Showing 177001 words to 180000 words out of 359620 words
akan maganar Irfan da Akila suna son junansu, na yi murna sosai, na kuma bawa Irfan aurenta, Friday mai zuwa za'a ɗaura aure, ranar Wednesday gabaɗaya iyalan gidan Deen zasu tattaro su dawo nan dan ayi komai waje guda, sai bayan biki zasu koma, Batula tana zuwa jibi, mantawa nayi ban gaya muku ba, amma an gama shirya komai ai". Tashin sense da ba'a saka mishi date, zube gwiwowinsa a kasa Aseef ya yi, nan take hawaye suka fara wanke mishi fuska cikin sanyin murya ya ce "Please Abba kada ka yi hakan, am very sure heartbeat bata son Irfan, ni ba zan iya rayuwa ba idan ka hana ni ita, please and please ka taimake mu, na san ita ma heartbeat ba zata iya rayuwa da kowa ba sai ni, wlh muna son junanmu over, ni kayi mini duk abin da zaka yi mini amma kada ka hanani auren Heartbeat, ba zan iya jurewa ba, ba kuma zan iya ɗauka ba". Yana magana hawaye wani na bin wani, Ammie bata san lokacin da hawaye ya fara bin kuncinta ba ita ma, dan dole Aseef ya bawa mutun tausayi a yanayin yadda yake magana.
Zubewa kasa ita ma Akilar ta yi, tana kuka tamkar ba gobe, hawaye wani na bin wani "Abba wlh ni bana soyayya da yaya Irfan, ni Heartbeat nake so, dan Allah kada ka aura mini yaya Irfan, Allah bana son shi". Imran sarkin saurin kuka tuni ya fara yi musu hawaye, dan shi yasan menene soyayya, yasan wahalarta, ya kuma ɗanɗana, Akil kuwa tunani yake yi tun da Akila ta buɗe baki ta ce bata son Irfan to gaskiya bai ga dalilin da zaisa a aure mata shi ba, aure ba abin wasa bane, ba abu ne da ake yin shi shekara ɗaya ko biyu ya kare ba, rayuwa ce ta har abada, zama da wadda baka so yafi komai wahala da azaba a duniyar nan, dan haka iyaye ku ji tsoron Allah ku dai'na yiwa yara dole, zama da wanda zuciya bata so babbar barazace ga rayuwar yarinya, ya kan sakata ta yi abubun da kowa zai zo ya yi dana sani daga baya, to maganin bari kada asoma, ku sani dai Allah zai tambayeku.
"Abba dan Allah ka duba wannan magana da kyau". Cewar Imran. "Imran ya kake so na yi to? Deen fa nace maka, bappanku Deen fa!, Shi da kansa ya zo ya nemanwa Irfan aurenta, yana da damar da zai aurawa Irfan ɗin ita ko ban sani ba, ba shi ya ɗaura muku aure ba? Nasan time da ya ɗaura muku ne? Ai ban sani ba, to haka ita ma Akilar zai iya aurar da ita ba tare da sanina ba, kuma bani da abin cewa, amma duk da haka ya wanke kafa ya zo ya nemi auren ta, na kuma ɗauka na bashi, yau saura kwana takwas kenan a ɗaura auren, kenan so kuke nace mishi na fasa bashi wani na waje zan bawa ne ko yaya?". Shiru palon ya yi, ban da shasshekar kuka Heartbeat and Heartbeat babu wani abin da yake tashi, su Imran dai sun rasa bakin magana, sun san ba ta yadda za'ayi Abba ya ce wa Abbi ya fasa bawa Irfan wani daga waje zai bamawa, hakan sam ba abune mai yiwuwa ba.
Suna tsaka da tunani basu ankara ba sai ganin Aseef suka yi ya sulale kasa sumamme, ihu Akila ta kurma ta yi kansa tana ambatar sunansa Heartbeat!! Heartbeat, kamata Akil ya yi ya rungumeta a jikinsa tare da bubbuga bayanta dan ta samu ta natsu.
Da gudu Umaisha ta fito daga cikin kitchen dan ta zo taga me yake faruwa ake ihu haka, Abba, Imran a zafafe suka yi kansa, sai kiran sunansa Aseef, Aseef Imran yake yi, amma ina shiru, ruwa Ammie ta ɗauko a fridge Abba ya karɓa ya tarbo a hannu ya shafa mishi a fuska, shi kuma Akil sama ya wuce da Akila dan kada ta karawa Aseef ɗin zafi a kan zafi, ga ciwo ga kuma kukanta, wucewa Abba ya yi yana faɗin "Ana jiransa a office tun ɗazun, bari ya je". Okey suka amsa mishi da shi, sauri yake yi sosai, kuma baya son tsayawa ne, dan baya son ganin halin da Aseef da Akila suke ciki, saboda yasan duk wuya duk daɗi ba zai canza magana ba, ba zai iya hana Irfan ya ɗauki Akila ya bawa wani bare ba, amma fa har can kasar zuciyarsa shi ma yana son bawa ƴar tasa zaɓinta, amma ba dama ne kawai, bashi da yadda zai yi, jini ba karya ba.
Sai rarrashinsa Imran yake yi, amma ina yaki yin shiru, sai ruwan hawaye yake yi bawan Allah, ba zai iya jure rashin Akila ba, ita ɗin ta zame masa wani ɓari na rayuwarsa, ita ce first love ɗinsa,. Sai da Imran ya ce ya yi mishi alkawarin zai shawo mishi kan Abba, duk wuya In Sha Allah Akila matarsa ce, sannan ne ya ɗan hakura ya dai'na ruwan hawaye, ita ma Ammie karfafa mishi gwiwa ta yi a kan kada ya damu, da izinin Allah Akila tasa ce, tun da har ta furta bata son Irfan to kada ya damu zasu shawo kan Abba idan ya dawo, da haka dai suka samu suka lallaɓa shi ya daure ya hakura ɗin.
Imran ya ce su je ya tuka shi zuwa gida, okey ya amsa tare da cewa Imran ɗin dan Allah kada ya gayawa su Areef, idan ya gaya musu yasan Lion zai ce sai dai ya rabu da Heartbeat ɗin tun da haka ne abin, to dan haka kada ya gaya musu, okey ya amsa mishi da shi, da haka ya yi wa Ammie sallama sai hakuri take bashi suka nufi gida.
Yana komawa bedroom nasa ya wuce ya haye gado saboda tsananin ciwo da kansa yake yi mishi, bai kula kowa ba yau a gidan, yana kwanciya ba jimawa barci ta yi awon gaba da shi, sai sauke ajiyar zuciya yake yi cikin barci, shi kuma Areef yana can yana faman bincike a kan case ɗin Jehan.
Da misalin karfe 8:30 na dare, bayan sun gama cin abinci, da kyar Rimsha ta ci abinci, nan ma har sai da Areef ya ɓata rai sannan ta yarda ta ci, shi ma dai Aseef ba wani abincin kirki ya ci ba, dan ma dai Imran ya sake kiransa a waya ya kara kwantar mishi da hankali ne yasa ya yarda ya ci abincin, da kuma baya son su Lion su gane yana cikin damuwa, dan Lion ba zai goyi bayansa ba, zai ce akan mace har zai ɗaga hankalinsa, shi bai san so ba, ganin abin banza yake yi mata.
Wanka ta yi ta shirya cikin wani wando da bai karisa kai mata idon sahu na kafarta ba, sai riga mai karamar hannu mai shegen kyau, ɗaura handkerchief ta yi a kanta, ta yi kyau ba karya, sai dai fa kallo ɗaya zaka yi mata kasan tana cikin matsananciyar damuwa, plat shoe ta sanya a kafarta tare da nufar waje, ban da tunanin jenan babu wani abu da take yi, garden ta nufa dan ta rage wa kanta raɗaɗin abin da take ji, gabaɗaya blue light ne kunne a garden ɗin, saman sofa ta kwanta tana tunane tunane har barci ya yi awon gaba da ita, sai misalin karfe 11 na dare da sanyin ya ratsata ne ta farka, a hankali ta waro dara daran sleeping eyes nata, ganin a cikin garden take yasa ta miƙe a tsorace, bata lura da akwai mutun a cikin garden ɗin ba kawai ta nufi cikin gida, sai dai kash Mark ya rufe gabaɗaya kofofin gidan, ga shi bata fito da wayarta ba bare ta kira Areef, ga kofar ko ta yi knocking ba lallai su ji ba, kuma ma tana tsoron yin knocking ɗin dan kada Lion ya tashi daga barci.
Ta jima tsaye a wajen tana tunanin mafita, can ta ɗan ji motsin su Brady, dake ɗaure a kusa da ta wajen pool, a guje ta juya ta koma garden ɗin, saman sofar da ta tashi nan ta koma ta kwanta tare da takure jikinta waje guda, ga sanyi ga kuma tsoro, sai ta takure sosai, ta datse idanunta gam tamkar zata fasa su, jikinta har wani kerma yake yi, duk abin da take yi yana kallonta, dama idan baku manta ba, wajen zamansa kenan da daddare, wani lokaci sai ya kai karfe 2 na dare a wajen, so yanzu ma yana zaune yana aikin latsa waya, da ya gaji sai ya kishingiɗa a saman doguwar sofa dake kusa da shi, sai dai tsawonsa ta fi ta sofar, dan haka sai ya ɗan naɗe kafa, duk wani motsinta yana gani, amma ita bata san da shi a cikin garden ɗin ba, da haka barci ɓarawo ya sake ɗaukarta, ta takure jikinta over.
Can cikin dare misalin karfe 1 sanyi ya sauƙo sosai, sai dai ita kuma ɗumi take ji yana ratsata ba sanyi ba, wani irin daɗin barci take ji abinta, miƙa ta yi da nufin bari ta juya daga yanayin kwanciyar da take, sai ta ji wuyarta na ɗan yi mata zafi, waro idanunta waje ta yi, idanun nata ɗauke suke sosai da barci, still dai a cikin garden ɗin take, yunkurawa ta yi zata miƙe sai ta ji kamar ba jikin sofa ta dafa ba mutun ta dafa, da yake akwai hasken blue light a wajen sai ta kai kallonta in da ta dafa kafin ta ɗago kanta izuwa kansa, yana zaune ya jingina kansa da jikin headboard na sofar, da alama shi ma barci ne ta yi awon gaba da shi. Abin da ya faru, da misalin karfe 12 na dare, sai rawan sanyi take yi, hakwaranta na garuwa da na juna sosai, kasa jure jin sautin hakwaran nata ya yi, suna toshe mishi kunne, hakan yasa ya miƙe tare da dawowa saman sofar da take kwance, sofar ta yi musu kaɗan, dan haka sai ya ɗaga kanta ya ɗaura saman cinyarsa bayan ya zauna kenan, sannan ya cire jacket dake jikinsa ya rufa mata, da yake jacket ɗin nasa yana da girma sai ta rufe ta da kyau, ga kuma kauri jacket ɗin, cigaba da latsa wayarsa ya yi har barci ta yi awon gaba da shi shi ma, to shi ne abin da ya faru, ya yi mata hakan ne kuma a cewarsa yanzu tausayi take bashi saboda irin wahalar rayuwa da ta sha, idan baku manta ba a Abuja ya faɗa, ita ce mutun ta farko da ta fara mashi tausayi a rayuwarsa.
(To mudai je zuwa daga tausayi se me readers?)
Ganin shi ne ba karamin ruwan mamaki ta sha ba, tunani ta fara yi a kan yaushe ya zo garden ɗin kuma? Bata san tun karfe 9 yana wajen ba, kai kallonta saman jacket nasa dake rufe da jikinta ta yi, ba ƙaramin daɗi ta ji ba, da yake zuciya bata da kashi, sai ta ce yaya Saif yana da kirki, har ta manta abubuwan da suka faru a baya, zuba mishi idanu ta yi tana kallon yadda yake barci cikin kwanciyar hankali, Allah ya yi halitta, kyau iya kyau, tsabar rashin ji irin nata sai ta kai hannu ta shafi kumatunsa, kada ku manta bashi da nauyin barci, tun motsinta na farko da ta yi lokacin da ta yi miƙa tana son juyawa kafin ta farka kenan, to motsin nata ya farkar da shi, sai dai da yake barcin yana kan shi sosai ne sai bai buɗe idanu ba, ya cigaba da lumshe su dan kada barcin ya watse mishi.
Daga ita har shi sai da suka ji wani irin yarrrrr a jikinsu lokacin da ta shafa lallausa kuma kyakkyawar kumatunsa, sai dai ko motsawa bai yi ba, hannunta na kerma saboda rashin ji sai da ta sake kai hannu saman dark black curly hair, shafawa ta yi a hankali har zuwa sajensa, a hankali ta gangaro da hannunta zuwa saman lallausan laɓɓansa, tana ɗaura hannun nata a lips ɗin nasa caraf ya cafke hannun nata ba tare da ya buɗe idanu ba, ba ƙaramin razana ta yi ba, a zafafe ta yi yunkurin sauƙa daga saman sofar ta gudu.
(to ki gudu ki je ina? Ba kin iya neman bala'i ba? Baki jin magana ai sai ki tsaya ayi wace za'ayi)
Riƙe hannun nata da kyau ya yi tare da sauko da kansa sai tin face nata, a hankali ya waro dara daran blue eyes nasa masu ɗauke da barci a saman razananniyar face ɗin tata, datse idanunta ta yi tana addu'ar Allah yasa kada ya ce zai dake ta, Allah yasa ya yafe mata, wai mema ya kai ta ne? Wani ɓangare na zuciyarta ne ya ce mata kyau mana, kyansa ya kai ki taɓa shi,.
"Open your eyes". Ya faɗa a sanyaye, ya yi maganar can kasar maƙoshinsa, da ni da ku dukka mun san idanun nata yake son kallo, suna matukar burgesa, izza ta hana shi ya nuna sun burge shi, dama duk wanda ya kalli sleeping eyes nata dole su burge shi, ga su dara daran farare tas kamar audiga, dole su ɗauki hankali dan idanun duniya ne, bare ma idan ta tsorata ta zarosu ai ba'a magana, zata sanya samari da ƴan mata faɗawa cikin kwata, dole idan ta tsorata ta burge mutun, ko dan kara zarosu da take yi.
Tsuke ɗan bakin nan nata ta yi tare da waro idanun nata a hankali, kai tsaye sai cikin nasa idon, ita tana bala'in son na shi idon, shi ma yana son nata, ɗan kawar da kallonta ta yi daga cikin kwayar idanun nasa zuwa saman lips nasa da suke red color sosai.............
❤️❤️TRIPLETS❤️❤️
E47-48💋
Tsuke ɗan bakin nan nata ta yi tare da waro idanun nata a hankali, kai tsaye sai cikin nasa idon, ita tana bala'in son na shi idon, shi ma yana son nata, ɗan kawar da kallonta ta yi daga cikin kwayar idanun nasa zuwa saman lips nasa da suke red color sosai, ita dai a duniya wannan lallausa kuma kyakkyawan lips ɗin nasa suna bala'in burgeta, ji take yi kamar ta sa hannu ta taɓa, shi kuma ya zubawa idanunta kallo babu ko kyaftawa, kamar mai nazarin wani abin a tattare da ita.
Slowly ya dawo da kallonsa saman beautiful lips nata sa suke pink color, ga shi ta tsuke ɗan bakin nata alamar a tsorace take, "Me haɗinki da face na?" Ya faɗa can kasan maƙoshinsa, girgiza mishi kai ta fara yi tana faɗin "Babu komai". Wani irin yanayi ya ji yadda ta motsa lips ɗin nata, shi bai san menene soyayya ba, bayan kaunar TRIPLETS nasa bai san wani so ko kauna or tausayin wani ba, ita ce ta farko da ya fara tausayawa bayan TRIPLETS nasa, wannan yanayin da yake ji a jikinsa idan tana kusa da shi, yana danganta hakan da tausayin da take bashi, idan baku manta ba shi a budurwar Areef ma yake ɗaukarta, dan ba karya ya san ɗan uwan nasa yana sonta, sai dai fa ganin abin ma a hauka yake yi, yana ganin Areef bai san me yake yi ba da zai ce yana son ƴar yarinyar nan da bata wuce a goya ba, to me abin so a wajen?.
(A lallau Lion ya yi mugun raina Rimsha, wai bai san cewa Rimsha tsab za'a iya yi mata aure kuma ta zauna bane? Ya je Gombe ya ga ikon Allah, gombawa ayi hakuri gaskiya ce🤪)
Sake hannun nata da ya riƙe ya yi tare da mayar da kansa jikin headboard na sofar ya lumshe idanunsa, barci yake ji sosai, jikinsa duk a mace, ya kasa miƙewa ya shige ciki, idan kuma bai shiga ba, ita ma ba ta haryar da zata shiga. Saboda tsiya irin tata da kuma tsoron wajen da take ji, sai ta mayar da kanta a hankali saman cinyar tasa ta kwanta tare da kara jawo jacket ɗin nasa ta rufe jikinta da kyau tana shakar daddaɗar kamshin perfume nasa, wani irin farinciki na wuce misali ta tsinci kanta a ciki, sai sakin murmushi take yi abinta, yau gata a cinyar abin kaunarta, kai abin ba'a magana, idan baku manta ba, ranar da ta kwana a saman kirjinsa a Abuja bata cikin hayyacinta, tana tsorace sosai, so bata sani ba, yau kuma tana cikin hayyacinta.
A can cikin gida kuwa, mu koma baya kaɗan, lokacin da suka gama cin abinci, Areef ya ɗauki laptop ɗin Aseef ya kule cikin bedroom nasa yana bincike da ƴan dube dubensa na wasu bayanai da ya kwaso a kan Family'n Nawazudden ɗin daga laptop na Lion, shi kuma Aseef bedroom nasa ya koma.
Bayan ya haye saman gado, gabaɗaya bawan Allah ya rasa me yake yi mishi daɗi, duniya har wani juya mishi take yi, wayarsa ya jawo tare da fara kiran number heartbeat, dan ita ce kaɗai zata sanya shi farinciki a rayuwarsa ta yanzu, bugu ɗaya ta ɗauka, baiwar Allah ta ci kuka har ta godewa Allah.
Tana ɗauka wani kukan ta saka mishi, dafe kansa dake yi masa barazanar tarwatsewa ya yi, murya a dashe can ƙasa ƙasa ya fara magana "My heartbeat please and please ki yi shiru, idan ba haka ba, kina iya jefani cikin damuwar da zata iya yin sanadiyar rayuwata, ni kukanki ya fi zama mini bala'i a kan hanani ke da akayi, please ki daina kin ji? Kada ki ɗauka daɗin baki ne nake yi miki, duk abin da zai fito daga cikin bakina ki sani tsantsar gaskiya ce wadda babu mix ko ɗigo, na san idan ban same ki ba, mutuwa zan yi, yanzu dai ki yi shiru kin ji ko?".
Tsabar kukar da ta sha, voice nata sam baya fita sosai, da kyar ta ce mishi, "Wlh Heartbeat kukan ne yaki tsayawa, idan har na ce zan tsayar da shi sai yaki, hawayena sun ki dai'na zuba, kai'na ciwo yake yi mini sosai, komai ya tsaya mini cak, duniya gabaɗaya juya mini take yi". Miƙewa zaune ya yi tare da nufar wajen da ya ajiye key ɗin motarsa yana faɗin "To shikenan, yanzu dai kinci abinci ne?" Girgiza mishi kai ta yi tamkar tana a gabansa, "Baki