Showing 207001 words to 210000 words out of 359620 words

Chapter 70 - Triplets Book 3 Hausa Novel Complete

10 Dec 2024

3070

sanya mata a kan nata yana faɗin "Bana son ki rinƙa sake gashin nan naki haka, nafi son ki rinƙa ɗaure mini shi kina ɓoye mini shi, kada ki bari kowa ya kalla mini abina, nawa ne ni kaɗai".

Mamaki ne ya kamata ganin yadda gashin nasa ya zubo mishi har kafaɗarsa kamar wata mace, dama bata san gashinsa yana da tsawo har haka ba, dan baya barinsa a sake, kullum a tare a bayan wuya ya sanya mata ɗan karamin pil ya ɗaure, ba zaka taɓa tunanin yana da tsawon gashi har haka ba, ya fi Lion tsawon gashi sosai, dan shi Lion yana rage tsawon nasa, baya bari ta wuce mishi bayan wuya, shi kuma Areef ɗin baya ragewa, ya bar kayansa ta kai har baya abinsa, yana kashe mata kuɗi over yana gyarata, kuɗin shampoos na gyaran gashinsa kawai ta isa ta sayawa mutum dankareren gida, ba karamin kuɗi suke kashewa gashin nasu ba, kowa da ra'ayinsa a cikinsu, shi Aseef ma ai dukka yake tankewa abinsa, baya son wahala, Lion rage tsawon, shi kuma har baya ya bar abinsa.

Zubawa gashin nasa idanu ta yi tana mamaki, ya fi nata tsawo. Bayan ya ɗaure mata nata ne ya tara nasan ya kulle a bayan wuyar nasa, duk da ya san zata warware, bai wani damu ba tun da ya ɗaure mata nata, gashin TRIPLETS akwai bala'in tsantsi ne sosai, hakan yasa dole idan zai ɗaure gashin nasa sai ya sanya pil, idan ba haka ba, warwarewa zata yi.

Hira ya ɗan yi mata na ƴan mintoci da basu wuce 10 ba, sannan ya yi mata sallama tare da rankwafowa ya manna mata sumbata a goshinta yana faɗin "Ki kula mana da kanki, ina son uncle ya zo ya sameki cikin ƙoshin lafiya, dan haka ki kula". Kallon uku goma ta watsa mishi, ko a jikinsa ya nufi waje abinsa yana yi mata bye bye.

Yana fita ba'afi da minti uku ba sai ga gandurobobin suka dawo ciki, macen da ta fito da ita, ita ta mayar da ita tare da ɗaukar ledar da ya bata, sai da suka je bakin kofar ɗakin nasu, sannan suka cire mata sarkar da suka ɗaure ta tare da karɓar ledar da Areef ɗin ya bata dan su zuba me a ciki, always ne da pants a ciki, sake baki ta yi tana kallon always ɗin da matar ta fitar, ko waye ya gaya mishi yau period nata ya zo da safe? Kai wato ma ya saka mata ido na wuce misali kenan? Ta tsaya sai tunane tunane take yi, sai magana gandurobar take yi mata a kan ta shiga ciki, amma ina ta lula duniyar tunani waye ya gaya mishi yau tana period kuma?.

Sai da gandurobar ta taɓata sannan ne ta dawo daga duniyar tunanin nata, Nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta karɓi kedar ta wuce ciki, rufesu matar ta yi tare da juyawa ta bar wajen.

Shi kuma Areef yana barin prison ɗin gidansu Imran ya nufa dan ya riga da ya gaya wa Imran ɗin yana zuwa yau.

Gidan cike yake da ƴan biki, part ɗin Imran ɗin suka wuce, Akila tana ciki tana kwance bata da lafiya, zazzaɓi kamar zai kasheta, har Abbi ya ce ko za'a ɗaga bikin ne, Abba ya ce a'a ayi kawai ta je ta yi jinyar a gidanta, da yake shi ya san me matsalar, Ammie dai raba dare take yi tana rokan Allah da ya kawowa ƴar tata mafita, ya zaɓa mata abin da ya fi zama mata alkhari, bata wani nuna damuwa ba.

Lokacin da Areef ya shiga cikin palon, Imran, daddyn Jelly, AKil, Irfan, Dr Nawid, duk suna zaune saman sofa suna zuba hira, da yake yana sanye da black glass sai Akil bai iya rabe shi da Aseef ba, ya ɗauka ma Aseef ne, dan haka sai ya ɗan kawar da kansa, dan sam baya son haɗa idanu da Aseef, ya kasa manta zubewa a kasa a gabansa da Aseef ya yi kwana uku da suka wuce, lokacin su Abbi ba su dawo gidan ba, ya zo wajen Akila hira ne, har cikin palo ya shiga dan Abba baya nan, Akil ɗin ya fito zai fita zai je unguwa, shi ne ya zube gwiwowinsa a gabansa yana rokonsa da dan Allah ya rokan mishi Abba, wlh ba zai iya rabuwa da Akila ba, idan aka rabasu zai iya mutuwa, wannan abin ya tsayawa Akil sosai a rai, yadda ya kalli fuskar Aseef a wannan rana, ban da tsantsar soyayyar Akila babu wani abin da yake cikin idanunsa, bawan Allah.

Lallai rayuwa ba ta yadda bata zuwa wa bawa, yau a kan mace, a kan soyayya har ɗaya daga cikin TRIPLETS jinin William jacop, TRIPLETS ga The General Of Armys yake zube gwiwowinsa a kasa yana rokan kada a raba shi da ita? Ya ilahi ya lillahi, duk wata zuciya mai imani sai ta zubarwa da Aseef kwallah na halin da yake ciki, tabbas yana cikin halin mutuwa ko rayuwa, domin kuwa ya yi mummunar zurmawa over ne a soyayyar AKila.

Da yake shi Areef bai san komai ba, sai ya miƙa musu hannu dan su yi musabaha fuska ɗauke da murmushi, sosai Akil ya sha mamaki, sai kallonsa yake yi, ya kuma kasa gane cewa ba Aseef bane Areef ne, kila da ya cire glass ɗin face nasa ne ya iya gane shi ta kalar kwayar idanunsa.

Haka suka cigaba da hira Areef yana ta kallonsu dan baya jin Hausa, bai san me suke cewa ba. A nan ya yi sallar mangariba da issha sannan ya yi musu sallama ya nufi prison dan ya sake duba Jehan su yi sallama sai gobe, yana fita sai da Akil ya tambayi Imran ya akayi Aseef ya hakura ya wastsake? Nan yake gaya mishi wannan ba Aseef bane, Areef ne, ya sha mamaki irin tsantsar kamar da suka yi mishi har ya kasa raɓesu, shi kuma Dr Nawid ya sha mamakin dama wannan TRIPLETS na Lion ne, su Lion kawai suka sani, shi ma ba face nasa suka sani ba, bai taɓa ganinsu a zahiri ba sai yau, ga shi har musabaha suka yi ba tare da ya san shi ba ne.

A ɓangaren Lion kuwa, bayan ya yi sallar mangariba da issha bedroom nasa ya wuce dan yunwa yake ji sosai, zaune ya iskota ta kawo mishi abinci tana jiransa.

Wajen da ya saba zama ya je ya zauna tare da bata umarnin ta zuba mishi abinci, ba musu ta zuba mishi ta turo mishi a gabansa, ɗaukar spoon ya yi ya fara ci, shiru ta yi tana tunanin ƴar uwar tata, kamar saukar aradu haka ta ji zazzakar muryarsa ya daki dodan kunnenta. "What is wrong with you?". Shi ne abin da ya faɗa cikin sanyin murya.

Girgiza mishi kai ta yi tana faɗin "Nothing". "Saboda na hanaki zuwa prison ko?" Nan ma girgiza mishi kai ta yi alamar a'a, ga idanunta kuma har sun kumbura saboda kuka, dole dama zai gane tana cikin damuwa ta kuma yi kuka sosai, saboda idanun nata, kuma kunsan yadda yake tsantsar kaunar ganin idanun nan nata, dole dama zai ɗago ya kallesu, idan ya gansu a kumbure kuma ai dole ya tambaya.

Shiru ya yi bai sake yin magana ba har ya kammala cin abincinsa ya tashi ya fita daga gidan, waje gabaɗaya ya nufa, a waje Mark ya fito da mota ya same shi, akwai in da za su je ne.

Kwashe kayan abincin ta yi ta mayar kitchen kafin ta koma bedroom nata ta ɗan kwanta, da misalin karfe 10, Lion bai dawo ba haka shi ma Areef, Aseef kuma har lokacin yana ta barci alluran bata sake shi ba. Sam ta kasa barci, ban da tunanin Jehan ba wani abin da take yi, a haka har 11 gari ya yi shiru, kasa jurewa ta yi ta diro kasa daga saman bed ɗin nata, mayafin abayar tata ta ɗauka ta yafa a kanta tare da nufar waje, gabaɗaya sojojin sai kewaye suke yi a cikin harabar gidan dan tabbatar da tsaro, wucesu ta yi ta nufi gate, kwata kwata ta manta Lion ya ce kada ta kuskura ta fita, idanunta sun rufe, ban da tunanin Jehan babu wani abin da take yi.

Hanata fita gateman ya yi, karya ta zuba mishi a in da ta ce mishi Areef ne yake kiranta yana waje, da yake ta san Areef ɗin baya nan. Jin hakan yasa ya buɗe mata gate ɗin ta fita, tafiya ta fara yi bata san ina ta dosa ba, ita dai prison kawai take son zuwa abinta.

Har ta fita daga layin nasu ba tare da ta sani ba, sai a lokacin ne kuma ta tuna ashe bata san hanyar zuwa prison ɗin ba ma, ga shi babu abin hawa, bugu da kari babu kuɗi a hannunta. Daurewa ta yi ta cigaba da tafiya abinta, ta ɗan kara tafiya can ta ci karo da irin matasan nan ƴan shaye shaye, wuka suka zare mata a kan ta basu kuɗin jikinta, dan a tunaninsu irin karuwan nan ne ita.

Kuka ta fara yi jikinta na kerma, ga shi ba abin da ta fito da shi, ko wayarta bata ɗauko ba bare ta basu su rabu da ita, cikin kuka ta ce musu ita bata da kuɗi, ɗaya daga cikinsu ya ce ta yi shiru ta dai'na yi musu kuka ko su kasheta, a yadda take kyakkyawan nan ne zata ce musu bata da kuɗi? Kenan a banza mazan suke kwasanta ne? Duk wannan kyau ɗin nata su kwasa ba biya? Ina karya take yi, ta basu kuɗi ko kuma su kasheta,. Rantse musu da Allah ya rinƙa yi a kan wlh ita bata da kuɗi, jikinta sai kerma yake yi, tana kuka kamar ranta zai fita tare da danasanin fitowarta.

Wuƙa ɗaya daga cikinsu ya fitar dan ya caka mata a ciki tun da taki basu kuɗi, cikin sauri wani daga cikin ya dakatar da shi yana faɗin "Kai wawa ne fa, ba gara muma mu ɗan kwasa na banzan ba tun da ba kuɗi, ka ga karamar yarinya ne, wato wayo mazan suke yi mata su kwashi daɗi basu biyanta, daga ganin wannan yarinyar irin yaran nan ne da uwarsu ta mutu suke hannun matar uba haka, shi ne yasa take fitowa bin maza, idan ba haka ba, ba yadda za'ayi uwarta tana raye ka ganta a yawon ta zubar a cikin daren nan, ka ganta kyakkyawa dan haka muma mu kwashi rabonmu tun da ba kuɗi". Amsa mishi suka yi da e haka ne ya kawo shawara mai kyau gaskiya.

Jin hakan yasa ta yi ƙoƙarin guduwa ta kuma yi musu ihu, damko mayafin abayarta kanta suka yi, da sauri ta cire musu mayafin ta fara gudu dan ta tsira, ina ai tana mace ba zata iya guje musu ba, tuni suka damko gashin kanta, janta suka fara yi da gashin dan tsabar mugunta, ɗaya daga cikinsu ya toshe mata baki, cikin ma gudanar ruwa dake gefe da gefen titi wato lambatu suka yi ƙoƙarin shigar da ita, da yake babu ruwa a ciki, duk ruwan saman da aka yi ya ganganre ya tafi, wajen har ma ya bushe, ga shi ya yi fresh saboda ruwa ya wanke shi.

Yana riƙe da gashin kanta gam, da shi yake janta yana ƙoƙarin shigar da ita ciki, ya toshe mata baki, ita kuma ta yi yarda ta shiga, haushi hakan yasa wanda ya ciro wuka ɗazun ya sake cirowa dan ya yanke mata wani sashe na daga jikinta ko kuma ya caka mata a ciki ta yadda zata zube kasa su shugar da ita, koma ta mutu su za su iya biyan buƙatarsu, cike da mugunta ya yi yunkurin caka mata wukar a cinya, cap Lion ya damki hannunsa, wani irin baya ya yi da hannun ya murɗe da karfi ji kake kas ya karya kashi, ihun azaba ya saki.

Saketa wanda ya riƙeta ɗin ya yi suka yi ƙoƙarin guduwa, kap nasu Mark ya damkosu, da yake sun ɗan yi shaye shayensu babu wani kuzarin kirfi a tattare da su, kwallo da su sosai Mark ya yi kafin ya haɗesu ya cire wandon ɗaya daga cikinsu ya yage shi ya ɗauresu da kyau kamar wasu goro.

Abin da ya faru, lokacin da yaran suka tareta, a lokacin motar Lion ta wuce su, sai dai bai kawo cewa ita ɗin ba ce, ya dai ga mace da maza suna tsaye, a tunaninsa ma duk tare suke, hira suke yi da yake ta bawa hanyar baya, sai dai fa da kallo ɗaya ya yi wa bayan nata ya ji cewa ita ce a zuciyarsa, sanin ita tana gida ba zata taɓa fitowa bane yasa ya kawar da tunanin a ransa suka wuce, bayan ya koma gida ya buƙaci shan fruits, ya kira Areef a waya dan ya sanyata ta kawo mishi tun da shi bashi da numberta, sau uku Areef yana kiran numberta bata ɗauka ba, shi ne ya sake kiran Lion ɗin ya ce dan Allah ya dubata a ɗakinta ko lafiya bata ɗaukar waya, da farko ya share ya kwanta, sai kuma ya tuna da yarinyar da ya gani tsaye cikin mazan nan tabbas bayanta ya yi maka da nata.

Tuna hakan yasa ya fito ya shiga bedroom ɗin nata, bata nan, palo ya fito zuwa waje ya tambayi gateman, a nan ne yake gaya mishi ai ta fita, wani mahaukacin mari ya sakarwa gateman ɗin wanda ya sanya shi sumewa, tsawa ya dakawa sojijin dake wajen a kan hauka suke yi ne da zasu bar wani ya fita daga cikin gidan nan ba tare da saninsa ba, kasa suka yi da kansu suna tsoron ce mishi yarinyar ta ce Areef ne ya kirata, in da ya harzukannan zai iya yanke musu mummunar hukunci, dan haka sai suka ja bakinsu suka yi shiru.

Tuna cewa tana tare da mazan can yasa bai bi ta kansu ba ya ce Mark ya fito da mota suje, to shi ne abin da ya faru a gida da har ya iya sanin in da take ha zo.

RIMSHA

Suna sakinta ta zube gwiwowinta a kasa a wajen, kuka ta saka dan tasan yau ta mutu a hannunsa, daga yanayin tsayuwar da ya yi ma tun bata kai kallonta ga face nasa ba tasan babu mai kwatarta yau, a zafafe rai a matukar ɓace sai huci yake yi ya damko wuyarta, jan ta ya yi har zuwa wajen mota, a gidan baya ya wurgata kafin ya shiga mazaunin driver, ya ja motar ya bar Mark ɗin a wajen, shi yasan ta yadda zai yi ya dawo gida tare da tantiran yaran da ya kama.

A guje ya figi motar tun bai karisa wajen gate ba yake danna musu uban horn, a zafafe sojojin nasa har suna rige rigen buɗe mishi gate ɗin gidan, da wani irin mahaukacin gudu ya danna hancin motar, sai huci yake kamar wani zaki, yau Rimsha ta kure shi, har zai ce kada ta fita kuma ta saka kafa ta fita, kenan tafi karfin shi ya yi mata magana, ta raina shi kenan, dole yau ya kashe yarinyar nan a cewarsa, dan babu wanda ya taɓa yi mishi abin da ta yi mishi.

Dani da ku duk mun san azababben bala'in kishi ne na waƴan can matasan sun taɓata, shi ne yake damunsa, ba wani dan ya ce kada ta fita ta fita, shi ne dai yake ganin ai raina shi ta yi, ya ce kada ta fita ta fita, mu kuma mun san kishin bala'i ne irin nasa.

Tun bai kashe motar ba ta fito a guje ta nufi cikin gida, dan tasan yau tashiga ɗari ba uku ba. Kai tsaye bedroom nata ta nufa, banko kofar ta yi tare da murza key ta je ta haye gado tana kuka tare da danasanin abin da ta yi, shi ma dai bai kashe motar ba ya fito a zafafe, cikin zafin nama yake taku ya bi bayanta, wani soja ne ya zo ya kashe mishi motar.

Kai tsaye bedroom ɗin nata ya nufa, jin kofar a rufe yasa ya yi baya ya take kofar da karfi, wani irin jijjiga ta yi bata buɗe ba, sake yin baya ya yi ya take ta da karfi sai ga kofar a kasa ta ruguzo, ihu ta kurma tare da miƙewa, ta rasa ina zata sanya ranta, ga kofar toilet nata already ya ɓalle mata shi ranar, wajen ɓuya dai ya kare, yau tashi ga ukunta.

Ihu take yi kamar mahaukaciya, a zafafe cikin takun jarumta ya shigo cikin ɗakin, gudu ta fara yi tana ƙokarin neman ina zata ɓuya, Aseef yana can yana barci ya sha allura bai san me yake faruwa ba, bawan Allah duk tsoronsa da allura yau da kansa ya ce ayi mishi, daga nan zaka san bala'in ta kai mishi bala'i.

Dai'dai lokacin motar Areef ya danno kai cikin gidan, damkota shi kuma Lion ɗin ya yi, ya jata har zuwa bedroom nasa, a tsakiyar ɗakin ya yi wurgi da ita, belt na wandonsa ya fara cirewa, dan wlh yau sai ya yi mata azababben dukar mutuwa, idan ta yi sa'a ta rayu to, idan kuma ta mutu ita ta ji yo a cewarsa, har lokacin ihu take yi ta kasa magana.

Jin ihunta yasa Areef ya karisa haurowa benen da sauri, dama yana haurowa zai zo wajen Lion ɗin ne. Yana shigo ya ga abin da yake faruwa, kai tsaye ɗan uwan nasa ya nufa yana tambayarsa me yake faruwa? Me ta yi mishi? Ko kallon in da yake bai yi ba ya zaro belt nasa tare da nufarta gadan gadan, da sauri Areef ɗin ya tare gabansa yana faɗin.

"Sister ki gudu, Lion dan girman Allah kada ka ce zata taɓa lafiyar Rimsha yanzu, wlh zaka iya kasheta har lahira, dan girman Allah ka yafe mata sai zuwa da safe ka yi mata hukunci duk da ma ban san me ta yi maka ba". Ko kallon in da Areef ɗin yake bai yi ba, yau idan bai ga Rimsha ta dai'na numfashi ba, wlh ba zai taɓa jin sanyi a ransa ba, da duka zai kasheta, tun da ita bata jin magana, dan kawai sun yi tafiya ya ɗan sake


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login