Showing 168001 words to 171000 words out of 359620 words
A'A ma gabaɗaya cikin turawa suka yi karatun, so babu wata kunya a lamusansu, wannan dalilin ne ma yasa zaku sami Abbi da Aunty a palon kasa suna soyayyya, Aunty ta tada kai da cinyarsa ko a jikinsu, shiyasa suke zuba love iya son ransu har su daddyn jelly babu mai jin kunya yin soyayyya, misali lokacin da su Akil suka zo da matansu, ai kunga haɗuwa suke yi a palo, kowa yana kula da matarsa babu kunya, to uzuri zaku yi musu, suma ruwa biyu ne ba ɗaya ba, shiyasa suke a haka, kuma su su Abbi idan baku manta ba, a can suka taso har sai da suka zama manyan samari kafin su dawo nan, daddyn Jelly shi kaɗai Naurat ta haifa a Nigeria, shiyasa idan kuka lurama duk cikinsu shi ne kaɗai mai ɗan kunya, kuma yana nuna kunyarsa a fili kowa ya san shi da ita, amma hakan baya nufin shima ɗabi'ar Turawan ya kyale shi, a'a akwaita sosai, ciki kuma har da zuba love babu kama hannun yaro, kuna dai ganinsa shi da Jelly'nsa ma bare kuma Ayla da take matarsa, ai abin nasu a jini yake.
"Kina sona Hanan?" Ya yi maganar yana kara tsareta da idanun, da yake ita kam jinin Katsina da mutan Kaduna ne, akwai kunya a lamuranta, sai ta kasa magana, tana son tashi ta bar wajen ma ta kasa, saboda tana ganin idan ta tashi za'a ce ta dawo, kuma ga kowa yana kallonta, dan haka sai ta cusa kanta cikin cinyoyinta tana murmushi, dan tana son A'A, ya yi mata, kuma shi ma irin mijin da kowacce mace zata buƙata ne, akwai kyau sosai na jinin Hausa Fulani, akwai kuɗi, ga ilimin addini da boko ba kaɗan ba, nitsastse da shi, bashi da hayaniya, so har cikin ranta tana kaunarsa, tun ranar ma da ya zo ya yi mata kyau sosai, ta rinƙa satar kallonsa.
Aunty ce ta katsesu da cewa "A'a fa Hanan kada ki yi mana hakan, ya muna shirin komawa India zaki wani ɓoye fuska, ki ɗago ki gaya mishi gaskiya kina son shi ko yaya?". Ta yi maganar cikin zolaya, shi dai Irfan sai murmushi yake yi bawan Allah, duk ya rame kamar mai wani ciwon, kuma ba wani ciwo da yake damunsa, kawai rashin samun kwanciyar hankali ne ta sako shi a gaba.
"Kada ku takurawa ƴa ta" Cewar daddyn Jelly, hannu A'A ya saka ya karɓi wayar da yake hannunta, numbersa ya sanya a wayar tata ya yi flashing, sai ga number tata ta shigo wayarsa, mai da mata da wayar tata ya yi a cikin hannun nata yana faɗin "Yaya Maik ku kyaleta ne, zuwa gobe zan dawo muku da amsa". Ita dai maman Ayla sai kallon A'A take yi, ita kuma Aylar sai zuba barci take yi a cinyar mijin nata, kunsan yanzu tana mumzalin barci ne, da ta kwanta kaɗan sai barci abinta.
A'A na ƙoƙarin sake yin magana aka sako labarai a Tv, "Ku kara mana Volume". Cewar Abbi, Aunty ce ta kara Volume ɗin, natsuwa suka yi dukkansu dan saurara, wata ƴar jarida ce ke magana kamar haka "A safiyar yau ne Allah ya yi wa shararren ɗan siyasarnan wato ABUBAKAR SALAHUDDEEN rasuwa, ya rasu ne kuma sakamakon taimakon da ya je yi, duk wanda ya san ABUBAKAR SALAHUDDEEN ya san shi mutun ne mai taimakon talakawa, yana kan hanyarsa ta zuwa gidan hutawarsa dake cikin Kaduna ya hangi wata yarinya a bakin titi tana zaune tana kuka, matashiyar budurwa ce da zata kai shekaru 18 zuwa 19 a duniya, ganin hakan kun san shi da taimakon yasa ya ce a tsayar da mota, da kansa ya fita ya nufi in da wannan yarinyar take zaune tana kuka, dan kunsan duk mai hankali ya ga yarinya budurwa da daddare a kan hanya tana kuka dole zai tambayeta ko me ya faru, yana isa wajenta dan ya tambayeta me ya faru, yarinyarnan ta zaro wuƙa mai kaifin bala'in ta shammacesa ta daɓa mishi da iya karfinta a cikinsa, daga shi sai wasu ƴan'sanda biyu dama suka tafi, nan take ya yi kokarin faɗuwa kasa ƴan'sandan suka riƙe shi, a nan ne ita kuma yarinyar ta gudu, dan babu security sosai a tattare da shi lokacin, gidan hutawarsa zai je ya huta, shiyasa bai ɗebi securitys ba, dama kun san mafiya yawancin lokaci haka yake yi, daga nan ƴan'sandan suka ɗauke shi zuwa asibitin, tun a hanya Allah ya yi mishi cikawa, ya ce ga garinku, a safiyar yau muka sami labari, ita kuma yarinyar ta gudu, sai dai an yi nasarar samun hoton fuskarta, a yanzu haka jami'an tsaron su bazama nemanta, wannan shi ne hoton ABUBAKAR SALAHUDDEEN tare da makashiyarsa JEHAN NAWAZUDDEN, da ƴan'sanda suka sami hotonta ne, a nan ne muka san cewa ƴar gidan Nawazudden ce, wanda ya kasance tsohon ɗan takarar shugaban kasa da ya rasu ta hanyar haɗari, sai abin mamaki a nan shi ne, Nawazudden dai ya mutu da shi da family'nsa dukka, to bamu san ya akayi ita kuma Jehan ta kasance a raye ba, hukuma suna nan suna bincike, kome yake ciki zamu rinƙa kawo muku labarai a kai a kai, ku kasance damu, mun gode da sauraran mu". Babbar magana, masu karatu, akwai lauje cikin naɗi, da ni da ku duk mun san cewa wannan labaran ba gaskiya bace, da farko Jehan bata kai 19 years ba 16 to 17 years gareta, na biyu kun san ba'a kan hanya ta daɓa mishi wuƙa ba, a cikin gida ne, kuma ba ɗaɓa mishi wukar a ciki ta yi ba, yanke mishi gaba ta yi, amma ya akayi cikin ƙanƙanin lokaci a ka juye maganganun dukka, kenan dan a rufawa ABUBAKAR SALAHUDDEEN asiri ne a matsayinsa na ɗan siyasa ne a kace hakan ko kuma yaya abin yake,? Lallai an shiryawa Jehan kadar zare ba na wasa ba, daga ganin wannan abin babban shiri ne daga abokan gaban mahaifinta, dan yanzu faɗar ta koma ta siyasa, ba abin da zamu ce sai dai Allah ya kuɓutar da Jehan, mu dai je zuwa, komai zai warware a hankali, ku kasance da alkaramin Fateema Zahra Musa dan jin yadda zata kasance.
A wani irin mahaukacin razane A'A ya miƙe tsaye, dan ABUBAKAR SALAHUDDEEN ba kowa bane face mahaifinsa da ya haifesa, AHMAD ABUBAKAR SALAHUDDEEN shi ne suke ce mishi A'A, miƙewa su Abba ma suka yi dan su taushe shi, saboda duk sun san mahaifinsa ne, miƙewa ita ma maman Ayla ta yi tana faɗin "Alhadulillah, Alhadulillah, Alhadulillah, Allah na gode maka da ka muna mini mutuwar Abubakar kafin na bar duniya, azzalumin, mugu, macuci, banso ka mutu a haka ba, na so ne ka mutu a walaƙance, wanda ko kare sai ya fika daraja, bakin shaiɗani". Tana magana tamkar wadda ta zare, da alama farinciki ne ya yi mata yawa.
Kwantar da Ayla a hankali daddyn Jelly ya yi tare da miƙewa yana faɗin "Mama lafiya me yake faruwa,? Menene tsakaninki da Abubakar kuma?". Nisawa ta yi tana ta uban murmushi wadda tun da ta zo gidan bata taɓa yin shi ba "Abdul Malik wannan Abubakar ɗin da kake gani ba mutun bane, shaiɗan ne yazo a siffar mutun, ba kuna tambayata waye uban Aliya ba,? To shi ne, shi ne uban Aliya". Tashin sense da ba'a saka miki date. Nan take kallo ya dawo kanta, gabaɗaya palo suka zuba mata ido, Ayla baiwar Allah sai zuba barci take yi, bata san me yake faruwa ba.
"Shi ne mahaifin Ayla kuma?" Cewar Abbi, "Kwarai kuwa shi ne uban Aliya, babu wata tantanma, bakin azzalumin, ai naso Aliya ta girma ta kai mishi kanta da kanta ne, idan ya isa yanzu kuma ya ce ba yarsa bace, ai da yake Allah ba azzalumin bawansa bane, da ya tashi bani ita sai ya bani ita kaman uban nata sak, babu in da ta baro shi, lokacin da take cikin cikina, ya ce ba cikinsa bane, ni kuma nasan ba mazinaciya bace, ban taɓa zina ba sai da shi, bayan shi ni ban taɓa kusantar wani ɗa na miji ba, nasan cikinsa ne, amma ya ce ba nashi bane, ya barni cikin bakin azaba da wahala, saboda son kai irin nasa, to ga shi yanzu babu wanda ya isa ya ɗaga idanu ya kalli Aliya ya kuma kalli Abubakar ya ce ba ubanta bane, kama harta idanunsa bata bari ba". Tana magana tana murmushi yau zuciyarta fari tas.
Cikin dakiya Abbi ya ce "Dan Allah ki yi mana bayani dallah dallah yadda zamu gane, ya akayi ya zama mahaifin Aliya? Kun taɓa yin aure da shi ne?". Dariya ta yi kamar zautatciya, da alama ta cutu sosai na abin da ya yi mata, da alama yau farincikin ya zautar da ita baiwar Allah, bata jin komai yau sai murna, dan haka bata damu ba zata iya wangale komai yau, dan tasan ko bata faɗa yau ba, to dole gobe ta faɗa, dan dole mijin Ayla ya buƙaci jin tarihinta.
Dan haka nan take ta buɗe musu aiki mai gabaɗaya "Ni ban taɓa yin aure ba, Aliya shegiya ce kuma ga ubanta nan a gabanku yanzu aka gama labarai a kansa, yanzu ni bana jin komai a raina, ko yanzu na mutu hankalina ya kwanta, ABUBAKAR SALAHUDDEEN bakin azzalumin, kune kuke kallonsa kamar mutumin kirki, saboda ya sanya fatar ɓauna ya lulluɓewa duniya laifukan da yake aikatawa, da Abubakar da Farooq wlh ko sun tuba sai sun ɗanɗani azaban Allah, dan kuwa akwai da yawan al'umma da suka mutu ta sanadiyarsu, waƴan nan azzaluman guda biyu, wlh sai Allah......" Bata kai karshen maganar ba A'A ya ɗaga hannu zai zabga mata mari, cak ta riƙe hannunsa tana kare mishi kallo.
"Saboda ina faɗar gaskiya a kan ubanka shi ne zaka mare ni? To kai kanka ka kalli kanka da kanka ka kalli Aliya dake kwance tana barci zaka iya banbanta fuskarka da tata ne? Bari ka ji idan kayi kuskuren marina, wlh, wlh, wlh, sai na kwantowa gabaɗaya juri'arku ruwan da ba zaku iya tsayar da shi ba, wlh sai na bankaɗo dukka laifukan ubanka da ɗan uwansa wa duniya, sai ya zama baku da idanun fita ku kalli jama'a saboda kunya, wasunku ma bakin cikine zai kashe su, idan kuma kace ba haka ba to Bismillah zaka gane shayi ruwa ne wlh, dama na rufe ne dan saboda kada ya kashe mini ƴa ta, na ɓuya ne dan kada ya kalli Aliya ya kasheta, shiyasa ban fito na nunawa duniya ɓarnar da suke yi ba, amma yanzu kabi a hankali!!". WANNAN SHI NE TASHIN HANKALI, BABBAR MAGANA.
Wani irin azababben kululun bakin cikine yasa A'A zubewa kasa tamkar gawa baya numfashi, kansa su Abbi suka yi suna ambatar sunansa, amma ina ko motsawa bai yi ba, ruwa Irfan ya ɗauko mai sanyi a fridge ya zo ya zuba mishi, amma ina ko motsi bai yi ba, daga karshe dai suka kwashe shi zuwa asibiti dan ceto rayuwarsa.
Ita kuma maman Ayla sama ta haura ta nufi ɗaki abinta, dan yau zuciyarta fes, Aunty kam taga tashin hankali yau, Hanan kuwa tun da aka fara hayaniyar ta bar palon, ta koma bedroom nata, dan bata son hayaniya ita ma,. Yanzu babbar abin tambayar a nan shi ne, a ina maman Ayla ta san mahaifin A'A? Menene yasa kuma ya ce ba cikinsa bane? Akwai lauje cikin naɗi, amma muje zuwa, zata warware mana komai ta bamu labarin yadda akayi komai, yanzu dai bari mu leƙa gidan Lion dan ganin wani hali suke ciki, wata kila kafin mu dawo wannan family sun ɗan sami kwanciyar hankali.
Misalin karfe 8 na safe, shirye suke cikin shiga iri ɗaya, sai dai wandon Areef ya fi shiga kalar brown sosai, na Aseef ya yi light, zaune suke a garden da alama dai shirin zuwa wani wajen suka yi, zubawa Aseef dara daran ash eyes nasa ya yi yana kallon yadda fuskarsa take wani kyalli, da alama yana cikin farinciki over, sai aikin latsa waya yake yi.
"Wai Aseef yana ga sai wani fresh kake yi ne? Seriously Naija ta karɓeka kai da Lion, sai wani kyalli face naka take yi, zo ka gaya mini me sirrin ne?". Bai ɗagoba, yana ta faman aikin latsa waya, sai murmushi yake yi Heartbeat ta yi kira. "Kana ji Areef, Heartbeat ce ta yi mini ciki, shiyasa kaga nake wannan kyan". Ya kai karshen maganar tare da miƙewa dan Akila ta ce yazo yanzu. Areef ya gama fahimtar tun da Aseef ya fara soyayya ya dawo mara mutunci, da an yi mishi magana zai shere mutane, ko kuma ya mayar musu da amsar iya shege, yanzu me na wani cewa wai heartbeat ce ta yi mishi ciki daga tambaya? Gaskiya abin da ban haushi.
Yana can yana tunani sai ya ji tashin motar ɗan uwan nasa, alamar da gaske barin gidan zai yi, tafiya zai yi kenan, miƙewa ya yi da sauri ya nufe shi dan tare zasu je su gaida Ammie ya kalli heartbeat ɗin shi ma.
Lokacin da ya isa wajen, Aseef ɗin ya kashe motar ya fito zai nufi cikin gida, "Ina kuma zaka je mu tafi mana?" Ɗan juyowa ya yi yana faɗin "Yauwa Areef zo dan Allah, zo muje ka kallah wani abin". Ba musu ya bi bayansa, kai tsaye ɗakin da Jehan take suka nufa, ita kuma Rimsha, sai zuba barci take yi abinta, shi ma Lion haka, da alama dukkansu a tsananin gajiye suke.
Da sallama ya shigo cikin ɗakin, tana zaune a bakin gado ta farka, tun da Areef ya ɗaura idanunsa a kanta ya ce tabbas gaskiyar Aseef ne, duk yadda aka yi wannan jinin Uncle Hosain ce, akwai alaƙa mai ƙarfi a tsakaninsu, dan kamar ta yi yawa, amma bari su je wajen heartbeat su dawo, tun da Rimsha tana nan zata warware musu komai ai.
Sannu suka yi mata, sai binsu da idanu kawai take yi, tana mamakin me kuma ya kawota gidan Turawa? Ko dai a kasar turai take ne? To yaushe a ka kaita can? Iya saninta a Nigeria take. Ganin taki yin magana ne yasa Areef ya ce "Kila bata magana ne, yanzu dai muje mu dawo, zan gayawa sister ta kula da ita kafin mu dawo sai mu san abin yi". Okey Aseef ya amsa, ya kuma ji matsananci daɗi da Areef ya yarda da cewa tabbas tana da alaƙa da uncle ɗin su, ya yi murna da hakan, juyawa suka yi suka fice daga ɗakin zuwa na Rimsha, ganin sai zuba barci take yi ne yasa Areef ya rubuta massage a wayarta a kan idan ta tashi akwai bakuwa dake ɗakin Imran, ta ɗan taimaka mata kafin su dawo, daga haka suka nufi waje dan su je wajen heartbeat, Lion kuwa tare suka yi sallar asuba da shi, dan haka sun san yana lafiya yana barci, sai ba su shiga ba bare su tashe shi suka wuce.
Sai misalin karfe 9 Rimsha ta farka daga barcin gajiya da take yi, da kyar ta sauko kasa ta nufi toilet dan yin wanka.
A gurguje ta yi wanka tare da shiryawa cikin kananan kaya ta fito da nufin ta duba su Areef dan su ci abinci yunwa take ji, ganin babu kowa a gidan ne yasa ta dawo cikin ɗaki ta ɗauki wayarta dan ta kira Areef ɗin, a nan ne ta ci karo da sakon da ya ajiye mata na bakuwar da suke da ita, fasa kiran nasa ta yi ta ce bari ta fara duba bakuwar tana zuwa, fitowa ta yi ta nufi bedroom ɗin.
Bakinta ɗauke da sallama ta shiga, a sukawane ta sanya hannu tana murje idanunta dan ta tabbatarwa da kanta abin da take kalla gaskiya ce ko ba gaskiya bace, ita ma Jehan ɗin a razane ta miƙe tsaye tana mai murza idanunta dan ta tabbatarwa da kanta ba mafarki take yi ba.
"Jehan". Rimshar ta ambaci sunanta, tare da tafiya da gudu ta rungumeta, ita ma rungumeta sosai ta yi suka shiga kewaye ɗakin suna ruwan hawaye. "Rimsha dama kina raye?" Ta faɗa tana kwallah. "Ina raye Jehan, ina raye, dama kema kina nan Kaduna? Shi ne Sadiq bai gaya mini ba".
"Rimsha bana Kaduna, dogon labarine zan baki daga baya, yanzu dai ina su mummy?" Ta yi maganar tana raba jikinsu. "Ban san in da suke ba, daddy kawai na san in da yake". "What daddy kuma?!!" Ta faɗa tana zaro idanu kamar zasu faɗi kasa, "E Jehan daddy, yana nan, yana raye bai mutu ba". Zata yi magana kenan suka ji jiniyar motocin ƴan'sanda ya karaɗe ko'ina a cikin anguwar, da alama jiga jigan ƴan'sanda ne, da alama kuma suna da yawa, dan motocin nasu manya ne, jiniya ya karaɗe ko'ina tamkar filin yaki suka nufa, kallon juna suka yi, "Zo mu je waje mu gani menene". Cewar Rimshar, da yake Jehan bata da tsoro ko kaɗan a fili, ga karfin hali da dakiya sai ta bita suka nufi waje dan suga menene.
Daga bakin kofar palon kasa suka tsaya suna hangen gate ɗin gidan, amma kafin su fito sai da Jehan ta sanya doguwar rigar Rimsha, dan idan baku manta ba, ba wani kayan arzikine a jikinta ba, daga three quarter sai ƴar vest, shiyasa ta ce ba zata fita a haka ba duk da bata san su waye ne a gidan ba, sai da Rimsha ta ɗauko mata doguwar rigarta ɗaya, ta sanya sannan suka nufo wajen.
Can suka hango gateman yana dirama da ƴan'sandan a kan lallai ba zasu shigo cikin gidan nan ba, su kuma sun kafe sai sun shigo, daga Rimsha har Jehan basu san menene yake gudana ba, garama Jehan bata yi mamakin ganin ƴan'sadan ba.
Waya gateman ɗin ya yi wa Lion da ƴan'sandan suka matsa, a lokacin shi ma ya tashi daga barci, ya fito daga wanka kenan, yana tsaye a gaban mirror ɗaure da towel a kugunsa, umarnin ya bawa gateman ɗin da ya bar ƴan'sandan su kama yarinyar tun da a kan aikinsu suke, shi yasan menene doka, dan sune doka, sune suke tsawatarwa da abi doka, tun da sunce kisan kai ta yi to su kamata, kuma sai ya ji dalilin da