Showing 33001 words to 36000 words out of 300844 words

Chapter 12 - Tagwaye Book 1 Hausa Novel Complete

22 Dec 2024

2038

ba zan boye maka ba tun ranar dana fara ganinka naji zuciya ta tana sonka, naji a raina ina ma dai kai dana ne, kuma yanzu zanji dadi sosai idan ka zamo dan nawa wato in ka auri yata, sai dai, in har ka amince ina son ka chanza daga Ruqayyah ka nemi Sumayya"

Ruqayyah ta dago kai daga yankan farcen ta, ba tare da ta ce komai ba ta mike ta tafi daki tana jin zuciyarta ta zama tamkar dunkulallen garwashin wuta.

Wannan littafin na kudi ne, duk mai son siya tayi wa wannan number din magana 08067081020


Episode thirteen: The Strategy

Duk suka yi shiru suna kallon sa, Hassan cikin sanyin jiki yace "saboda me Baba?" Baba yace "Saboda kamar yadda na fada ina sonka, duk su biyun yaya na ne basu da banbanci a guri na kuma suma duk ina son su, dan haka nake fatan idan sunyi aure auren nasu zai zauna har mutuwa, bana fatan ka auri yata kuma ka rabu da ita saboda wani hali nata da zaka ga baiyi maka ba, wannan shi yasa nake ganin alakar ku zata fi tafiya daidai da Sumayya, saboda a yadda na fahimta kamar halin ku yafi zama daya akan ita Ruqayyah"

Jabir yayi gyaran murya yace "Baba ita Ruqayyah tana da wani aibu ne? Wani hali da ya kamata a sani kafin a aure ta? Ko tana da wata cuta ce?" Baba ya girgiza kai, Ruqayyah yarsa ce kuma yana sonta, kuma son da yake mata ne ya saka shi wannan batu, aure ba abin wasa bane ba, ba kuma a gina shi a kan ƙarya da rufa rufa in dai har ana so ya dore. Yana son auren Ruqayyah da Hassan ya dore in dai ya kasance, shi yasa zai gaya masa in zai aure ta a haka shikenan in kuma ba zai iya ba sai ya karbi Sumayya in ita ma baya so shikenan.

Yace "Ruqayyah tana da zafin zuciya sosai, taurin zuciya da kafiya, ko mu iyayenta muna fama da ita a kan hakan. Bata da son mutane sosai saboda tana da fada, bata da tsoro sam. Kai kuma na fahimci mutum ne mai jama'a dan haka nake ganin kamar tafiyar ku ba zata zo daya ba"

Hassan ya shafa kansa yana sauke ajjiyar zuciya, shi baiga aibu a duk abinda Baba ya fada ba, dama ai ya riga yasan da rashin tsoron da taurin zuciyar tun sanda ta taimaka masa, rashin son mutane kuma shi zai iya cewa abin dadi yayi masa dan shi din ma ba mai son mutanen bane ba dan haka kullum yake fatan kar ya samu mace mai kwashe kwashen mutane yadda zasu ji dadin zamansu su kadai.

Yayi murmushi yana kallon Jabir shima da yake murmushi, sun dai fahimci cewa Baba mutum ne mai karanci da yawa yadda har zai fada musu abinda yake ganin aibu ne akan yar da ya haifa a cikinsa saboda ya kyautata dangantakar sa da su. Hassan yace "Baba ni ina ganin wannan ai duk ba wani abu bane ba, wannan ba abinda zai hana ayi aure bane ba, kuma ni itan dai Baba in za'a bani ita nake so Sumayya kuma sai ta zama kanwata" Jabir yace "wannan haka ne, kuma kusan duk halin daka lissafa irin na Hassan ne" ya fada cikin tsokana, "haka muke ta fama dashi, baya daukan raini ga kafiya, ina jin abin nasu a sunan ne" suka yi dariya su biyu banda Baba, shi gani yake yi kamar basu fahimce shi bane ba, amma zama da Ruqayyah su kansu da suka haife ta dauke kai kawai suke yi a lokuta da dama, suna ta yi mata addu'a kuma suna saka ran idan ta kara girma zata rage, sai dai baiyi tsammanin za'a zo neman aurenta haka da wuri ba. Yayi wa Hassan tayin auren Sumayya ne saboda yana ganin Hassan da Ruqayyah ba wai saba wa suka yi da junansu ba.

Yace "shikenan tunda kunji kuma kun amince, kunga nan gaba ba zaku zo min da korafi ba kuma. Zamuyi ta muku addu'a, Allah yayi mana jagora baki daya, Allah ya hada kanku. Na baka damar ka neme ta, idan kuma ka chanza shawarar a tsakiyar neman ka sani ba zan kullace ka ba sai dai ba kuma zan baka Sumayya ba a lokacin".

Hassan yace "insha Allahu hakan ma ba zata faru ba. Kowa a duniya ai dole yana da wani aibu da wadansu daga cikin mutane ba zasu so ba, ko ba Ruqayyah ba nasan bazan samu mace da take da komai ba dole sai an samu aibu".

Suka yi godiya, sannan Baba ya jero musu doguwar addu'a duk duka shafa suka tashi. Hassan yaso yaga Ruqayyah amma kuma yana jin nauyin Baba, haka ya shiga mota suka tafi yana kallon kofar gidan da fatan ko Allah zai saka yaga giftawar ta.

Ruqayyah tana shiga daki sai ta kwanta akan katifa ta jawo zani ta lulluba duk da ba wai sanyi take ji ba, so take tayi kuka amma kukan yaki zuwa, haka taje ji lokuta da dama idan aka bata mata rai sai dai tayi ta jin zafi a ranta ba zata iya kuka ba har sai ta samu tayi masifa tukunna zata ji ta huce. Idonta ya kada yayi jawur kamar garwashin wuta. Anya kuwa Baba ne ya haife ta? Anya kuwa uban da ya haifi ya zai iya yi mata abinda Baba yake shirin yi mata? Har zai ce zai bawa Hassan Sumayya? Zai ce da Hassan kar ya aure ta? Ita kuwa wanne irin laifi tayi wa Baba da yayi mata irin wannan tsana haka?

A lokacin Sumayya ta shigo dakin, farko bata lura da Ruqayyah ba sai daga baya ta ganta a takure a karshen katifa, ta taba jikinta da sauri "innalillahi wa inna ilaihir rajiun, Ruqayyah baki da lafiya? Menene ya same ki?" Sai a lokacin Ruqayyah ta samu hawaye suka zubo mata, ai kuma ta fara rera kuka marar sauti kamar zata fito da zuciyarta, Sumayya kawai ya rungume ta ta barta tayi ta kukanta sai data gama sannan tace "Sumayya Baba baya sona ya tsane ni" da sauri Sumayya ta rufe mata baki tace "subhanallah, me kike fada haka? Baba yana son mu mana, yana son mu sosai da sosai" Ruqayyah tana girgiza kai tace "yana sonki dai amma banda ni. Ni ya tsane ni kamar bashi ya haife ni ba" sai ta bata labarin abinda taji.

Sumayya ta dora hannu aka fuskarta rubuce da tashin hankali sannan ta sauke tace "me ya kaiki Ruqayyah? Me ya kai ki zuwa kiji abinda zasu ce, ina ruwanki" Ruqayyah tace "magana ta fa zasu yi, zuciyata tana ta gaya min inje inji abinda zasu ce ashe akwai dalili, ashe zuciyata bata yarda da Baba bane ba"

Sumayya tace "wato ke kuma shikenan duk abinda zuciyarki ta gaya miki shi zakiyi? Ba zaki yi tunani da kwakwalwar ki ba sai kiyi aiki da zuciyarki? Ban shiga ran Baba ba Ruqayyah, bansan menene dalilin sa na fadar abinda ya fada ba amma nasan ba wai dan baya sonki bane ba sai don yana tsoron halinki, yana tsoron kar kije gidan kiyi ta musu halayyar ki azo aji kunya, kuma ni banga laifinsa ba" Ruqayyah ta fara ture ta tana kokarin mikewa tsaye tana kunkuni, Sumayya tace "ko me zaki ce sai dai kiyi ta cewa amma ni dai ba zan daina gaya miki gaskiya ba, kuma ina so ki sani, ko maza sun kare a duniya bazan auri Hassan ba dan haka kar ma ki saka wani abu a ranki, tunda Hassan ya nuna yana sonki to kuwa tabbas ya haramta a gareni. Amma in baki chanja hali ba zaki yi loosing dinsa, ko Baba bai hana shi ke ba shi da kansa zai gudu yace ya fasa"

Ruqayyah tayi hanyar kofa zata fita kuma sai ta tsaya, sai ta juyo tana kallon Sumayya tace "menene zai saka yace ya fasa?" Sumayya ta jawo ta ta dawo da ita zaune tace "halinki. Yadda na fahimce shi shi kamilar mace yake so mai kyawawan dabi'u, to in kina so ya aure ki sai kin zama mai wannan halin, abu mafi muhimmanci kuma sai kin cire son abinsa a zuciyarki, dan in dai ya fahimci kudinsa kike so bashi ba to kuwa zai gudu, ki nuna kudinsa bai dame ki ba, kinuna masa kina sonsa sosai, watakila ma kiga har kin fara son nasa da gaske"

Ruqayyah tace "waye yace miki bana sonsa yanzu" Sumayya tayi murmushi tace "ina fata. In ma kina sonshi to kinfi son dukiyarsa a kansa, ba Hassan kike so ba CEO na H and H kike so, ko ba haka bane ba?" Ruqayyah tace "shi din dai shine duk biyun, to menene abin damuwa a ciki?".

Sun jima suna hirar abin a tsakanin su, Sumayya tana ta bawa Ruqayyah shawarwari a ranta kuma tana fatan Hassan bai karbi tayin Baba ba saboda in ya karba dole zata yi wa Baba musu, dan ba zata iya auren Hassan din Ruqayyah ba. Ko da ace ita yace yana so zata iya barwa Ruqayyah shi dan a zauna lafiya. Ita farin cikin family dinta shine gaba da komai a gurinta.

A bangaren Ruqayyah kuwa hankalin ta ya kwanta sosai ta jin ikirarin Sumayya na cewa ba zata auri Hassan ba, kuma tasan indai Sumayya tace haka to Baba ba zai matsa mata ba. Sai kuma ta fara duba shawarwarin da Sumayya ta bata, ta kuma yarda lallai Hassan mace ta gari yake nema kuma indai ta nuna masa iri dabiun ta zai iya cewa ya fasa sai dai duk su biyun suyi asarar sa, ita kuma bata fatan wannan irin babbar asara ta same su. Ba dai mace ta gari yake so ba? To kuwa tabbas zai samu mace ta gari. Ita Ruqayyah ta kama shi a cikin faratan ta kuma ba zata taba releasing dinsa ba har sai burin ta ya cika, burinta na zama matar CEO of H and H.

Tagwayen sunyi ta jira suji Baba yayi musu magana akan abinda suka tattauna da Hassan amma bai ce musu komai ba, dan haka suka kasa tantancewa ko Hassan ya karbi tayin Baba ko kuma bai karba ba. Ruqayyah kuma tayi iyakacin kokarin ta na dannewa bata nuna wa Baba cewa taji tayin da yayi wa Hassan ba, sai dai a zuciyarta ta kuduri aniyar cewa zata tabbatar cewa watarana yayi nadama, wata rana sai yayi nadamar zaben Sumayya akan ta.

A bangaren Hassan kuwa fushi yake yi sosai da Hussain saboda halin ko in kula da yake nunawa akan Ruqayyah, rigima a tsakanin su har gaban Aunty "Aunty yaron nan wai yaje yaga yarinyar nan yayi mata godiya akan abinda tayi min amma yaki, kiri kiri yake nuna min kiyayyar sa akanta" Hussain yace "ni nace maka bana sonta? Ni nace maka ina kinta? Kawai hankali na ne bai kwanta da ita ba" Hassan yace "ta yaya to hankalin naka zai kwanta da ita idan baka je ka ganta ba? Ta yaya zaka yarda da ita in baka fahimce ta ba?" Hussain ya mike yace "alright, send me the address, zanje gobe mu gaisa shikenan?" Hassan yace "ba shikenan ba, sai kaje sannan maganar zata wuce".

Suka mike a tare suka fita suna cigaba da rigimar, aunty ta bisu da kallo sannan ta girgiza kanta, ita da aka zo gurinta da niyyar tayi Shari'a amma ba'a bar ta tace komai ba har aka gama shari'ar.

Bayan sun fita daga gurin Aunty dai suka ajiye maganar Ruqayyah suka koma hirar Company, dama batan Hassan ne ya tsayar da maganar amma yanzu tunda komai ya lafa zasu cigaba da shirye shiryen su. Hassan yace "already dama na riga nayi sanarwar wadanda aka yiwa interview su dawo a sake musu, tunda na rasa duk bayanan su a cikin mota ta data bata" Hussain ya daga kafada yace "shikenan, duk abinda kace haka za'ayi. Ina dai son mu gama daukan ma'aikata as early as possible saboda in samu in mayar da hankali na kan ginin gidan can da kuma sauran al'amuran biki" Hassan ya juya ya kalli side din da twin houses dinsu suke.

Gida ne Hussain ya siya ajikin gidansu, mai gidan ne Allah yayi masa rasuwa sai magada suka saka gidan a kasuwa shi kuma Hussain ya siya, katon gida ne na gaske, amma Hussain ya saka akazo akayi flat dashi, a lokacin sai da suka yi ta rigima da Hassan saboda shi yana ganin rashin dacewar hakan. "Wannan ai almubazzaranci ne" shi kuma Hussain yace "plan din mutum daya ne a gidan, ni kuma so nake muyi twin houses ni da kai yadda zamu zauna da iyalan mu seperately but together, sannan kuma ga Aunty a kusa damu".

Sai dai kuma ganin cewa da akwai sauran lokaci ya sa har yanzu bai mayar da hankali wajen kammala ginin ba saboda so yake yayi shi a nutse, using the very best of komai, dan Hussain baya karbar komai in ba best ba.

Hassan ya bude motar sa yana shiga, Hussain ya leko da kansa yace "zanje fa" Hassan ya haɗe rai yace "kar Allah yasa kaje ɗin".

Washegari Hussain ya shirya yaje. A kofar gidan da aka kwatanta masa da Google map ya tsaya yana karewa gidan kallo sannan ya juya yana karewa unguwar kallo, yana lura da yadda mutane yara da manya suke ta kallon motarsa. Ya dan sauke glass ya kira wani yaro wanda ya taho da gudu yana leka cikin motar. Hussain yace "ka shiga gidan nan kace wai ana kiran Hassana tayi bako" yaron ya girgiza kansa yace "babu Hassana a gidan" Hussain ya hade rai yace "babu Hassana kuma? Sai wa?" Yaron yace "akwai Sumayya akwai Ruqayyah" Hussain ya tabe baki yana sake kallon gidan, tabbas nan ne gidan ta yadda aka fasalta masa shi.

Yace "to kace ana kiran su duk su biyun" da sauri yaron ya shiga. Yana bude kofa kofar gidan suka kusa yin karo da Ruqayyah wadda taji alamar tsayuwar mota ta taho yin tsegumi, a ranta tana fatan Hassan ne ya dawo kuma gurinta yazo ba gurin Sumayya ba. Ta ja yaron gefe, "waye a waje?" ya wangale mata baki cikin murna yace "wani farin kyakkyawan saurayi ne yake kiran ku ke da Sumayya" ta bata fuska cikin mamaki "fari kuma? Baki dai ko? Ko baka gani sosai ba?" Yaron ya girgiza kansa yace "fari ne wallahi, tas ma kuwa"

Ta juya tana kallon dakin da Inna Ade take ciki sannan ta leka ta tsakanin kofa, ba irin motar ranar nan bace wadda Hassan yazo da ita, wannan ta ci uban waccan, ita bata taba ganin irin wannan motar ba ma. Ta koma da baya tana dafe kirjinta. Waye wannan kuma? Ko Hassan ne yayo mata aike a daya daga cikin motocin sa? Ko motar ya aiko mata da ita kyauta?

Muryar Inna Ade taji daga bayanta, "me kike yi a gurin nan Ruqayyah?" Ta dan tsorata kadan sai kuma ta saki fuskarta. "Wai wani ne yake kiran mu ni da Sumayya" Inna Ade tace "kuma shine kike leka shi" ta juya gurin yaron tace "kaje kace waye" yaron ya fita ya tambayi Hussain, ya danyi tsaki yana kallon agogon hannun sa yace "kace hussainin Hassan ne" yaron ya koma ya fada.

Ruqayyah ta dan bata rai. Me yasa shi Hassan ɗin ba zai zo ba sai ya bawa Hussain motarsa ta taho? Ko dai ya karbi shawarar Baba, ko kuma har yanzu yana tunani ne akan shawarar. Inna tace "ku saka hijaban ku ku je, zuwa yayi ku gaisa" sai ta dauki kudi a cikin kuɗin da Hassan ya ajiye musu shekaran jiya ta bawa yaron tace yaje ya siyo lemo guda daya da ruwan roba guda daya.

A tare suka fita, ya bi su da kallo yana studying dinsu har suka zo gaban motar suka tsaya sannan ya sauke glass din. Sumayya tayi masa murmushi, sai ya mayar mata kuma yaji bai kamata suna tsaye a waje shi kuma ya zauna a mota ba. Ya bude motar ya fito. Wani irin lugude zuciyar Ruqayyah take yi. What? Wannan ai yafi Hassan dinta haduwa, ya akayi dan uwansa ya fishi haduwa?

Ta sauke idonta kasa tana tuno karin maganar hausawa da suke cewa ba haka aka so ba kanin miji yafi miji kyau.

Sumayya ce ta fara gaishe shi sannan Ruqayyah ita ma ta gaishe shi. Ya amsa yana rarraba ido a tsakanin su. Yace "wacce ce yayar tawa a ciki?" Sumayya tace "ka chanka" ya kalle ta ya kalli Ruqayyah da idonta yake kasa yace "hmmm. Hassan yace min hassanar sa tafi yaruwarta komai, hankali, nutsuwa, kyau, bla bla bla. Jiya haka ya kwana yana min sambatu duk ya hana ni bacci shi yasa nace yau dai sai nazo naga wannan Hassana na huta, kuma from all indications..." Ya nuna Ruqayyah "ke ce Hassanar" Ruqayyah taji sanyi a ranta, wato Hassan bai chanja ra'ayin sa ba, Baba bai yi convincing dinsa ba.

Sumayya tayi dariya tace "son kai yake yi fa da yace ta fini komai" Hussain yace "na yarda dake, ta dai fiki sunkuyar da kai. Kin fita fara'a kuma daga alama zaki fita son mutane" ya fada cikin sigar tsokana, Ruqayyah ta danyi murmushi tana wasa da bakin jihab dinta sannan tace "na gane niyyar ku, so kuke ku hade min kai dan kunga baya nan ballantana ya tare min" Hussain yace "ohhh ashe kina magana. Ni na dauka ai mu biyu zamuyi hirar mu ban da ke"

Yace "to Malama Hassana, nazo ne......." Ruqayyah ta katse shi "Ruqayyah" yace "what?" Tace "Ruqayyah shine sunan" yace "ohh, ni kuma Hassana ake ta gaya min a kunnuwa na" tace "wannan shi kadai yake fada ai. Special" yayi dariya sosai yana bayyana dimple dinsa, Sumayya ma ta taya shi dariyar tana cewa "Ruqayyah yaushe kika kile har haka?" Hussain yace "wallahi Hassan ya taro match. Kuma kamar kin fada a kunnuwan sa" ta dan rufe fuska alamun kunya "kar ka gaya masa dan Allah".

Yace "kinsan me? Naga alamar kamar zaku daidaita da Gimbiya ta, Fatima sunanta, ita ce wadda zan aura. Tunda taji labarin ki take addu'ar ku daidaita da Hassan


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login