Showing 213001 words to 216000 words out of 359620 words
da shi, shi ne zaɓinta, bazata iya rayuwa da wani namijin bayan shi ba.
Ganin tana hawaye ba ƙaramin ɗaga mashi hankali ta yi ba, cikin sauri ya sake hannayenta tare da ɗago haɓarta suna fuskantar juna, muryarsa har sarkewa yake yi wajen cewa "My Heartbeat please and please ki yi shiru, ki yi hakuri kada ki kara mini zafi a kan zafi, zan iya jure komai amma ban da kukanki heartbeat nawa, wlh hawayenki na bakin ciki, daidai yake da ana caka mini wuƙa a kahon zuciyata, zafi nake ji my heartbeat idan kina kuka, ni zan iya ɗaukar komai ban da kukanki, ki daina please". Yana magana yana hawaye shi ma.
Cikin kuka ta ce "My shagwaɓati kukan ka yafi nawa zama tashin hankali da bala'i a gare ni, ka daina dan Allah, wlh idan kana hawaye zuciyata zata iya bugawa ka ji?".
Bai san time da ya jawota jikinsa ba, wani irin shock suka ji su dukkansu biyu, dannewa ya yi tare da fara rarrashinta cikin salo da dabara tare da natsuwa, tamkar kara ingiza ta yake yi, sai kara kukan take yi, ta lafe a kirjinsa tana jan hanci tare da shaƙar daddaɗar kamshin perfume nasa mai kwantar mata da hankali.
Hannu yasa ya ɗago haɓarta daga saman faffaɗar kirjin nasa, ya zama suna fuskantar juna, goge mata hawaye ya shiga yi yana mai cigaba da rarrashinta, kukanta babbar bala'i ce a gare shi, zuciyarsa ba zata ɗauka ba.
Ganin taki daina ruwan hawayen ne yasa ya ranƙwafo kanta sosai tare da fito da harshensa ya fara lashe hawayen nata, cak ta tsaya da kukan nata sakamakon wani irin baƙon yanayi da ta ji na sanya harshensa a kan fuskarta da ya yi.
Shi kuwa tas ya lashe hawayen nata kafin ya ɗago da brawn eyes nasa ya sauƙesu cikin tata fararen idanun. Da kyar ya ƙaƙalo murmushin dole dan ya sanya ta farinciki, zuba mishi ido ta yi, ba ko kyaftawa, shi ma dai zuba mata dara daran idanuwansa ya yi yana mai kare mata kallo.
Sun ɗan ɗauki lokaci a haka kafin ya matso da fuskarsa daf da tata sosai ta yadda suna iya jiyo numfashin juna, can kasan maƙoshinsa da kyar ya iya furta "Can i kiss you one my heartbeat?". Wani irin faɗuwar gaba ta ji jin yadda ya yi maganar, ji take yi tamkar rabuwa da shi zata yi, ta kasa magana, ta dai zuba mashi ido kawai.
Ganin bata yi magana bane yasa ya matso da lausasan laɓɓansa zuwa saman tata, wani dogon numfashi ta ja tare da sauƙewa a hankali, yayin da shi kuma ya sauƙe nauyayyar ajiyar zuciya, a hankali cikin natsuwa ya haɗe bakinsu ya shiga kissing nata.
Sumar zaune ta yi mishi, ko da sunan wasa ba wanda ya taɓa kissing nata, bata ma san ya ake ji ba idan aka yi kiss sai yau, tana dai karance karance novel nata, da kalle kallen film, amma bata taɓa ji a zahiri ba.
Shi kuwa kara jawota jikinsa ya yi tare da rungumota da kyau da kyau, kissing nata yake yi babu kama hannun yaro, cikin dabara ya zame mata mayafin kanta tare da ɗankwalinta baki ɗaya, shi ma bai taɓa yin kiss ba, bai san ya ake ji ba sai yau, kuma yau ɗin ma ya haɗu da ya yi wa macen da ya fi kauna a duniya, wow abin ba'a magana.
Shafa kyakkywar gashin kanta da ya sha gyaran biki ya shiga yi yana mai kara matseta a jikinsa bakinsu na a cikin na juna.
Sosai ya yi kissing nata, ita kuma ta yi mashi sumar zaune, duk jikinta ya mutu, ko motsin kirki ta kasa yi, bata ankaraba sai jin sauƙar hannunsa ta yi a saman breast nata, cikin sauri ta kwace bakinta tare da ja baya daga jikin nasa tana mai laluɓar ɗankwalinta.
Idanunwansa sun yi jawur, murya na rawa ya ce "My heartbeat lafiya kuwa? Me yasa zaki hanani?". Shiru ta kasa yi mishi magana, sai faman ɗaura ɗankwalinta take yi, tanayi tana hawaye, ji take yi kamar shikenan zata rabu da shi.
Tana ƙoƙarin mayar da mayafin nata ya yi saurin riƙewa yana faɗin "My heartbeat talk to me now".
Sai a lokacin ta ɗago idanuwanta wadda suke cike tap da ruwan hawaye, ga shi wasu kuma suna zuba mata a saman face nata, wani na bin wani.
"Ya subhanallah, Heartbeat me ya faru kuma kike sake yin kuka haka? Saboda na yi kissed naki ne? To idan saboda haka ne ki yi hakuri, na tuba, bazan kara ba, kin ji ko? Please ki daina kuka".
Kin yi mishi magana ta yi, da sauri ta sakin mishi mayafin tare da fita daga cikin motar, da gudu ta nufi gida tana sakin kuka mai sauti, tasan ko zata mutu Abba ba zai canza magana ba, dole gobe a ɗaura aurenta da Irfan, ga shi kuma ta zo ta yarda Heartbeat nata ya yi mata kiss, yanzu me makoman hakan kenan? Taci amanar yaya Irfan ko dai yaya?. Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun.
Cikin sauri da zafin nama shi ma ya fito daga cikin motar, hannunsa na riƙe da mayafinta da ta bar mishi. Kafin ya fito har ta shige ciki gida, kifa kansa ya yi a jikin motar yana kuka tare da dana sanin kissed ɗin nata da ya yi, a tunaninsa hakan ce tasa ta gudu, kuma hakan ce ta sakata kuka sosai.
Ya jima a wajen ya kasa motsawa, banda ruwan hawaye babu abin da yake yi, lokaci guda duk ilahirin jikinsa ya yi zafi jau alamar zazzaɓi, zuciyarsa tamkar zata fashe, sai da ya kwashi good 30 mins a haka, da kyar ya iya lallaɓawa ya shiga cikin motar.
Wayarsa ya ɗauko ya fara kiran number ta, dan ya rarrasheta ta yi shiru, yasan halinta sarai, yanzu tana can tana kuka, ba zai iya tafiya ba idan har bai rarrasheta ta yi shiru ba.
Sau uku yana kiranta bata ɗauka ba, sai a na huɗun ne ta ɗauka, ban da kuka babu wani sauti dake fitowa daga cikin wayar, dafe kansa dake barazanar tarwatsewa ya yi, zuciyarsa na bugawa da sauri da sauri, da kyar yake fitar da numfashi mai zafin zazzaɓi, su dukkansu biyu sun kurɓi gubar soyayya, hawaye babbiyu yake zuba mishi daga idanunsa, ya kasa magana, ita ma ta kasa magana, dukkansu sai kuka suke yi wa juna,..... To fa, waye kenan zai rarrashi ɗan uwa? HEARTBEAT+ HEATHER ƴan auta kenan, kuma shagwaɓaɓɓu, bugun zuciyar family'ns guda biyu, sanyin idanunyar mutane da dama, BABBAR MAGANA akwai kallo da.
❤️❤️TRIPLETS❤️❤️
*Duk wace ta karanta mini littafina ba tare da ta biyani hakkina ba Allah ya isa ban yafe ba, sai Allah ya tsayar da mu ranar da bata da abin da zata biyani face ladarta*
💋Dedicated to My comments section groups people's🌹
E55-56💋
Jin irin sautin numfashinsa dake fita ta cikin wayar ne yasa ta tsagaita da dukan da take yi, a ruɗe cikin tashin hankali ta ambaci sunansa, shiru ya kasa amsawa, sake kiransa ta yi hawaye wani na bin wani a fuskarta, tana kwance a saman bed ɗin Akil, nan ma shiru, sau uku tana kira bai amsa ba, dan ba zai iya magana ba.
A tsananin razane ta miƙe zaune tare da dirowa kasa ta nufi waje, tamkar wata zararriya haka ta nufi waje babu ko mayafi a jikinta, ƴan biki suna ta hidimar gabansu, sai aikace aikacen girke girke da sauransu suke yi, haka ta keta mutane ta nufi waje.
A guje ta nufi motar tasa, ya kifa kai da jikin steering motar yana wani irin numfashi wanda da ka ji kasan da kyar yake fitar da ita, a tsananin tashin hankali ta buɗe motar ta shiga, sunansa ta rinƙa ambata Heartbeat! Heartbeat, amma ina ya kasa amsawa, jijjiga shi ta fara yi, jin irin azababben zafin da jikinsa ya yi yasa ta kara tsorata sosai tare da yin yunkurin ɗago kansa daga jikin steering dan ta kalli face nasa.
Tana ɗago shi ya sake mata jiki ya kwanta a saman kafaɗarta yana fitar da numfashi mai tsananin zafi, girgiza kumatunsa ta fara yi tana ambatar sunansa, ina ko motsin kirki baya yi, ban da wannan numfashin da yake fitarwa babu wani abin da zaka ji a tattare da shi, wayar dake hannunsa ta karɓa dan ta kira ɗaya daga cikin ƴan uwansa su zo kada ya mutu.
Kash wayar da akwai password a jikinta, tamkar zuciyarta zata fashe ta fito waje haka take ji, cikin fitar hayyaci ta fara lalauɓar number Imran a wayarta da ta fito da ita, har lokacin ko motsawa bai yi ba.
Bugu ɗaya ta yi wa Imran ya ɗauka, kuka ya hanata wani maganar kirki. "Yaya Imran ka zo, kazo Heartbeat zai mutu". "Akila ki natsu ki yi mini magana, na zo ina kuma?". Da kyar ta iya cewa "Kazo waje, yana waje". Daga haka ta katse kiran ta cigaba da ambatar sunansa.
Tana kashe wayar sai ga shi ya fito da sauri, nufo motar tasu ya yi, cikin sauri ya buɗe kofar ɓangaren da take, ba ƙaramin tashin hankali ya shiga ba ganin abin da yake faruwa, ina ai idan wani abin ya sami Aseef a dalilin familynsu ya san sun shiga uku da Lion, dan ba zai taɓa ɗaukar wannan kaddara ba, shi da likitoci ma suka tabbatar mishi da Aseef ɗin ya mutu a baya, amma ya kafe ya ce sam ba za'a binne shi ba, ba wanda zai sanya mishi ɗan uwa a rami, bare kuma yanzu Aseef ya mutu sanadiyar AKila, ai wlh duk sai Lion ya kashe su har lahira, idan ma bai haɗa da mai gadi da kowa da kowa ba, ai duk wanda ma ya zo bikin nan sai ya mutu.
Fita ya ce ta yi bari ya duba Aseef ɗin, da kyar ta iya raba jikinta da na shi, ta kwantar da shi a jikin headboard na kujerar ta fito, sai kuka take gwanin ban tausayi, shi ga cikin motar ya yi yana ambatar sunansa, amma ina ba zai iya amsawa, ya rigada ya kurɓi gabar soyayya.
"Akila ki koma cikin gida bari na mayar da shi gida dan ayi gaggawar duba lafiyarsa kin ji?". Durkushewa a kasa a wajen ta yi tana kuka kamar ranta zai fita, cikin kuka ta ce "Yaya Imran dan Allah ka tafi da ni, wlh ba zan iya zama ban san halin da yake ciki ba". Tana magana tana dafe kirjinta da yake yi mata tsananin ciwo tamkar zata mutu.
"A'a Akila ki je gida, idan na tafi dake abin ba zai yi mana kyau ba dukkanmu, ke dai ki je gida, baki san waye kike tare da shi ba ne shiyasa kike cewa na tafi da ke, so ki koma kawai". A gudu ta miƙe ta nufi gida, binta da kallo ya yi yana matuƙar tausaya musu, ya rasa ya zai yi, tunani yake a kan wlh dukkansu biyu zasu iya mutuwa fa idan ba'a duba wannan lamari ba.
Fitowa ya yi daga cikin motar ya dawo ta ɓangaren da Aseef ɗin yake ciki, ya buɗe kofar, da kyar ya iya fito da shi ya mayar da shi gidan baya, sannan ya shiga mazaunin driver ya tada motar, da gudun gaske ya figita dan su isa gida da wuri, idan ba haka ba daga yanzu zuwa ko wani lokaci suna iya rasa Aseef ɗin bakiɗaya.
Horn ɗaya ya yi Donald ya buɗe mishi gate ɗin, dan gateman kam yana gadon asibiti bai farfaɗo ba, ciki ya danno hancin motar, yana kasheta ya fito da sauri ya nufi cikin gida, ya kuwa yi sa'a ya sami Areef da daddyn Rimsha a palo suna hira, Rimsha kuma ta tafi school bata nan daddynta ya iso, sai dai ta dawo ta same shi kawai, Jehan tana ɗaki tana barci.
Cikin tsananin tashin hankali ya ce da Areef "Ina Lion?" Miƙewa Areef ɗin ya yi yana kallonsa da mamaki na lafiya?.
Lion baya nan ya fita neman Aseef ɗin ne, dan ya yi ta kiran numbersa bata shiga, suna zaune suka ji su coper suna ta daka haushi, hakan yasa Lion ɗin yasan Aseef baya lafiya, shi ne ya yi ƙoƙarin neman numbersa network babu kyau, bai same shi ba, wannan dalilin yasa ya fita nemansa.
Areef na kokarin tambayarsa ko lafiya ya shigo a birkice haka, sai suka ji tsayuwar motar Lion a harabar gidan, da sauri Imran ɗin ya juya, dan ba zai gayawa Areef me ake ciki ba, yasan ba zai iya ɗaukar Aseef ba saboda ciwonsa, dan haka sai ya nufi wajen kawai.
Da sauri suka rufa mishi baya, Lion na shigowa shi kuma yana fita, karo suka yi, baya yaɗan yi yana gaya mishi ya zo ya fito da Aseef daga cikin mota, ya yi sauri dan yana bukatar taimakon gaggawa, ɗan zaro idanu ya yi, ya ma kasa tambayar me ya sami ɗan uwan nasa, dan ba zai iya jin mummunar labari a kan TRIPLETS nasa ba, bai shiryawa hakan ba, kuma ba shi da wannan juriyar gaskiya.
Cikin sauri suka rankaya zuwa wajen motar, a zafafe Areef ya buɗe kofar ɓangaren da Aseef ɗin yake ciki, dan jikinsa har tsuma take yi yana son ya ga menene ya sami ɗan uwansa. Yana zaune kansa na jingine da jikin headboard na kujerar, tamkar babu rai a jikinsa, da alama ya suma ne, ga kuma mayafin Akilar a hannunsa bai saki ba, ya riƙe gam.
Areef zai taɓa shi Lion ya dakatar da shi tare da kai hannu dukka biyu ya tallaɓo shi, Imran kam baya ya yi yana jiran ya ga saukar aradu kawai, dan kuwa yasan akwai yaki yau ba kaɗan ba, wani abu ya sami Aseef dalilin AKila, tab aikuwa Akila zata mutu a tunaninsa.
Ciki Lion ya wuce da shi bayan ya saɓa shi a kafaɗarsa, har lokacin mayafin Akilar na hannunsa, saman bed nasa a bedroom nasa ya kwantar da shi, kallon juna Imran da Areef suka yi, yana ƙoƙarin tambayarsa menene ya sami ɗan uwan nasa, sexy voice ɗin Lion ya katse shi da cewa "Bani ruwa Areef". Da sauri ya nufi fridge.
Roba ɗaya mai sanyi ya ɗauko ya dawo ya miƙa mishi, karɓa ya yi tare da buɗewa ya tarfo a hannunsa, a fuska ya shafawa Aseef ɗin, shiru bai motsa ba, sake tarfowa ya yi ya shafa masa, nan ma shiru, sai a karo na uku ne ya ja dogon numfashi tare da saukewa a hankali, sai kuma kuka ya biyo baya, dukkansu zuba mishi idanu suka yi suna kallon ikon Allah.
Kuka yake yi sosai, idanuwansa a datse gam ya fara sambatu. "Ki ce da Abba wlh zan iya mutuwa, ba zan iya jurewa ba, ki yafe mini dukkan abin da nayi miki a rayuwar da muka yi tare, ni nasan yau ba sai gobe ba zan rayu ba, mutuwa zan yi, zuciyata tana yi mini zafi sosai, mutuwa zan yi my heartbeat, ba zan rayu ba, idan na mutu ki rinƙa yi mini addu'a kin ji? Kuma kada ki manta dani, kin ga dai kin yi mini alkawarin ba zaki rabu da ni ba ko? Kuma ba zaki manta da ni ba, to dan Allah kada ki manta da ni, ki cika alkawari".
Juyowa Lion ya yi da kallonsa zuwa kan Areef while shi kuma Areef ɗin ya juya yana kallon Imran, shi kuma Imran daddyn Rimsha yake kallo. "Me ya sami my pleasure?!" Lion ya tambaya cikin tsawa. A tare dukkansu suka dawo da kallonsu kan shi.
Jin muryar Lion ɗin yasa Aseef ɗin dakatawa daga sambatun da yake yi, a hankali ya waro idanuwansa da suka riƙiɗe suka yi ja sosai na wuce misali, da kyar ya kai hannunsa ya riƙo hannun Lion ɗin, jin ya kama hannunsa yasa ya juyo da kallonsa kansa.
Zuba mishi idanu ya yi kafin ya kankame hannunsa cikin na shi, "My pleasure what is happening? What is wrong with you? Who break your heart?" Cewar Lion ɗin kenan.
Ba ɓoye ɓoye ya gaya mishi komai, tun farkon ganinsa da Akika har yau da suka yi sallamar bankwana, daga karshe ya rufe da cewa "Ba zan iya rabuwa da ita ba Lion, mutuwa zan yi yau na sani, aurenta za'a ɗaura da wani, ba zan iya juran hakan ba, burina a duniya bai wuce na aureta muyi rayuwa a tare ba, shi ne burina na karshe kuma zan mutu da shi ban cika ba, zafi zuciyata take yi mini sosai, ku yafe mini duk abin da na taɓa muku a rayuwarmu, ni na san ba zan tashi ba, ina ji a jikina mutuwa zan yi, zafi nake ji my TRIPLETS, ban san ya zan yi ba, jikina ciwo yake yi mini, amma dan Allah idan na mutu, in kun zo binne ni ku sakani da mayafin Heartbeat data bar mini, shi ne abinta ɗaya kawai da nake da shi, dan haka ku rufeni a rami da shi". Yana magana yana tari tare da fitar da wani irin numfashi mara daɗin ji na zafin zazzaɓi.
Duk taurin zuciya irin na daddyn Rimsha sai da ya yi hawaye, Imran kam tuni dama hawaye ya wanke mishi fuska sosai.
A ɓangaren Akila kuwa, bata kai ga shiga gida ba Abba ya ganta, ganin haka yasa ya ce da Abbi ya taro dukka mazan gidan yau za'a ɗaura auren nan, dan kuwa ya ga komai, ya ga motar Aseef, shiyasa dan gudun abin ya zama matsala ya san halin Turawa yanzu Aseef yana iya ɗaukarta su tafi kasarsu ma ko kuma ya biya bukatarsa da ita, shiyasa dan gujewa hakan ya ce a ɗaura auren yau kowa ya huta, bai san cewa Aseef kam soyayyar gaskiya yake yi mata ba, tsakani da Allah yake sonta babu wasa ko kaɗan, so ba zai taɓa kwanciya da ita ba tare da aure ba, lokacin da yake krista ma bai yi zina ba, baruwansa da mata, yanzu da ya musulta ya san girman Allah ba zai taɓa aikata hakan ba.
Lokacin da ta samu labarin Abba ya ce yau za'a ɗaura aurenta, a haukace ta nemo wayarta ta fara kiran number Aseef ɗin, sai kuka take yi.
Sau uku ta kira bai ɗauka ba dan wayar ya barta a mota, number Imran ta kira, bugu ɗaya ya ɗauka dan ya ji tana lafiya ne ko yaya, saboda shi ma bai cire rai