Showing 255001 words to 258000 words out of 381117 words

Chapter 86 - Auren Katin Kasa Book 1 Complete Hausa Novel

07 Feb 2025

1984

nan ya buqaci da yayi mashi bayani akan operation din da komai daya kamata ya sani.

Cikin Yan mintuna qalilan jirgin su ya daga sararin samaniya& ..
Adawo lpy sir general=?-?

Yau kwana biyu kenan bayan tafiyar Amar, gidan yayi shuru kamar an dauke masu annurin gidan, ammah kullum tana daki, abu daya ke fiddata daga daki shine dubo amra don sanin yanda ta Tashi, aranar da Amar ya tafi wahee gari ya chanza masu securities na gidan gaba daya, Banda baba mai gadi, sannan ya sanya asad yayi mashi inspecting wani babban company da suke kawo helps daga wata kasar, nan yasa asad yayi mashi kwakwaran buncike akansu kafin a kawosu gidan, ya mata ne guda biyu akalla zasukai shekaru talatin talatin, dukkansu Yan phillipines ne, bai yarda ya kawo Yan Nigeria ba,
Salima ne tayi kokarin training dinsu akan ayyukan gidan don kusan a tare suke yin komai, daya danganci abunci don basu iya abuncin mu na nan Nigeria ba,yanxu ayyukan gidan Duk ya koma hannunsu.
Yau sati guda kenan da graduation din salima, don haka amra tayi deciding fada mata komai, don daman dalilin dayasa ta ki fada mata was saboda Karta fada ma Aman don idan ta fada mashi zai ita fada ma Amar shiyasa ta qi fada mata a wanchan lokacin, yanxu kuwa inka ga yanda suke ma junansu kamar zasu cinye juna.

Zaune take akan gado hankali kwance tana chan mango da salima ta yanka mata,ayanxu bata da wata damuwa kwata kwata, don daman Amar ne ke bata ciwon kai, tun bayan tafiyarshi kuwa hankalinta ya dan kwanta, bata wani damu ba da alamarinshi don harta ma manta dashi saboda basu da wani memories mai dadi da zaisa ta tuna dashi saidai sometimes yakan dan fado mata arai.
Sallama salima tayi hannunta rike da wani plate din ta sake yanko mata saboda ta buqaci hakan, tana zuwa gaban gadon ta ajiye mata akan gado tana turo baki don hira take da habibinta a sabuwar wayar daya bata don yaje office shine ammah ta tado akan tazo ta yanka ma amra mango.
 Gashi nan, dan Allah abarni na huta haka nan, Wallahi adda lamarinki gaba yakeyi kamar wata mai ciki tana kaiwa nan ta juya, amra kuwa mai zatayi Banda dariya din haka Tayi saurin katseta  ba laifina bane laifin danki ne ay
Da sauri salima ta juyo don bata gane inda ta Dosa ba, shafa belly bump dinta tayi kafin ta maida kallonta kan salima  kingani ba? Shike damunki bani ba
Da sauri salima ta tako inda take idanunta a waje Bakinta ya kasa rufuwa ta shafa cikin amra  adda baby ne anan?
Salima ta fada tana shafa cikin amra, girgiza mata kai amra tayi tace  yes& 
Fadin irin farin cikin da salima ta shiga a wannan rana bata lokaci ne don kowa saida ya shaida hakan a gidan, she s so happy Harda dan kukanta.


After one months& .
A kwana a Tashi babu wuya yau wata guda kenan da tafiyar Amar, ayanxu hankalin ammah ya gama Tashi, wata guda kenan tun bayan tafiyarshi da sukayi waya sau daya lokacin daya shaida mata sun isa wajen operation inda bai fada mata ba saboda basa fadin work related to anyone hatta family wannan dokar sojoji ce.
Fadin irin tashin hankalin da ammah ke ciki bata lokaci ne ta rame sosai saboda tunanin Amar, this is the first time hankalinta ya Tashi da tafiyar da yayi don this is not the first time yake tafiya operations, don Duk sanda zaije koda yana chan dubai saiya fada mata kuma haka zasuyi kusan wata biyu basuyi magana ba idan yana chan Duk bata damuwa saidai akasin na wannan Karan abun ya dameta sosai, Wai irin unnecessary tunani take yi aranta wanda ada bata yinsu kwata kwata,  what if wani abu ya sameshi? What if something is wrong? Kullum tambayar da take ma kanta kenan, abunda yafi damunta shine sai yanxu take dana samun fada mashi maganar cikin amra.
Tana nan zaune amra ta shugo dakin, kallonta na???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?yi sama Har kasa sanye take da doguwar rigar atamfa bubu anyi nata free gown da ita, tayi wani irin bulbul skin dinta yayi haske sosai kamar jini zai fita, fuskanta tayi fayau, ga dan baby bump dinta daya futo ba laifi don yanxu kana ganinta kasan tana da ciki, yanxu cikinta watan shi bakwai da sati guda.

Shugowa tayi dakin atsanake ta karaso Ind ammah ke zaune Har zata zauna a kasa ammah ta kalleta jiki a mace kana ganinta kasan tana cikin damuwa sosai  haba daughter, baba hanaki zaman kasa ba yanda kika fara nauyin nan
Murmushi amra ta danyi kafin ta zauna gefen gado ta gaisheta, cikin fara a ammah ta amsa mata. Shuru ne ya buyo baya kafin amra ta soma magana  ammah, Akwai abund ake damunki ne?
Shuru ammah tayi kafin ta nunfasa  babu komi daughter,kinci abunci?
 Eh naci tuwo amra ta bata amsa
 Ammah please Ki fada min abunda ke damun ki, bakya cikin walwala kwanakin nan
Kallonta ammah ta danyi baya son ta saka mata damuwa don haka tace  daughter yau wata guda kenan rabon da na samu son a waya, wayarshi baya shiga kwata kwata, Ina jin kamar wani abu ya faru
Hannunta amra ta kama kafin ta soma magana in a calming tone  ammah ki kwantar da hankalin ki, nasan he s perfectly fine Insha Allah, maybe Har yanxu basu gama operation sun bane shiyasa bakya samunshi a waya

Haka amra ta dunga tausasa ta da kalamai masu kwantar da hankali harta danji nauyin da zuciyarta keyi ya ragu, hira suka danyi don yanxu inka gansu kamar uwa da ya babu wani kunya, amra ta sake sosai da ita.

Washe gari suka shirya da ammah da salima da amra suka wuce asibiti don salima tace Yanxu dole da ita za a dunga hidiman baby, suna zuwa doctor ya duba lafiyar baby Har alokacin ammah taki yarda Suga gender na baby don haka doctor ya bata magungunan Karin jini da wanda zai dunga sakata cin abunci don zatafi buqatan hakan ayanxu don ta kusa shiga wata takwas wanda ya zamana anzo gangara.


Bari mu Yan katsina& .
Duniya ta juyama wannan family baya, yanxu taluacin da suke ciki haryaci uwar na da saboda da khady kawai suka dogara da take saida gwanjo itama ribar yanxu tayi kasa saboda hidiman gidan daya dawo hannunta dukda ba wani kudin arziki take fiddawa ba idan zasuyi cefane kullum, dari biyar ce safe da dare don ba a cin abuncin rana a gidan, dady kuwa tun bayan wannan targade da yayi har kayi mashi gyara a hannu da kafa, inda a hannunshi samu karaya while kafar kuwa ya samu targade, Toh da dai gyaran karayan nan baiyi ba kafarcema ya dan samu sauqi saidai hannun ne ya shanye gaba daya baya wani amfanuwa, sai kuma jan ruwa da yakeyi saboda inda ya ciwo wajen hannun ba a yi dressing ba haka gudaje da bad environment din wajen yayi affecting hannun, nan ya dunga Jan ruwa sai wani karshe dai hannun shanyewa tayi babu wani amfani.
Haka kullum zai zauna a gida baya uban komai, tun kareema na jin tsoro shi lokacin daya gano tana da cikin shege har tazo ta daina tsoronsa take gasa mashi aya a hannu, zagi cin mutunci babu wanda basa yima juna agaban yayansu, yaranma Har sun saba da yanda iyayensu keyi ma junansu, ah anguwa kuwa babu wanda baisan kareema matar mustapha mai damfara nada cikin shege ba, tayi cikin shege da aurenta, wannan zance yasa ko fita bata iyayi yaranma idan sun futa da irin zagin da ake jifansu dashi kenan, khady dai ta gama zama yar tasha idan ma an fada bata wani damuwa don Har cewa take  Toh saime idan tayi cikin shegen idan uwar wani ce Tayi ku fada min badai tawa uwar bace to munji tayi ciki
Yanda ta zama yar daba daba yasa wasu idan sunso goga mata magana suke kyale ta saboda kangararren saurayin ta.

Bangaren wahab yana chan a kurkuku don asad saida ya tabbatar an yanke mashi hukunci daidai da abunda yayi, nan aka kaishi prison na shekara goma,don Akwai diyyar daya kamata ya biya wanda yayi ma yarinyar maqocinshi na chan lagos fyade inda aka tuntubi iyayenshi ko zasu iya biya don in ba a biya ba shekarun da zaiyi a prison zai karu, nan aka tuntubi Alhaji mustapha, lokacin da suka kirashi ma yana gida a zaune babu uban abunda yake sai zaman banza don haka da sukayi mashi bayani nan take yace  ku rufeshi kawai babu abunda zaku samu a waje na
Yana kaiwa nan ya kashe wayar baima tsaya sauraron su ba, da kareema ta tambayi ko da wa yake waya kai tsaye ya mata bayani, nan take ta dunga kuka tana tsine daddy kan Duk shine ya janyo masu wannan masifa Har yayanta suka wulaqanta gaba daya saboda zalumcin shi da cin amanar dan uwansa da yayi na wulaqanta yayansa.
Nan suka dunga Sarfa ma junan su zagi ta uwa ta uba  kije kiji da shegen ciki wahallaiya asararriyar mata Wallahi nayi dana sanin aurenki kareema kina da kaso mai girma a cikin lalata rayuwata kece ma baqar kafar data lalata kin komai, badan kin sa an zubar da waennan yarannan ba da tuni na samu wani abun a wajen yayarsu
Kallonshi karima tayi tana takaici ace Wai mutun baiyi nadama ba ko kadan,  shiyasa zaka kare a haka a wulaqance, Har yanxu zuciyarka a mace take
Nan suka cigaba da cece kucensu dagashi Har ita aka rasa wanda zai jaa baki yayi shuru maqota na jin su.

Bangaren Muhammad kuwa yana chan Australia, yau watanshi biyar kenan, acahn yaqi dawowa don daddy s ya kirashi ya shaida mashi uwarshi tayi cikin shege don haka ya tura masu da kudi, ranar da yaji wannan baqin labari ya shiga tashin hankali sosai inda ya ko sun kirashi ma kasa daukan wayan yakeyi don yana Allah wadai da iyaye nashi, wannan yasa yaqi dawowa yayi zamansa acahn ya maida hankali wajen aikin shi inda yake taimakawa kaninshi ishaq daya dage yana masters dinshi anan Australia don bayan ya gama karatu ya dawo wajen Muhammad nan ya muyi sponsoring dinshi ya samu schorlaship nan ya fara masters.

Bangaren kakarsu salima kuwa, rana daya Allah ya dauki ranta anan kauye inda take zaune wajen dan uwanta, tayi jinya sosai inda suka dunga bata maganin gargajiya da farko kamar komai ya lafa sai daga baya kuma gadan gadan ciwon nata ya dawo Har Allah ya dauki ranta bata samu damar Ganin marayun jikokinta ba.

Bangaren labaran shima bayan noma haka ya samu yayi renting wani kanti nan kusa da inda yake yake haya, nan yayi amfani da kudin da ammah ta bashi ya zuba provision a cikin shagon don bashi da wani girma sosai, cikin wata biyu wajen ya bun kasa don haka ya hade da shagon dake kusa dan wanda yake haka, cikin ikon Allah Allah ya by kasa mashi, don Allah ya bashi wannan baiwar da zarar ya saka hannu akan abu sai Allah ya bukata mashi, kullum kuwa saiyayi mafarkin yarannan guda uku ada chan baya yana mafarkinsu baya Ganin fuskokoinsu saidai shadow dinsu kuma yana jin saurin kukansu Yanxu kuwa yakan iya ganin su a fili saidai Har yau baiga fuskokinsu ba saidai yaji su suna dariya.
Bayan wannan Har yanxu zane kam yana. Yin shi, don idan ya dauka alakali yana Zane kamar wani pro nan ya gane cewa yayi ilimi don saida ilimi zaka iya zane irin wannan da ake kira da architecture.
Abunda yafi daga mashi hankali kuwa shine Akwai ranar da yazo tsallaka titi bayan ya dawo daga shago, nan take wata mota taso bugeshi Allah ya rufa asiri mutumin ya Taka burki nan take flashback din wani mummunan accident yazo mashi, inda anan ya gane lokacin da yayi accident ne kenan, everything was dark don haka bai gane komai ba.

Alhaji kabiru dai Ana chan prison shima an kaishi gidan yari inda zai gama rayuwar shi acahn gaba daya, irin dukan dasu asad sukayi mashi yasa yayi loosing site dinshi daya, ya rame ya jeme ya zama kamar wani mai kanjamau, talking of kanjamau lokacin da yayi wata irin rashin lafiya anan prison aka kaishi asibiti nan akayi mashi test take kuwa aka gano yana da hiv.
Haka aka sallamoshi bayan ya danji sauqi aka maidashi prison aka rufe shi, Har lokacin he can t imagine rayuwarshi zata juya ta zama haka ba, ya zama kaskantacce, ya lalace kuma naka sasshe bashida kowa bashida komai, dukiyar daya tara ta hanyar haramci bata amfaneshi da komai ba saima jefa shi cikin mawuyacin hali datayi.
Aman Duk wata yana zuwa nan prison yana dubashi, wani sa in yakan futo ya ganshi wani sa in kuwa haka zai Karaci zamanshi daddy yaqi futowa don yanxu blaming dinshi yake yi akan cewa ya cuceshi yana matsayin ubanshi ya fallasa asirin sa.

Su lantaana da doctor ma ana chan ana serving a gidan yari, kowannensu an bashi shekara biyar for attempting murder.



Abuja Nigeria& &
After 2 months&
Yau wata biyu kenan da tafiyar Amar, Har ranar dai shuru babu labarinshi, at this point hankalin ammah ya gama Tashi don haka ta fara neman manyan mutane da ta sani acahn dubai en, shuru dai Har lokacin don haka ta fara tunanin zuwa dubai din saidai kuma tunawa da amra tayi nauyi yanxu yasa tayi cancelling tafiyar.

***
Ammah ce zaune a sitting room hannunta rike da charbi tana lazimi gefenta Salim ne dake ta faman yin game a wayar Salima don batama san ya dauko ba tana barci.

Ahankali ta soma saukowa tana dingisawa harta sauko daga stair tana nishi, amra ce sanye da doguwar rigar chan iska wadda ammah ta sayo mata su da yawa saboda ta dunga sakewa a cikin rigar, saurin nishin da takeyi ne yasa ammah ta kalli inda take tsaye bayan ta sauko kasan, murmushi kawai ammah takeyi harta karaso parlor, kallonta ammah tayi da yanda yake tafiya, cikinta ya futo sosai kamar mai wadda zata haihu yau ko gobe, daman doctor ya fada masu cewa da zarar takai wata takwas cikin nata zai bude, yanxu kuwa cikin nata yakai 8months da sati daya, cikin ya futo sosai kuma yayi mata kyau sosai, ta Kara fresh da kyau kamar bamai ciki ba babu wannan kumburu fuska da na hanci, dass dass abunta.
 Wash barka da yamma ammah ta karashe tana zama gefen kujera mai zaman mutun biyu
 Sannu daughter kina kokari, wannan babyn namu tubarkallah
Dariya amra ta danyi kafin ta kalli inda Salim yake tace  kai kuma baka daddara ba ko, saita sauko ta mammake zaka daina daukan mata wannan wayar yar gold din
Dan murmusawa ammah tayi tana kallonsu.
Salima ce ta sauko rai a bace Har tana grade kafafunta daga stairs, tana karasowa parlorn tayo kan salim,  kai Ka gama rainani ko? Toh Wallahi yau Saina koya maka hankali
Tana kaiwa nan tayo kanshi, ammah ne Tayi saurin hanata  haba yarinyar kirki, yi hkui bazai sake ba kinji
 Ki barta ta bugeshi ammah tunda baya ji, haka ya lalata min yawa Yanxu kwata kwata idan an kirani baba jin kara amra ta fada tana kallonsu
 Ah ah baza ayi haka ba daughter karban wayar ammah tayi daga hannunshi kafin ta mikama salima  ungo yarinyar kirki yaci albarkaci na
Dungure kanshi salima tayi kafin ta karbi wayar, alokacin call din Aman ya shigo don haka ta wuce sama abunta tana murmushi.
Kallonta amra tayi da yanda jikinta ya dau zumudin Kira harta wuce sama, shuru ta danyi don sai a lokacin amar ya fado mata, dukda tana kokarin hana zuciyarta tunanin shi saidai hakan ya gagara don yanxu idan babyn cikin ta ya danyi motsi shine yake fadi mata arai.

Suna nan zaune wayar ammah tayi vibrating, dan waigowa ammah tayi, kamar a mafarki idanunta ya sauka akan sunan Amar, cikin sauri ta dauka wayar Har hannunta na karkarwa yau wata biyu kenan rabonta dashi,  hello hello son is that you
Cikin jin dadi da murna Amar yace  yes ammah nine
 Subhanallah!! Son in Ka shiga Ka barmu cikin damuwa, wata biyu& 
 So sorry ammah na shiyasa na kira ma yanxu, ko sauka bamuyi daga jirgi ba ayanxu haka maganar da nake dake
 Ya kake are you okay babu abunda ya sameka? Kana cikin koshin lafiy& 
Saurin katseta yayi  I m fine ammah, please don be worried I m perfectly fine okay? Hope kuma kuna nan lafiya?
 Yes son we re fine alhamdullah yaushe zaka dawo? I have something very important to tell you
 I don t know ammah, saimunyi rounding up komai anan, but inason ki kwantar da hankalinki I m perfectly fine, Muna gama operation Zan dawo Insha Al& .
Dip wayar ta dauke, amra data gyara zama tana. Kallon ammah data sauke wayar, gaba daya ta maida hankalinta kan ammah haka zalika Salim shima yana daga gefe yana kallon ammah Duk sun zama curious suji ko lafiya,
 Ammah lafiya dai ko?
Dan Nunfasawa ammah tayi tace  Alhamdulillah, son ne yace yana lafiya Har yanxu basu gama operation bane
Wata ijiyar zuciya amra ta saki Har yasa ammah ta juyota.
 Har hankalina ya kwanta daughter, yau wata biyu da kenan, alhamdullah ya Allah
Sauke kanta kawai tayi kasa batace komai ba, saima wasa da Yan yatsunta data fara.

Washe gari wajen karfe biyu suka fito gaba dayansu, da yake weekends ne, sunyi kyau gaba dayansu daga kan amra zuwa salima sai ammah, Duk sunsha native kaya, atare suka fito gaba sayansu suka wuce motar ammah, ammah ne ke jan motar sai salima a bayan motar,
Anatse ammah ke drinving while tana dan duban amra ta jikin mirror, hira suka dan farayi a tsakanin au inda amra dai saidai tace uhm ko ah ah saidai kuma in anyi abun dariya Harda ita ake kyakyatawa.

Gaban wani katon mall suka 360 mall, mall din ya gadu sosai don yana dauke da wani


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login