ta baya kenan. Ruwan ciki akwai zafi dai'dai yanda suke wanka.
Sundumata ya yi a ciki da gabaɗaya kayan jikinta, ƴar kara ta saka mishi dan ruwan da akwai ɗan zafi, ya yi mata yawa zafin. Shiga ciki ya yi tare da jawota jikinsa yana yi mata sorry na zafin da ta ji. Hannu ta ɗaura saman ɓul ɓul ɗin breast nasa tana faɗin "Noori kirjinka a cike sosai". "Kina son kallonsu a zahiri ne?". Cikin sauri ta girgiza mishi kai alamar a'a. Ɗan shafa fusatatcen face nasa ya yi yana faɗin "Why?". Ba komai, ta bashi amsa.
Hannu ya kai saman hannun rigarta, zamesu ya yi ta saman kafaɗarta suka sauko kasa zuwa wajen hannunta. Zamesu gabaɗaya ya yi rigar ta dawo saman cikinta. Hannunsa dukka biyu yasa ya riko tula tulanta, ko wanne da hannunsa ɗaya ya riko shi. Runtse idanunta gam ta yi. Da ɗan karfi ya matsa mata su har sai da ta ce "Wash Noori akwai zafi". A hankali ya lumshe idanuwansa tare da sake buɗesu a kanta. Sake tula tulan ya yi yana mai kara jawota jikinsa. Shafa zanen sunansa ya fara yi yana mai jin matuƙar kaunar zanen.
Meesha, ya ambaci sunanta. "Na'am My Noori". Ta amsa tana ɗan murmushi. "I like this your tattoo". Shiru ta ɗan yi kafin ta ce mishi ba tattoo ba ne, wani abin ne da yarabawa suke kwaɓawa. Shiru ya yi yana mai cigaba da shafa wajen na tsawon lokaci.
Sun jima manne da juna a cikin ruwan kafin su fito. Bedroom nasu suka koma a in da suka tsara shirinsu cikin kayan mutunci, dan sun kusa shigowa Nigeria.
A ɓangaren su Areef kuwa, sai misalin ƙarfe biyu ya ce da daddyn Rimsha ya shirya su je unguwa. Sam daddyn bai kawo komai a ransa ba, shiryawa ya yi suka nufi gidan Abba. Areef ɗin ne ya ja motar, sam Jehan taki yarda ta zauna a gidan gaba, a baya ta zauna, daddynta ya zauna a gaba. Ko da suka je gidan Aseef da Imran basu nan, sun je gidan Abbi, Akila, Umaisha, Jelly kawai suka samu a palo, shi Akil ya ma yi tafiya zuwa Abuja yau da safe, yana shirye shiryen komawa Madina.
Su na shiga palon bakinsu ɗauke da sallama, da sauri Akila ta miƙe ta nufo Jehan tana yi mata ayoyo, dama kwana biyun nan suna shiri sosai. Rungume juna suka yi tare da karisawa cikin palon. Ina Aseef, Areef ya tambayi Akilar, kasa ta yi da kai wai ita a dole tana jin kunyar yayan miji, cikin girmamawa ta ce mishi sun tafi da yaya Imran. Okey ya amsa mata tare da ɗaukar wayarsa da call ya shigo yanzu ya nufi waje yana cewa su daddyn yana zuwa.
Hira suka cigaba da yi har Ammie ta fito ta same su, cikin mutunci suka gaisa, Akila ce ta gaya mata daddyn Rimsha shi ne bappansu Hossain. Kara faɗaɗa murmushinta ta yi tana sake ɗaga mishi gaisuwa. Wancan karon da ya zo basu haɗu da ita ba, ta so su gaisa, amma tana barci, shi ne yasa bata san shi ba.
Cikin farinciki suka cigaba da zuba kiransu har lokacin da Areef, Abba, Mummyn Rimsha da kuma gwaggo suka shigo cikin palon bakinsu ɗauke da sallama. Areef ne ya binciko in da suke, dama idan baku manta ba su mummyn sun zo Kaduna saboda azumi ya kusa, sun zo yin azumi gidansu Anaya, shi kuma Areef da farko ma ba su mummyn ya je bincika a gidan ba, ganin cewa daddyn Anayar yana tsananin kama da daddyn Rimsha ne yasa ya fara bibiyarsa dan ya san wanene shi, tun a school ɗin su Rimsha ranar ya ga daddyn Anayar. Rana ta farko da ya fara zuwa gidan ya sha ruwan mamakin ganin Anaya, da farko ya ɗauka Jehan ce, sai da ya kalleta da kyau, sai yaga Jehan ta fita haske, ta kuma fita cika, shi ne kawai banbancinsu, banda haka suna kama over.
A ranar da ya je sun gaisa da daddyn Anaya a in da ya yi mishi tambayoyi a kan ko ya san su Abba, bai nuna mishi cewa suna tare da daddyn Rimsha ba. Amsa mishi daddyn Anayar ya yi da e su Abba ai yayyunsa ne, ya sansu, sai dai baya zuwa in da suke, kuma ya yi alkawarin ba zai sake zuwa in da suke ba har sai sun nemo mishi Hosain ɗinsa. Sosai Areef ya ji matuƙar daɗin maganar daddyn Anayar. Shi kuma daddyn Anayar ya bashi wannan amsa ne dan yana tunanin kila wani abin ne ya sami su Abba da yasa har Areef ya zo bincike, a tunaninsa da kuma kallon da yake yi wa Areef, babban jami'in ne, shi ne yasa bai ɓoye mishi ba ya bashi amsa ta gaskiya. Ko da ya dawo gida, sam bai nunawa daddyn Rimsha ya je wajen daddyn Anaya ba, ya kyalesu dan sai ya gama binciken da yake yi.
Zuwansa gidan na karshe jiya da ya ce Jehan ta zo su je unguwa ta ce ba zata je ba, to wannan fita da ya yi gidansu Anayar ya je, ya kuwa yi sa'a daddyn Anayar ya ce su shiga cikin palo.
Suna shiga shi ne yaga mummy da gwaggo suna hira, dama idan baku manta ba, ya ce zai karɓi hotonta a wajen daddyn Rimsha, to ya karɓa, shi ne yasa da ya ganta, ya gane ta, amma bai nuna mata ya gane ta ba, kuma bai nuna mata ya san mijinta ba, dan yasan ba ma zasu yarda da hakan ba, sai ya kyaleta ya zo ya gayawa Abbansu Imran. Sam bai je ɗaukota ba, sai ya bari Abban ya je ya ɗaukota da kansa, dan idan shi ne, tabbas mum zata biyo shi. To wannan shi ne surprise da ya shiryawa daddyn Rimsha.
Ai kuwa ya ga tsantsan farincikin daddyn Rimsha da bai taɓa gani ba. Gwaggo sarkin masifa, da farko ta ce wlh ita ba zata shigo gidan Abba ba, ai ita da Abba har abada, sun yi hannun riga. Sai da Areef ya fito ya yi mata daɗin baki, shi ne ta yarda ta shigo, dama wannan ɗaukar waya da Areef ɗin ya yi ya fita, waje ya je dan Abba ne ya kira shi a kan gwaggo ta ce wlh ba zata shigo ba, ta tsani gidan..........To meyasa gwaggo zata tsani gidan yayanta kuma? Mu dai je zuwa, amma fa akwai rina a gaba ba kaɗan ba, akwai cakwakiyoyi na wuce misali, ku gyara zama dan ƙwaƙwalwarku ta iya ɗaukar wasu abubuwa, cakwakiyar gidan Hjyr Umaiya ma na dodannin nan kawai ya wuce tunaninku gaskiya.
Gwaggo har da kukanta na ganin daddyn Rimsha. Allah sarki rayuwa kenan, palo ya cika da tsantsan farinciki, tuni Jehan ta haye jikin gwaggo, dama kun san ita ai ta gwaggo ce, bata wani turmushe mummynta kamar yanda ta turmushe jikin gwaggo ba, sau ɗaya ta rungumi mum, daga nan ta haye jikin gwaggo ta kwanta kamar wata jaririya. Ita ma gwaggo dama kunsanta da goyawa Jehan ɗin baya, idan kana neman bala'in gwaggo to ka taɓa Jehan, nan zaka ga ruwan bala'i da masifa kwando kwando, kai gwaggo ba dai faɗa ba wlh, akwaita da zafin rai ga karfin hali, isa da kuma izza, duk ta haɗe kamar wata jinin sarauta, dama ita Jehan ta gado, shiyasa suke shiri, sai hali yazo ɗaya ake abota.
Sai wani lallaɓa Jehan ɗin gwaggon take yi, ita kuma Jehan ɗin tana zuba mata ruwan shagwaɓa. Har wani taɓe baki Areef ya yi yana mamaki, wai dama Jehan ta iya shagwaɓa har haka? Dama tana magana har haka?..... Bai san cewa ainahi dama ita idan ba da gwaggo ba, ko da mummynta bata sakewa ta yi hira, idan kana son kaga tana magana, to ka ganta tare da gwaggon, ai shagwaɓa kwando kwando take zubawa gwaggo, ita kuma tana biye mata.
Ansha kuka kamar ba gobe. Sai da komai ya ɗan lafa ne gwaggon ta ce wai ina Rimshar ta ne, bata ga ƴar autarta ba, uwar rigima da kukan. Tamkar jira Jehan take yi a tambaya, nan ta fara bawa gwaggo labarin duk abinda ya faru na auren Lion da Rimshar.
Nan fa gwaggo ta yi tsalle ta dire, ta ce idan an isa me take, bata uban da ya isa ya yi musu wannan iskanci ba, kamar Rimshar ce za'a aurar? To wlh ba zata saku ba bindiga a ruwa, da sake wlh. Hakuri daddy ya fara bata. Ina taki sauraran shi, ta in da take shiga ba ta nan take fita ba, sai hura hanci sama take yi. Abba ya yi ƙoƙarin saka baki, amma ina ta murje idanu sam ta ce wlh ba zai yiwu ba. Dama ita gwaggo fa idan ta fara ballin bala'inta, to wlh kowa a cikinsu sarara mata suke yi, sai time da ta sauko...... Gwaggo fa ita ta ɗauko ainahin jinin TRUMP, wato mutanen Russia, mahaifin Naurat, ita ta gadosu in dai fagen zafin rai da faɗa ne, ga bakar zuciya ta faɗa.
Shi dai daddyn Rimsha sanin halin Lion yasa ya cigaba da bata hakuri. A kule ta ce "Allah Nawazudden ka kiyayeni, ina magana kana magana ko?. Yau sai naga waye ubansa a garinnan, dole na ɗauko Rimsha yanzu, wai ce mishi aka yi bata da gata ne? Ko dai kwararota aka yi