Showing 204001 words to 207000 words out of 359620 words

Chapter 69 - Triplets Book 3 Hausa Novel Complete

10 Dec 2024

2042

ɗaukar wani ba kuma, kada ya mutu lokacin mutuwarsa bata yi ba.

Tsareta da idanu ya yi yana jiran amsa, a hankali ta motsa kyawawan laɓɓanta ta furta "Ka ce na fita, yanzu zan fita ɗin". Ganin yadda lips nata suke motsi dimples nata suke lotsawa ne yasa ya tuna abin da ya faru ɗazun na iska da ya hura mata cikin ɗan bakin nata, wani irin zirr ya ji a jikinsa tuna abin, sakinta ya yi ba tare da ya yi magana ba, da gudu ta juya ta fita, dama Malika ta faɗa, dole sai abin ya yi ta dawowa mishi cikin tunaninsa, dan abu ne da bai taɓa yi ba a rayuwarsa, so dole ya ji wani iri, dama mace da namiji kamar kararrawa suke, duk lokacin da suka haɗu dole sai zuciya ta bada sautin bugawar kararrawa, haka halittar take, musamman kuma yadda ya ji lips ɗin nata da bala'in laushi kamar me, ai dole ya tsaya mishi a rai.

(Gaskiya Malika bata kyauta mishi ba, Allah ya sakawa bawan Allah, yana zaman zamansa muguwa ta ɗarsa mishi abin da bai taɓa ji ba a zuciyarsa😭 justice for Lion, ta iya shirya kitimurmura Malikar nan wlh, duk wani tsiya ta san shi, yanzu sai Allah ma kaɗai yasan me ta yi ta shiryawa da har aka kawo wannan matakin😌)

Hanyar fita ya nufa, har ya yi gaba sai kuma ya juyo da kallonsa kan Aseef dake kwance ya basu baya, calmly ya ce "A karo na karshe zan tanbaye ka, me yake damunka?" Juyawa Areef ya yi ga Aseef ɗin, yayin da shi ma ya juyo ga ƴan uwan nasa, kasa kasa ya furta "Zazzaɓi and ciwon kai". Ɗan zaro idanu Areef ɗin ya yi tare da kai hannunsa saman lallausan kumatunsa dan ya ji akwai zazzaɓin ne ko babu, tabbas akwai ta a jikinsa, dan ga jikin nan ya yi zafi sosai, dawo da kallonsa kan Lion ɗin ya yi, gera ɗaya Lion ɗin ya ɗaga mishi alamar ya ake ciki? Jinjina mishi kai ya yi yana bashi tabbacin yes da akwai zazzaɓin a jikinsa, Juyowa ya yi ya dawo saman bed ɗin, hayewa ya yi tare da tallaɓo kan Aseef ɗin yana kallon cikin kwayar idanunsa.

Nan take dukkansu biyu suka shiga damuwa, A box Areef ya ɗauko dan su duba shi, shiru Lion ɗin ya yi yana tunanin cewa wannan zazzaɓi na Aseef ba zazzaɓin kwayar cuta ba ce, sai dai idan zazzaɓin tashin hankali ko makamancinsa, dan kuwa idan da zazzaɓin kwayar cuta ce dole za su ji a jikinsu na farko, na biyu kuma dole yanayin Aseef ɗin zai canza. Shi kuma Areef sai ƙoƙarin haɗa kayan aiki yake yi.

Kuka Aseef ɗin ya saka musu a kan shi dai ba za su yi mishi allura ba, ya warke dan haka su kyale shi, hannu Lion ya ɗagawa Areef a kan kada ya haɗa komai, da mamaki yake kallonsa, kwantar da kan Aseef ɗin ya yi a saman pillow tare da ɗan kwantowa kusa da shi yana faɗin "Menene ainahin abin da yake damunka?". Dama shi Aseef yariga da ya san tsab Lion zai iya gane zazzaɓin kwayar cuta da kuma ta firgici or tashin hankali, sai dai bai ɗauka da wuri haka zai gane ba, amma duk da haka sai ya kafe musu a kan shi babu wani abin da yake damunsa, hakan yasa Lion ɗin ya ce a kira mishi daddy Rimsha, dan yasan dole ne ma shi yasan menene yake damun ɗan uwan nasu, Areef na kokarin kiransa a waya, sai kuma ya ce no ya barshi kawai koma menene zai sani ne, shi kuma Aseef ya jira shi yana nan dawowa zai yi bayani ne tun da yaki gaya mishi gaskiya. Ya kai karshen maganar tare da miƙewa ya sauko kasa ya nufi waje dan aikin da yake yi bai karisa ba, ya dawo ɗaukar wasu abubuwa ne tare da birth certificate na Jehan.

Yana fita Areef ya dawo kusa da Aseef ɗin dan ya lallaɓa shi ko zai gaya mishi menene yake damunsa, nan ma dai kin faɗe ya yi, ya kafe a kan shi fa kansa ne yake ciwo da zazzaɓi, bayan haka kuma babu wani abu da ya sani, dole tasa Areef ɗin ya hakura ya kyale shi ba dan ya so, saukowa ya yi ya nufi waje, cikin sanyin murya Aseef ɗin ya ce "Areef please zo ka yi mini alluran barci". A sukwane ya juyo yana kallonsa da mamaki, wai me yake damun sa ne?.

Tunani cike fal ransa ya zo ya haɗa alluran ya yi mishi, bawan Allah yau tsawon kwana uku baya samun isasshen barci, yana son kuma ya yi barcin dan ya hutawa ransa, amma ina abin ya fi karfinsa, hakan yasa kawai ya ce ayi mishi alluran barci ko ya ɗan samu ya rintsa. Aikuwa ana yi mishi ba jimawa barci ta yi awon gaba da shi, Areef ya ɗauki tsawon lokacin yana kallonsa kafin ya miƙe ya fice daga ɗakin ya nufi nasa bedroom ɗin dan ya yi wanka ya je wajen Jehan a prison, gobe court zata yanke mata hukunci.

A ɓangaren Rimsha kuwa, tana fita bedroom nata ta koma..........

❤️❤️TRIPLETS❤️❤️



*Duk wace ta karanta mini littafina ba tare da ta biyani hakkina ba Allah ya isa ban yafe ba, sai Allah ya tsayar da mu ranar da bata da abin da zata biyani face ladarta*



E53-54💋



A ɓangaren Rimsha kuwa, tana fita bedroom nata ta koma, saman gado ta haye tana tunanin wai shi yaya Saif ɗin nan wani irin mutun ne? Sai ka rasa me yake damunsa sam.

Shi kuwa waje ya nufa dan ya je in da yake bukatar zuwa, har ya kai tsakiyar palon kasa sai ya tuna bai karɓi birth certificate ɗin Jehan ba, juyuwa ya yi ya nufo saman, bedroom nata kai tsaye ya nufa.

Kasa kasa ya yi sallama kafin ya faɗa, bata ji sallamar tasa ba sai dai ta ji daddaɗar kamshin perfume nasa da ya ziyarci hancinta, cikin sauri ta ɗago da kallonta zuwa bakin kofar shigowa, a bakin kofa ta ciki ya tsaya yana ɗan latsa wayarsa, zubur ta miƙe zaune tana kallon shi, tamkar ba bedroom nata ya shigo ba, ta ruɗe ta rasa me zata ce mishi, muryarta na rawa ta ce "Yaya Saif sannu da zuwa ina wuni?".

(Wayyo cikina 🤣 wai yaya Saif sannu da zuwa ina wuni)

Tamkar babu shi a wajen, ko kallon in da take bai yi ba, duk ya rikitata, dirowa kasa ta yi daga saman bed ɗin nata ta nufo shi, kusa da shi ta tsaya tana son tambayarsa me ya zo yi, kwata kwata ta manta da cewa ya ce ta bashi birth certificate na jenan, sai wani ƴan kame kame take yi, shi kuma ya kware wajen gindayar da mutane, yanzu ma dai shirun gindayarwar ya yi mata.

Sai da ya ɗauki good 5 mins yana tsaye kafin ya ɗago da kallonsa a kanta, kasa ta yi da kai, zubawa kyakkyawar dark black curly hairnta idanu ya yi, ba ƙaramin kyau gashin suke yi mishi ba, sai wani murza yatsun hannunta take yi alamar duk a tsarge take.

"Ina birth certificate da na ce ki kawo mini?". Cikin sauri ta ɗago idanunta ta saukesu a saman faffaɗar kirjinsa, "Ban gani ba ne, yana Abuja". Ta yi maganar cikin natsuwa, mamakin natsuwarta wani lokaci yake yi, wata zubin kuma sai ka ganta kamar wanda aka sakawa battery, rawan kai kamar me.

Ganin bai tafi bane yasa ta ɗan ɗago ido dan ta saci kallonsa, caraf suka haɗa idanu, kasa ta sake yi da kanta tare da takure kanta ta ɗan turo baki, wannan turo bakin da ta yi nan take ta tuna mishi da abin da ya faru ɗazun na iska da ya hura mata, laushin da lips nata suke da shi ne kawai yake yi mishi yawo a cikin kwakwalwarsa.

Tuna hakan kuma yasa ya juya ya fice daga ɗakin, bin bayansa da kallo ta yi har ya isa tsakiyar palon saman, a nan ne kuma suka haɗu da Areef da ya fito daga bedroom nasa bayan ya yi wa Aseef allura kenan.

Tsayar da shi Areef ɗin ya yi yana faɗin "Gobe za'a yankewa baby hukunci fa, kuma ka san kai tsaye hukuncin kisa zasu yanke mata, yanzu me abin yi? Ka dai san tana da gaskiya ko? Kare kanta zata yi ta kashe shi bisa kuskure, kuma kasan wannan hukuncin da ta yi mishi dai'dai ne, dan ko kai ka kama irin shi, wannan hukuncin zaka yi mishi". A takaice ya ce "To ina ruwana da case ɗin?". Ya kai karshen maganar tare da wucewa ya sauka kasa abinsa, bin bayansa Areef ɗin ya yi ba tare da wata damuwa ba dan yasan Lion ɗin ba zai taɓa bari a kasheta ba, dan kuwa yasan tana da gaskiya, kuma mugun iri ta kashe, shiyasa bai wani damu ba ya bi bayansa suka sauka kasa ya wuce bedroom nasa.

Ita kuwa Rimsha tun da ta ji abin da suka tattauna hankalinta ya yi kummunar tashi, nan take hawaye suka fara wanke mata fuska, shikenan za'a kashe Jehan kenan? Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun, ba zata iya jurar wannan bala'in ba, saman bed nata ta koma ta kwanta, hawaye tamkar ruwan famfo haka yake gudu a face nata, ji take yi duniya na juya mata, har wani duhu duhu take gani yana gilma mata ta cikin idanunta, daga Lion ɗin har Areef ɗin ba wanda ya san ta ji abin da suka tattauna, da sun ji Areef ba zai tafi ba har sai ya tabbatar ya kwantar mata da hankali.

Haka ta kwanta har aka kira sallar la'asar, jiki duk a mace, da kyar ma ta iya mikewa ta yi sallar, bayan ta idar ta yi wanka ta shirya cikin Abaya sannan ta fito zuwa kitchen dan ta ɗauki abincinsa ta kai masa, tun karfe 3 ta ji dawowarsa, amma ta san ba zai ci abincin a lokacin ba, shi ne yasa ta yi kwanciyarta kawai.

Kitchen ta nufa, tsaye ta isko Mark yana latsa wayarsa, sannu ta yi mishi, bai amsa ba, bai kuma ɗago ya kalleta ba, tamkar dai babu shi a wajen kamar kullum, wanke hannunta ta yi ta ɗauki abincin ta fito ta nufi bedroom ɗin nasa.

Bakinta ɗauke da sallama ta shiga, yana zaune saman bed nasa ya jingina da jikin headboard na gadon tare da rufa bargo zuwa daidai saitin cikinsa yana latsa waya. In da ta saba ajiye mishi abincin ta nufa, ajiyewa ta yi tana ƙoƙarin zama kenan muryarsa ya daki dodan kunnenta. "Kawo mini fruits kawai is okey". Ya yi maganar ba tare da ya ɗago ya kalli in da take ba.

Okey ta amsa mishi da shi tare da ɗauko mishi ta nufo shi, saman bedside drawer ta ɗaura plate ɗin tare da zama a saman carpet ɗin dake wajen, cike da tsoro ta ce "Yaya Saif ina son zuwa prison in ga Jehan". Shiru ya yi bai kulata ba, almost 10 mins suna haka, sannan ne ya ce zata iya tafiya bedroom nata, kuma kada ta kuskura ta fita daga gidan nan, ba zata je prison ɗin ba.

Da sauri ta miƙe ta nufi waje, tana shiga bedroom nata ta faɗa a saman gado tare da sakin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro, shikenan idan ma kashe Jehan ɗin za'ayi ita ba zata sake kallonta ba, innalillahi wa inna ilaihir rajiun, wannan bala'i da me tayi kama? Ji ta yi kamar ta rataye kanta dan bakin ciki, har wani irin shasshekar kuka take yi wadda daga ji kasan zuciyarta a kusa take, kiris take jira ta yi bindiga.

Shi kuwa ko a jikinsa ya sha fruits nasa kafin ya gyara kwanciyarsa da kyau tare da lumshe idanunsa kamar mai barci.

A ɓangaren Areef kuwa, wanka ya tsara ya nufi prison ɗin shi da Donald ɗaya daga cikin sojojin Lion, a lokacin Mark yana aiki shi ne yasa ba su tafi tare ba.

Sai da suka biya super market ya saya mata wasu abubuwa da yake ra'ayi, sannan ya fito suka nufi prison ɗin

Office ɗin shugaban gandurobobin ya zauna tare da bukatar ganinta, ba ɓata lokaci kamar dai kullum suka fito da ita, sun zuba mata sarkoki a hannu, dama idan za su fito da babban mai laifi haka suke yi.

A kasa saman carpet ɗin gandurobar ta zaunar da ita, hankalinta a kwance tamkar ba ita za'a yankewa hukunci gobe ba, Ameera da ba ita za'a yankewa hukunci ba ma, ta shiga tashin hankali sosai, duk bayan minti ɗaya sai ta ce "Yanzu Jehan ke sam baki damu ba? Kuma kin san hukuncin kisa zasu yanke miki fa ko?". Tsaki take ja tana faɗin "To idan su suka riƙe raina ba sai su kashe ni ɗin in gani ba, wai ma su suke da wuta ko aljanna ne? Ni fa Ameera ki daina damuna, duk wanda kika ga ya mutu to lokacinsa ne ya yi, idan lokaci kuma ya yi, ko a saman kadon kuɗi da mulki kike kwance sai kin mutu, to idan mutun ya san haka me zai wani takura wa kansa? Ke ni bari ki ji wlh ni bana ma ɗaukar alkalinma kamar mutun bare har na ɗaga idanu na kalle shi, ni dai nasan ga abin da na yi, so wannan tsakanina ne da ubangijina, idan sun cuceni a nan sun nuna mini fin karfi, suma suna nan zasu zo in da zasu turani ɗin, tun da babu wanda Allah ya ce zai tabbata a duniya, kowa sai ya mutu, dan haka za su mutu su zo su same ni suma, a nan ne kuma mai karfin iko, malikiyaumiddin mamallakin ranar sakamako zai karɓa mini hakkina, lokacin kuma babu wata rai da zata iya musawa ta ce bata yi kaza ba, ko kuskure aka samu, duk babu wannan korafin, ranar hukunci ne da ubangiji subhanahu wata'ala zai yanke ta dai'dai da abin da kowa ya yi, idan ta yi maka daɗi, ka yi da kyau kenan a duniya, kuma da haka zaka yi ta kallon mai kyau har abada, idan bata yi maka daɗi ba, to fa farkon kofar rashin jin daɗin rayuwarka ce ta buɗe har Illah Masha Allah, so dan haka ki dai'na takurawa kanki muddin kin san da mai wuta da aljanna kika dogara ba kato ba!!".

Baki Ameera take sakewa tana ganin ikon Allah ita dai, duk a tsorace take, amma ita da za'a yankewa hukunci ko a jikinta, hankalinta kwance tamkar wanda take gidan iyayenta tana shan Ac mai sanyi.

STORY💋

Zuba mata idanu sosai Areef ya yi yana kallon ramar da ta yi, sam baya son hakan, ba karya ta rame saboda zaɓar abinci da take yi, ji yake yi kamar ba zai iya hakuri ba, gara mishi kawai ya ɗauketa su tafi gida, amma yasan Lion ba zai yarda da hakan ba, dan ya saɓa doka, hakan yasa yake daurewa kawai yake kawar da kansa ya barta a prison ɗin.

Kallon shugaban gandurobobin ya yi, cikin natsuwa ya ce "Zaka iya bamu waje dan zan yi magana ta sirri ne da matata". Wani kallon sama da kasa ta wurga mishi, wai mata, ko waye ya bashi ita oho mishi.

Kashe mata ido ɗaya ya yi yana mata signal da gera ɗaya, guntun tsaki ta ja, dan duk lokacin da ya yi irin hakan, kama yake yi mata da tantiran maza irin ƴan duniyar nan, sai ya wani kashe ido ɗaya kamar wani tantirin ɗan iska, shi kuma ya saba abin ne sakamakon zaman da ya yi cikin ƴan ta'addan da ƴan iska, shi ne ya koyi abin, sai kuma ta zamo mishi jiki, har idan bai yi ba ma baya jin daɗi.

Miƙewa shugaban gandurobobin ya yi ya nufi waje, kallon Donald ya yi, tun bai yi magana ba shi ma ya fice da sauri abinsa.

Dawo da kallonsa kanta ya yi, cikin zolaya ya fara magana "Tun da ba zaki gaishe ni ba ni bari na gaishe ki? Ya jiki?". Kasa kasa ta amsa mishi da ta ji sauki.

"Wai da gaske baby har yanzu baki fara tunanina ba?". Ya yi maganar murya a sanyaye, kuma can kasa kasa ya yi maganar, harara ta watsa mishi ba tare da ta yi magana ba, dan a cewarta bata da lokacin ɓata bakinta na magana da shi, ga shi sai bala'in tsoronsa dake ji cike fal ranta, a fili kuma sai karfin halin bala'i.

Miƙa mata ledar hannunsa na shopping da ya yi mata ya yi yana faɗin "Okey tom shikenan yanzu dai bari na gama da case ɗin naki, dole zan koya miki tunanina, amma first yanzu dai karɓi wannan". Kin ɗagowa ma ta yi ta kalle shi bare ta yi ƙoƙarin karɓar ledar duk da hannunta ma dama da sarka a ɗaure, hakan yasa ya ɗaura mata ledar a saman cinyarta yana kara kare mata kallo, kyakkyawan gashin kan nan nata da ya sha gyara a gidan Hjyr daɗi kafin ta biyo Abubakar jaja, sai kyalli gashin yake yi in da ya leƙo ta cikin hijabin nata.

Hannu ya kai ya ɗan zame hijabin nata zuwa baya, ya sauke shi kenan daga kanta zuwa wuyarta, abin haushi shi ne hannunta ɗaure da sarka ba ta yadda zata yi ta buge hannunsa ko ta hana shi ya ta ɓata, ɗaure fuska sosai ta yi tana faɗin "Kada ka taɓa mini gashi". "Gashin ki ne ko nawa?" Harararsa ta gefen idanunta ta yi bata sake ce da shi komai ba, dan ko wani amsa ta bashi sai ya sake kawo mata wata maganar kuma, rufin asirinta kawai shi ne ta yi shiru.

Hannun ya sanya yana tara mata gashin nata yana faɗin "Uncle nawa yana zuwa gobe, dole na san abin yi, bana son uncle na ya zo ya same ki a nan, amma In Sha Allah nasan Lion ba zai taɓa bari a yanke miki hukuncin kisa ba, nima kuma ba zan bari ba, ki kula mini da kanki sosai, kada ki ji komai, gobe yiwar haka muna tare a gida, tare zamu ci abincin rana". Ko sannu bata ce mishi ba har ya tare mata gashin nata, pil ɗin da yake ɗaure gashin kansa da shi ya zaro ya


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login