Showing 42001 words to 45000 words out of 359620 words
ya ja maki bala'in da in danginmu dukka za su haɗu babu mai fiddaki, amma In Sha Allah komai zai wuce nan da ƴan kwanaki kaɗan, ina da tabbacin zai sauƙo, zuciyar zata yi sanyi".
Rushewa tayi da kuka tare da zube gwiwowinta a kasa ta toshe baki da hannayenta dukka biyu, ƙwaƙwalwarta yana tariyo mata irin muguntar da ya rinƙa yi mata, hannu yasa ya ɗagota yana mai rarrashinta.
A wannan halin Areef ya shigo garden ɗin ya same su, da fara'a ya shigo, amma ganinta a wannan hali yasa ya ɗaure fuska sosai. "Prof me ka yi mata take kuka?". "Me kuma zan yi mata Areef? Kawai dai taga sojojin nan da Lion ya ce zai kawo ne, to ta ga ya cika maganarsa ne, shi ne take kuka.
Murmushi kaɗan ya saki, cikin sigar rarrashi ya fara magana "Our princess ina raye ba zan taɓa barin hakan ta faru ba, ɗan uwana ne fa, na san ta yadda zan bi da shi, kada ki wani damu, In Sha Allah wannan aikin gabaɗaya kin kusa dainawa, daga yau zuwa gobe, zan san ta yadda zan dakatar da shi, ba dai na sami lafiya ba, kawai ki zuba ido ko sha kallo, yanzu dai share hawayenki gimbiyar TRIPLETS". Ba karamin daɗi ta ji ba, cikin sauri ta goge hawayenta tare da fara zuba mashi godiya.
Girgiza kai ya yi tare da sanya hannunsa ya ɗan rungumota a gefen jirjinsa, wani iri ta ji a jikinta, shi kuma ko a jikinsa bai damu ba, bai ji komai ba.
"Ku zauna mana, Prof ina da magana da kai". Ya faɗa tare da saketa ya zauna saman sofa, kusan a tare ita da Imran suka koma suka zauna.
"Prof what is goruba?". Ɗan zaro idanu waje Imran ya yi, tunani ya fara yi, wai a ina Areef kuma ya jiyo sunan goriba? Me kuma zai yi da ita? Dan dai tabbas shi dai ba iya cin gorobar zai yi ba, bai ma santa ba, amma ya zo yana tambaya.
"Prof i said what is goroba?". "Areef what are you going to do with the goruba?". Kai tsaye cikin wasa ya ce "My future wife mana zan kaiwa, wai kai Prof ina ruwanka ne? Just kawai tell me what is it, kai ni nama fasa son sani menene, just kawai a kawo mani goroba from now to tomorrow"........ To fa goruba kuma🤔
"To Shikenan za'a kawo maka, ba dai goroba ba? Ai gidanta kazo, Allah yasa ka iya ci". Imran bai yarda a kan wata zai kaiwa ba, domin shi dai yasan TRIPLETS ba ɗaya daga cikinsu da yake da girlfriend, kai idan ma ba Rimsha ba, ba su da wata mace da suke yi wa magana, hakan yasa bai yarda da zancen ya ce wata zai kaiwa ba, ya mayar mawai kila yana son ya gwada ci ne, tun da wani lokaci tana cewa zai ci abincin hausawa, to amma a ina yaga goriba? A ina yaji sunanta da har zai gwada ci ɗin? Shi da ko saninta bai yi ba? Akwai wata a kasa.
Areef zai yi magana Imran ya rigashi da cewa "Rimsha Saif na buƙatar abinci, ki je ki kai mashi, dan Allah Rimsha ki kula kin ji ko?" Gyaɗa mashi kai ta yi tare da amsawa da to, daga haka ta miƙe ta bar wajen, su kuma cigaba da hira suka yi.
Kamar kullun Mark ya kammala haɗa mata abincin, hannunta ta wanke kafin ta ɗauka ta wuce izuwa bedroom nasa.
Da sallama ɗauke a bakinta ta shiga, yana balcony, ya miƙe a saman ɗaya daga cikin tsadaddun kujerun dake a wajen, ya ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya, sai wani Lumshe idanu yake yi kamar mai jin barci, pajama ne a jikinsa, launin army colar, ya saki wannan kyakkyawar dark black curly hairn nan nasa, sai wani kyalli gashin take yi, kwana biyu da suka ɗan yi a Nigeria har ya ɗan yi duhu saboda zafi, fatarsa ta rage haske, sai dai kuma ta kara kyau da kwanciya luf luf kamar matar jariri, ya kara fresh sosai.
A in da ta saba ajiye mashi abincin, a nan ta ajiye, ita ma zaman ta yi tana jiran shi, shiru shiru ba shi babu labarinsa, sai ƴan waige waige take yi kamar mai neman wani abin, ji take yi tamkar ta tashi ta ɗan yi mashi taɓe taɓe tun da baya nan, amma sai ta tuna da abin da Imran ya gaya mata kafin ta zo, tuna hakan yasa ta daure ta cigaba da zama jiran shi kawai.
Sai da ta kwashi minti 30 a wajen a zaune kafin ya miƙe ya taho, wa iya zubillah, kallo ɗaya ta yi mashi, ta yi saurin kawar da kai, dan kada ya kamata, da yake yana nufota ne, amma ta kasa manta kyawun da ta kallah.
A in da ya saba zama ya zo ya zauna, abinci ta zuba ta tura Mashi, ba ɓata lokaci ya ɗauka tare da fara ci, sai satar kallon shi take yi.
Ɗan dai'dai ya ci abincin, ya ajiye spoon ɗin tare da yi mata alama da hannu akan ta zuba mashi ruwa, cikin sauri ta zuba ta mika mashi, ba ɓata lokaci ya karɓa ya sha, bayan ya ciro cup ɗin kuma, ya ajiye mata tare da miƙewa ya fice daga ɗakin, cikin sauri ta kwash kayan abincin ita ma ta fita.
Kitchen ta mayar da kayan abincin kafin ta dawo in da su Imran suke zaune, zama ta yi suka cigaba da hira.
Misalin karfe 10 daidai Imran ya je ya ɗauko AKILA, tun jiya dama Rimsha ta kirata a waya ta gaya mata cewa ta zo mata da kayan tea ɗin, yaya Imran ya ce zata zo su wuni, sai dai a gidan Akil ya je ya ɗaukota, yaki zuwa gida da kansa, domin ya ji labarin kiran da Ammie take mashi ta bakin Akil ɗin, to yaki zuwa, ya fi so sai ya haɗu da Abba sun tattauna kafin ya timkareta, sai Abbansa ya yanke hukuncin me zai ce mata kafin su haɗu kenan, shiyasa ya kira Akil akan ya ɗauko mashi Akilar daga gidan, ya ce wa Ammie za su je wani gari ne haka, domin yana so Akilar ta yi kwana biyu haka a gidan, ta ɗan ɗebewa Rimsha kewa, ai kuwa Akil da ya je, sai ya ce wa Ammie Abuja za su je, ita kuma in dai Akil ko Imran ne za su ɗauki Akilar, to bata damuwa, koma wata ne suje su yi, dan tasan suwa ye ta haifi........... OH WASA WASA AKIL DA IMRAN SUN ZAMA MAKARYATA SABODA SOYAYYA.🤔 SU DA BASU SAN MENENE KARYA BA, BASU YI, SUNA MA TSAWATARWA MASU YI, AMMA YANZU SABODA KAUNAR FAMILY'N ABBANSU SUN FARA KARYA SOSAI....🤔
Da Akil ya je gida ɗaukar Akila, Ammie ta tambaye shi ina Imran, sai ya ce mata ai baya kasar ne ma baki ɗaya, amma ya kusa dawowa, haushi kamar ta yi yaya, haka ta hakura ba dan ta so ba, ta yi kwafa tana jiran dawowar shi, dan dole ya saki jelly, bata san shi ma Akil ɗin yana tare da matarsa ba, in dare ya yi, sai ya dawo gida ya shiga ɗaki kamar mai barci, idan dare ta tsala kowa ya yi barci, sai ya fita ya gudu gidansa wajen Umaisharsa abinsa. (Ƴaƴan Ammie akwai ƴan air wlh🤣)
Yau murna a wajen Rimsha ba'a magana, ta rungumi Akila sosai kamar wani ya ce zai rabasu, ita tasan Akila ƴar uwarta ce ta jini, ita kuma Akila bata san hakan ba, kuma ga shi daddynta ya ce kada Imran ya faɗa, hakan tasa bai faɗa ba ya yi shiru, ita ma bata gayawa Akilar ba.
Ɗaki suka kule, sai zuba hira suke yi, a in da Akila take bata labarin masoyinta ya ce zai zo ranar Wednesday, tana cikin murna mara misaltuwa, sai murna Rimsha take taya ta, tun da Akila ta zo bata haɗu da Areef ba, haka ma Lion basu haɗu ba, hasalima daga Lion ɗin har Areef ɗin ba su san ma tazo ba, gara Lion ma Imran ya gaya mashi zai je ya ɗauko sister sa wa Rimsha, sai da ya bashi izini tukun nan ya ɗaukota.
Tun da tazo sun kasa motsawa ko nan da chan, sun baje a saman gado har sai da aka yi sallar azahar, a sannan ne suka yi wanka tare da sallah, yau Rimsha baki ya ki rufuwa, kuma ga shi yau gidan nasu a cike tab da bakin sojoji, idan ba ka kai zuciya nesa ba, to ba zaka iya zama a cikin waƴan nan jibga jibgan ba, wlh kallonsu ma kawai ya isa ya rinƙa razanaka har rai ya yi halinsa, gasu kamar wasu gumaka, basu magana ko kaɗan.
Shiryawa suka yi dukkansu cikin riga da wando, da yake Akila ta fi Rimsha cika sai kayan sam basu dace ta fita da su a haka ba, gara Rimsha, duk da ita ɗin ma bai dace ba cikin zaratan mazan nan ba, musamman yanzu da aka karo wasu, ita zuciya bata da kashi, da Allah yasa mazan ma dukka turawa ne, irin wannan shiga ba bako bane a wajensu, shi ne ma dama shigar matan kasarau, to amma ai yanayin jiki da halittar diri daban daban.
Palo suka fito, babu kowa a palon sama, dan haka sai suka nufi kasa, dukkansu suna sanye da ƙaramin hijabi please call me, sai murna suke yi, baki ma ba zai iya faɗen farincikin da bayin Allahn nan suke a ciki ba.
A palon kasa suka zauna suna hira, Mark na kitchen yana ta faman aikinsa, sai kallonsa Akila take yi, taga farin Bature tas babu mix.
A ɓangaren Gidan Abbo kuwa........
❤️❤️TRIPLETS❤️❤️
E11-12
A ɓangaren Gidan Abbo kuwa.
Bayan kwana biyu. A cikin wannan kwana biyun sun yi muguwar sabo a tsakaninsu, Aafia ta saki jiki sosai da shi, ya mantar da ita abin da yake damunta a ranta, har wa yau kuma Abbo dai shiru, ba shi ba labarinsa, kuma su dukka ba wanda ya sake tunawa da zancensa, abin kamar almara, ya rufe masu babinsa a bakunansu da kuma zuƙatansu.
Soyayya mai tsabta suke gudanarwa a tsakaninsu, sai dai fa tun daga wannan sumbata ɗaya da ta yi Mashi, ba wani abin da ya sake haɗa su, sai dai ya zauna ya yi ta zuba mata hira yana sanyata nishaɗi, Ummi na matikar kula da Aafia tamkar ita ta haifeta, ko ban faɗa ba kunsani, ta fi Hjy Hadiza sau dubu, dan ita dai Hjy Hadiza bata kula da ƴaƴan ba, kenan abin da nake nufi a nan shi ne, Ummi tana kula da Aafia fiye da uwar da ta haifeta.
Ba laifi Aafia na ƙoƙarin shiga kitchen ta taya Ummi aiki, suna yi suna hira, wani lokaci Nawid yana shigowa ya taya su, Ummi ta yi ta tsokanar shi wai yanzu kam ya san hanyar kitchen kenan, da sai dai ya zauna yana isar mutane da Ummi kaza zaki dafa mana yau, yanzu kuma har da shiga kitchen dan ya yi mata, kamar wani jikarta haka Ummi ke tsokanar shi, sai dai ya yi ta Murmushi dan bai san me zai gayawa Ummi ɗin ba.
Rayuwarsu abin burgewa da ban sha'awa, sun mai da Ummi kakansu, idan suna wani wasan ba zaka so su dai'na ba, saboda burgewa da ban sha'awa.
Kwance take a saman gado da misalin karfe huɗu na yamma, Nawid baya nan, ita kaɗai ce, Ummi na ɗakinta, gabaɗaya ko'ina a gyare tsab, sai kamshi yake tashi.
Sanye take da doguwar riga mai shegiyar kyau, launin pink color, duk kuma kayan jelly ce, Ummi ta ce sai sun huta, su shirya zuwa sayan mata kayan lefenta, shiyasa take amfani da na jelly tun da suna yi mata daidai.
Tayi simple make up a face nata, sai tashi wani irin fitinannen kamshi take yi, ta ɗaga kai sama da alama wani abin take tunani, karar ringing ɗin wayarta ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta faɗa.
A nutse ta miƙa hannu saman bedside drawer ta ɗauko wayar. Umaisha itace mai kirar tata, nauyayyar ajiyar zuciya ta sauƙe kafin ta ɗauki kiran. "Hello Umaisha". Ta faɗa tana miƙewa zaune a tsakiyar gadon.
"Aunty Afi ina ta jiranki tun shekaran jiya baki kirani ba, Allah ma yasa bamu samu damar zuwa gida ba, amma kuma naji yaya Akil ya ce yau zamu je, shi ne na kiraki in ji hukuncin da kika yanke, in ɗaukawa Ommu kuɗin ne ko yaya? Wlh ina jin tsoro sosai". Tana magana tamkar zata yi kuka.
"Umaisha shi ne ko sallama babu bare gaisuwa? Ki natsu mana". Kamar zata saka ihu ta ce "Kiyi hakuri Aunty Afi, ina cikin matsananciyar damuwa ce, shiyasa ma na manta da wata gaisuwa, to ina wuni yasu yaya Nawid?".
"Lafiya lou ya yaya AKil?" "Yana nan lafiya". Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Kina ji Umaisha? Magana ta gaskiya dama ina son in kiraki, kasan cewar kwana biyun nan Yaya Nawid yana nan bai fita bane yasa ban kiraki ba, dama ina Allah Allah kada ki ɗauki kuɗin, to Alhadulillah da Allah yasa ma baku je gidan ba, yanzu dai abin da nake so da ke shi ne, idan kunje gida ki gayawa Ommu yaya Akil bashi da kuɗi, bai ajiye a gida ba, amma duk ranar da ya kawo kuɗin gida, zaki ɗebo mata ko nawa take so, kinga idan kika gaya mata haka ba zata ce kinki ɗauko mata bane, ba zata ɓata rai ko ta yi fushi dake ba, kinga bata isa ta ce a ciro mata a account nashi ba, dole ta hakura ta jira sai ranar da ya kawo kuɗin gida, kafin lokacin kuma zamu nemo wata shawara, amma ba Ommu ba kome zai faru kada ki kuskura ki saci kuɗin mijinki, kai bana mijinki kawai ba, na kowa da kowa ma, kada ki yarda ki ɗauki abin da ba naki ba, duk wanda ya roƙe ki abu, idan ya fi karfin aljihunki, sai ki bashi hakuri babu wani zancen ɓoye ɓoye, kuma duk wani abu idan ya taso kada ki kuskura ki yi gaban kanki, ki gaya mani ko ki gayawa yaya Irfan, idan ba zaki iya gayawa Abbi da yaya Akil ba, kina ji na ko?".
Dogon numfashi ta ja tare da sauƙewa a hankali. "Aunty Afi na ji daɗi sosai, kuma ina godiya ga Allah daya bani ƴan uwa masu ƙaunata, nagode da shawararki a gareni, zanyi amfani da ita In Sha Allah".
"To shikenan mummyn Abbi in ji yaya Akil na ba, zan ji daɗi fa sosai idan yaya Akil ya cika alkawarinsa ya yi wa Abbi takwara". Dariya sosai Umaisha ta yi, tana matikar kaunar cikin nan nata, ko in ce suna matikar kaunar kayansu ita da mijin nata.
Da sallama ɗauke a bakinsa ya shigo cikin ɗakin, ganin shi yasa ta ce da Umaisha za su yi waya anjima, da haka suka yi sallama.
Ɗaura wayar saman bedside drawer ta yi tare da miƙewa da sauri ta nufe shi tana murmushi, sai wani lumshe idanu yake yi alamar a gajiye ya dawo, sanye yake da kayan aikinsa, daga ta ciki kuma suit baki ne kafin ya ɗaura rigar tasu ta likitocin, hannunsa na riƙe da bakar jaka mai shegen kyau, while kafarsa na sanye da cover baƙa, daga ciki kuma bakar safa ce a ciki, ya fito a cikakken likitansa.
Karisawa wajensa ta yi tana kara faɗaɗa murmushinta, shi ma murmushi yake sakar mata tare da buɗe mata hannu akan ta yi mashi oyoyo, kin yi mashi tayi, tana zuwa ta karɓi jakar hannunsa, zata juya ya yi maza ya riƙota.
"Ina zaki je ba tare da kin yi mani oyoyo da kuma sumbata na welcome back ba?". Kasa ta yi da kanta bata ce mashi komai ba.
"Haba matata, na fa gaji sosai, kuma nasha wahala, amma shi ne zaki zo ki karɓi jaka kawai, ba wani ɗan sumbata? Baki san cewa idan kika sumbace ni zan ji gajiyar ta gudu mani ba? please mana". Ya kai karshen maganar a ɗan shagwaɓe.
Bata san lokacin da ta juyo ta rungume shi ba, ya iya magana sosai, ta haka kuma yake bi da ita, har ya sanya ta ta yi abinda bata yi niya ba, ta haka yake kore mata duk wata damuwarta, ya mantar da ita komai.
Sosai ya sanya hannu biyu ya riƙota da kyau, tare da kara matseta a jikinsa yana mai jin tsantsar farinciki yau ta rungume shi.
Sun ɗan jima kaɗan a haka, kafin nan ya sanya hannu ya ɗago haɓarta suna fuskantar juna, idanunta a lumshe.
"Kinyi kyau over my mata". Ya faɗa kasa kasa. Duk da idanunta a rufe, sai da ta saki haɗaɗɗen Murmushi, da yawan mata suna son ace sun yi kyau, shi kuma ya kware wajen iya yabon mace, shiyasa ma ta yi saurin kware mashi haka.
"Saura sumbata, ko dai yau za'a bani har da kiss ne?". Ya yi maganar cikin sigar zolaya.
"Ni fa yaya Nawid ban iya ba". Ita ma cikin sigar zolaya ta yi maganar. "In koya maki ne? Kin bani dama?". Kai ta gyaɗa mashi alamar e.
Wani irin daɗi ya ji sosai tare da sakin haɓar tata ya saketa yana faɗin "Bari na yi wanka to, ko dai zaki tayani yi ne?". Da sauri ta juya ta bar wajen tana faɗin "A'a zan dai fitar maka da kayan sakawa, daga nan kuma na ɗauko maka abincinka". Murmushi ya yi tare da karisawa ciki ya fara rage kayan jikinsa.
Ita kuma bayan ta ajiye jakar a mazauninsa, sai ta wuce ta fice daga ɗakin ta nufi Palo, binta da kallo ya yi yana mai jin kaunarta na ninkuwa a ransa.
Abinci ta ɗauko mashi, da yake yanzu a ɗaki take kawo mashi abinci su ci a tare, Ummi ce ta ce su rinka ci a ɗaki, dan ta lura da shi Nawid yana son suna cin abinci suna wasa da dariya tsakaninsu na masoya, ita kuma Aafia tana jin kunyar yin hakan a gaban Ummin, da yake Ummi mace ce mai adalci, ga lura, sai ta gane hakan, dan haka sai ta ce A'AFIA ta rinƙa kai masu abincin cikin ɗakinsu suci a tare.
Lokacin da ta ɗauko abincin ta dawo ɗakin, har ya cire kayansa ya shiga toilet, saman Chinese carpet