Showing 18001 words to 21000 words out of 300844 words
dai ya dana jin dadin rayuwa ko yaya ne, bai zo a bati ya koma a alakoro ba" duk suka juya suna kallonta
A ranar da daddare sai Inna Ade ta samu kanta da saka Hassan a cikin addu'ar ta duk kuwa da cewa bata san shi ba amma tayi masa adduoi sosai da fatan alkhairi duniya da lahira.
A gidan Aunty ma daren ranar basu yi bacci ba, gabaki daya suka hadu a bedroom din aunty suna kai wa ubangiji kukansu. Daga mai sallah sai mai karatu sai mai zikiri a haka har assuba da cimmusu, suka yi sallar assuba sannan suka zauna Aunty tana jero Adduoi su kuma suna amsa mata da ameen har ta gama suka shafa. Suna shafawa ana turo kofar dakin da sauri, suka waiga kusan a tare suna kallonsa kamar yadda yake binsu shima da kallo daya bayan daya yana haki tamkar wanda ya taho a guje tun daga China. Aunty ta mike "Hussain?" Yace "Aunty kidnappers ne suka dauki Hassan, sun kira ni da wayarsa sun kuma turo min hotonsa a daddaure, kudi suke nema, 1billion naira suke nema".
Episode eight : Kidnapped
Hasken da ya shigo ta window ne ya sauka a dai dai fuskarsa. Ya kikkifta idon sannan yayi kokarin amfani da hannunsa gurin tare hasken amma sai yaji ya kasa motsa hannun nasa. Wani irin ciwo jikinsa yake yi masa tamkar wanda aka kwana ana duka da ƙulki. Ya bude idonsa da kyar, su kansu eyelids dinsa sunyi masa nauri kamar an dora wani abu akan su. Idonsa ya sauka akan window din da take kallonsa ta inda hasken ranar yake shigowa. Ya sake rufe idon da sauri saboda hasken daya kashe masa ido amma already yaga tagar kuma a ransa ya fahimci cewa bai san ta ba. A ina yake? Ya sake kokarin motsa hannunsa amma yaji ya kasa, wannan ya tabbatar masa da cewa hannayen sa a daddaure suke sannan ya fahimci ƙafafuwan sa ma haka. Bakinsa ma a like yake ta hancin sa kawai yake numfashi. Ya juya fuskarsa gefe sannan ya bude idonsa yana numfashi sama sama cikin tsoro, a hankali ya zagaye gurin da yake da idanunsa sannan ya fahimci cewa toilet ne, ya kuma fahimci shi kadai ne a gurin. Sai a lokacin tunanin abinda ya faru dashi ya dawo masa.
Farkon abinda ya fara fahimta shine har ya kwana ya hantse kenan, tashin hankalin sa shine wanne hali yan'uwansa suke ciki? Wanne hali Hussain yake ciki? Shin kidnappers din sunyi contacting dinsu ko kuwa? Abu na biyu daya tuna kuma shine bai yi Sallah ba, bai yi magrib ba bai yi isha ba baiyi assuba ba.
Ya ja ƙafafuwan sa ya lankwasa su yana jin tamkar zasu karye saboda sandarewa da suka yi ga kuma azabar ciwo da suke yi masa, ya yi kokari ya jingina bayansa da jikin bango sannan yabi bangon ya mike zaune yana jin jikinsa gabaki daya yana amsawa saboda ciwo, ciwon tafiyar da akayi dashi a booth din mota, daure shin da akayi for hours da kuma kwana da yayi akan tantagaryar sumunti. Ya sake karewa ban dakin kallo yaga bashi da wani girma sosai daga kofar da take a rufe sai yar karamar tagar da take can sama a rufe itama da glass. Kasa kasa yake jin muryoyin mutane yana shigowa ta kofar.
Ya muskuta a hankali har yaje jikin kofar sannan ya jingina jikinsa da kofar ya kasa kunnen sa yana so yaji abinda suke cewa amma har kansa ya fara ciwo saboda stressing kunnensa da yayi bai samu ya fahimci komai a maganganun nasu ba saboda can kasa suke maganar. Ya fara buga kansa a jikin kofar, yana jin kan yana kara yi masa ciwo amma yana so yayi calling attention din wadanda suke waje in mutanen kirki ne su taimaka masa in kuma holders dinsa ne ya nemi su kunce shi yayi sallah. Sukayi shiru da maganganun su a lokaci daya sannan suka taho bakin kofar da sauri suna gyara abinda suka rufe fuskokinsu dashi. Katon ne ya bude kofar da sauri yana auna Hassan da bakin bindigar da take hannunsa "Will you stop banging that door?" Ya fada murya can kasa kamar me rada. Hassan ya fara kokarin magana amma sai ya kasa saboda bakinsa yana rufe. Mutumin ya saka hannu daya ya cire abin bakin Hassan, Hassan yaji tamkar ya cire ne tare da fatar bakin gabaki daya saboda zafin da yaji amma babu hannun shafawa dan haka kawai ya runtse idonsa har zafin ya lafa, sannan yace "ina son zanyi Sallah dan Allah" mutumin ya sunkuyo fuskanta kusa data Hassan yace "kaga nayi kama da mai yin Sallah? Reserve your sallah kayi ta addu'a twin dinka ya biya mu kudin da muka nema and you will be out of here kaje kayi ta sallolinka".
Dayan ya matso yana turawa Hussain robar abinci data ruwa gasansa, ya kunce masa daurin hannunsa sannan yaja baya, mai bindigar yace cikin gurbatacciyar hausarsa "mu na nan a bakin kofa, if you dare try to make any sound I will fill your brain with bullets" and Hassan knows he means it.
Sai da suka rufe kofar sannan ya dauke ganinsa daga kansu ya mayar kan hannunsa yana shashshafa shi, bringing back blood, sai da yaji hannun ya danyi masa dama dama sannan ya jawo kafarsa yana noticing yadda ta kumbura ya fara kokarin kunce ta, da kyar ya iya kuncewa saboda karfin daurin da suka yi masa da kuma kumburin da kafar tayi. Ya jawo ta yana shashshafa ta sannan yayi kokarin mikewa yayi alwala da ruwan da suka bashi, bai san inane gabas ba kuma ko ya tambaya ba zasu gaya masa ba dan haka sai ya zabi guri ɗaya yayi niyya ya tayar da sallah sa, saboda shi addini mai sauki ne, ubangiji masani ne kuma mai rahama ne.
Bayan ya idar, yayi dogayen adduoi sannan ya zauna ya runtse idanunsa yana kokarin tuno yana yin da ya hango cikin dakin da mutanen suke. Dakin bashi da girma kuma da alama ba'a kammala shi ba dan jikin bangon babu penti kuma tagogin babu frames. Yayi assessing yadda yaga situation din, mutane biyu ya gani amma yasan su uku suka dauko shi, ina dayan? Ya tuno da muryar da yaji a mota, muryar da yaji kamar ya sani. Shin mai muryar ne baya nan? Ya tuna da yadda yaga suna magana cikin rada, da kuma yadda suka buga masa warning din kar yayi making sound, hakan yana nufin cewa a cikin gari suke, a cikin mutane suke. Ya kalli window din da take saman toilet din, glass ne, yana fasawa zasu ji kara kuma kafin ya gudu zasu harbe shi, dan babu imani sam sam a cikin idanun wannan katon.
Yayi ajiyar zuciya ya jingina kansa da jikin bango yana shafa fuskarsa yana jiyo maganagun su kasa kasa a cikin dakin, his only option is to wait har Hussain ya basu abinda suke so su sake shi. Ba shi da ko digon kokwanto cewa Hussain zai biya kudin, ko da kuwa zasu nemi dukkan abinda ya mallaka zai basu, ko da zasu nemi ya bada kansa zai basu, ko da wani aka kama ba shi ba Hussain zai iya biyan kudin ransom ya ceto mutum. Shi mutum ne da dukiyarsa sam bata dame shi ba.
Hassan ya yanke shawarar zai jira, yasan jiran ba zai yi masa dadi ba amma bashi da wani option than that. Zai jira har sai Hussain ya biya kudin sannan su sallame shi ya koma gida sannan kuma ya yanke shawarar yana komawa gida zai yi aure.
Five days later...............
Tunda Hussain ya dawo Nigeria yake jiran barayin Hassan su sake kiransa amma shiru, ba kira babu message babu komai, shima kuma in ya kira number din Hassan din bata tafiya. Hankalin sa in yayi dubu ya tashi kuma commissioner of police ya gaya masa abinda suke so kenan, so suke su gama tsorata shi yadda duk abinda suka ce yayi zaiyi.
Hussain ya girgiza kansa yace "then they don't know me as they claimed they do. I will give up anything for Hassan. One billion naira suka ce masa suna so in dollar bills kuma gata nan na hada na zuba a irin jakar da suka ce in zuba su kawai naje jira su gayamin yadda zanyi da ita" ya karasa maganar yana mikewa yana zagaye dakin. Haka yake tun sanda ya dawo daga China, baya taba zama na minti biyar a guri daya zai mike kamar wanda ake mintsinin sa, fuskarsa tayi baki, idonsa yayi ja kuma ya fada ciki saboda rashin cin abinci, rashin bacci da kuma rashin kwanciyar hankali.
A ranar da aka sace Hassan, Hussain Yana sauka a Beijing ya kira Hassan da niyyar ya gaya masa ya sauka, a lokacin kidnappers din suka dauka kuma direct suka gaya masa cewa yana hannunsu, suka bashi umarnin ya dawo Nigeria sannan suka gaya masa adadin kudin da suke bukata. Sai kuma suka turo masa hoto, hoton Hassan a daddaure a yashe a bandaki, hoton da har yau shine yake yawo a kwakwalwar Hussain, shine yake hana shi bacci.
Ranar da ya dawo Nigeria gidan su ya cika da police da yanuwansu na Gombe da sauran abokan arziki da abokan aiki, kusan duk uncles dinsu da aunties da cousins dinsu sun zo. Yana shiga gidan zai gansu duk a zazzaune da charbi suna ja kamar gidan makoki, sai gidan yake nuna masa kamar Hassan ya mutu ne, sai yake tunawa da mutuwar Abban su.
Wannan ya saka ya tattara kayansa ya bar gidan ya kama daki a hotel duk kuwa da nuna wa da Aunty tayi cewa bata yarda da hakan ba, tana jin tsoron kar wani abu shima ya same shi. A hotel din ne commissioner of police ya same shi kuma ya hada shi da SS dan suke tsaron lafiyar sa "bamu san menene nufin su na yin shiru haka ba, maybe tarko suka dana, maybe kai suke nema mistakingly suka kama Hassan".
Bayan kwana biyar da kama Hassan ne kidnappers din suka sake contacting Hussain da wayar Hassan din. Message suka tura masa
"Kana so ka sake ganin twin dinka? Ka cire police daga gidan ka sannan su daina zuwa hotel din da kake zaune, SS din da suke gadin ka ma ka sallame su idan ba haka ba zamu dawo maka da Hassan, but in PIECES"
Ya ajiye wayar a gefe ya mike ya fara pacing dakin da yake ciki yana yarfar da hannayen da, sai kuma ya shiga toilet ya yo alwala ya dawo ya gaya wa Allah sannan ya dauki wayar sa yayi wa commissioner forwarding message din na su. Jima wa kadan kira ya shigo daga commissioner din ya dauka baice komai ba. Commissioner yace "barazana ce suke yi maka kar hankalin ka ya tashi ba zasu iya yi masa komai ba tunda suna bukatar kudin ka" Hussain ya lumshe idonsa ya bude, he is not going to take that risk, yace "ku janye mutanen ku. I will do this thing alone, zan iya" commissioner yayi ajiyar zuciya yace "I understand, zamu matsa, but Please keep us updated, daga an karbe shi kuma zamu yi moving in mu kama su mu dawo maka da kudin ka" Hussain yace "alright. Nagode" ya ajiye wayar tare da saka hannayen sa ya rufe fuskarsa.
A lokacin wayar Gimbiya Fatima ta shigo, she had been very supportive dan sau biyu tana zuwa Kaduna gurin sa tare da brother dinta. Mai martaba ma ya aiko takanas anyi masa jaje kuma yayi alƙawarin saka Hassan a cikin adduoin sa da kuma umartar malamai suyi ta addu'a akan lamarin. Ya dauka wayar ya gaya mata duk halin da ake ciki. Cikin shigar lallashi tayi ta bashi baki tare da bashi shawarwari har sai da taji alamun ya dan daidaita sannan suka yi sallama.
Dare yana yi yabi shawarar da Gimbiya ta bashi, ya kira Salisu ya taya shi hada kayansa sannan ya zame jikinsa ya bar hotel din ba tare da sanin kowa ba, ya koma wani hotel din ya saka Salisu yayi masa reserving daki secrectly ya shiga yayi zamansa.
Washegari da safe wani message din ya shigo.
"Ka dauki kudin, da karfe goma sha biyu na dare ka saka a back seat din motarka ka fita kai kadai, make sure police basu bi ka ba, kaje kofar companyn ka, inda muka dauki Hassan kayi packing motar daga gefen katanga ka bar key a jiki ka fita ka hau babur ka koma gida. Ko Aunty ka gaya wa zamu sani"
Ya karanta sannan ya ajiye wayar, a ransa yana noticing yadda suka ambaci Aunty da sunan Aunty.
Sai ya dauki wayar yayi musu reply
"Then how do I get my brother?"
Suka amsa
"Zai dawo gida da ƙafafuwan sa, that's in kayi abinda mukace, if not, zaka tsince shi somewhere"
Hussain bai kira commissioner ba kuma bai yi niyyar kira ba. Da magrib ya fita shi kadai a mota ya koma gidan su, an tafi masallaci dan haka mai gadi ne kadai yaga shigarsa shima kuma ya gaya masa kar ya gaya wa kowa yazo. A dakinsa bayan yayi sallah ya bude safe box dinsa ya dauko jakar da ya zuba kudin ya sake kirgasu ya tabbatar sun cika sannan ya ajiye ya kwanta akan gado ya rufe idonsa.
Sai karfe goma ya tashi yayi wanka yayi sallar ishai sannan ya zauna yana kallon agogo yana ticking har ya sauka kan 12 sannan ya mike ya dauki jakar ya fita. Babu wanda ya ganshi sai salisu sai kuma mai gadi. Ya dauki hanya har zuwa inda suka gaya masa yayi packing ya tabbatar babu wanda yake ganinsa sannan ya fita ya danyi tafiya a kasa sannan ya tari babur ya hau ya koma gida, yana sauka sako yazo masa "very good boy, aikin ka yayi kyau. Ka zauna ka jira zuwan danuwanka".
Ya mayar da wayar cikin aljihun sa ya shiga gida ya zarce Bedroom dinsa ya sake wanka ya zabi kaya masu kyau ya saka, ya saka hula, agogo, socks da takalmi ya fesa turare ya dawo palor ya zauna, idanunsa akan kofa, waiting......
Ga masu son siya zasu iya turo kudinsu ₦300 ta account
GT Bank
Account Name : Nafisa Usman Tafida
Account Number : 0139433741
Sai su turo shaidar transaction din ta hanyar WhatsApp zuwa wannan layin
08067081020
Wadanda basu da account zasu turo katin MTN na ₦300 zuwa wannan layin
08067081020.
Dan girman Allah banda kira, WhatsApp only
Episode Nine : Gun shots
Kwanakin nan guda bakwai sune one of the worst kwanaki da Hassan ya taba gani a rayuwarsa. Sau daya suke bashi abinci ruwa ma sau daya, sunce in yaci ya koshi zai iya kokarin playing hero. Ruwan da suke bashi kuma shi yake cancanawa yayi alwala dashi saboda bashi da ruwan alwala, wanda ya rage kawai shine wanda yake sha sai gobe kuma. Wanka kuwa tunda yazo jikinsa bai ganshi ba, shi lanshi yasan jikinsa warin datti yake yi dana gumi, saboda toilet din da yake rufe a ciki babu hanyar iska sai ta cracks din kofa.
Addu'a ita Hassan ya rike a ransa, Alqur'ani kuma shine abokin hirarsa, shi yake debe masa kewa tunda bashi da wanda yake magana dashi sai dai in sun shigo sau daya, in suka shigo ɗin kuma babu magana a tsakanin su sai tsoratarwa a kan in yayi trying wani abu, suna kuma lissafa masa abubuwan da zasuyi masa idan har dan uwansa bai basu kuɗin da suke nema a gunsa ba.
Sannan ga kafar sa guda daya da take damunsa, har yanzu a kunbure take, yana tunanin wani kashin ya samu matsala wanda yake bukatar attention din likita, da yayi musu complain sai suka yi dariya suka ce "you won't be needing the leg in bamu samu kudin mu ba, so worry about our money not your leg".
A ranar da ya cika kwana bakwai ne suka yi masa albishir da cewa "yau zamu karbi kudin twin dinka, yau zaka tafi gida one way or another, in yayi abinda muka ce zaka tafi gida da ƙafafuwan ka in kuma bai yi ba........." Suka kwashe da dariya. Tun lokacin hankalin sa yake tashe, yasan halin Hussain sarai yasan zai bayar da kudin amma kuma yana da kankanba, yana da taurin kai kuma bai fiya bin umarni ba koda kuwa umarnin daga Aunty ya fito balle daga wadansu garorin unguwa, but since his life is at stake maybe, just maybe, zai zama careful for once.
Magrib tayi, yayi sallah, yaji ana kiran ishai itama ya tashi yayi sannan ya zauna ya mike kafar sa yana kallon guri daya, waiting..........
Wadannan sune awannin mafi ya tsaho da Hassan ya gani a rayuwarsa, gashi babu agogo balle ya duba yaga lokaci, a zaune kawai yake yana sakawa yana warwarewa. Mutum daya daga cikin kidnappers din yana lekowa gurinsa yayi reminding dinsa cewa yana nan fa, kar yaji shiru ya dauka babu kowa, sai Hassan ya fahimci cewa shi kadai ne maybe sauran sun tafi karbar kudin ne, sai yaji yana jin tsoron kar suyiwa Hussain wani abu.
After the long hours yaji tsayuwar mota a gaban gidan, jikinsa ya bashi cewa this is it. Yaji maganganun su a dakin suna magana kasa kasa da dariya. Sai yaji yana son jin maganar da suke yi, Allah yasa ba wani abin suka yiwa Hussain ba, ya mike tsaye jikinsa babu isasshen karfi yaje bakin kofar ya jingina kunnen sa yana son jin abinda suke tattaunawa akai. And then something happened...........
Jinginar da yayi a jikin kofar ya saka kofar ta bude da kanta, ashe wanda ya shigo dazu ya manta baiyi locking dinta ba, sai kawai ga Hassan ya fado cikin dakin kamar an jefo shi, ya fado tsakiyar kidnappers din, gaban jakar kudin da suke budewa fuskokin su cike da farin ciki da murnar cikar burinsu na shiga layin masu kudi. Farko tsorata sukayi duk suka mimmike kamar yadda shima ya tsorata, sai kuma tsoron fuskarsu ya rikide zuwa wani rikitaccen yanayi yayin da nashi tsoron ya koma mamakin abinda idanunsa suka gani a gurin.
"Salisu?" Ya fada da wata irin murya, "me kake yi a gurin nan? Ko kai Hussain