Showing 51001 words to 54000 words out of 300844 words
kuma suna yin iyakacin kokarin su. Allah shi ya barwa kansa sanin yadda zaiyi da Ruqayyah.
Da safe yaran suka zagaye uban. "Baba ba ka ga gidan ba, bandakin fa irin wanda ake korawa da ruwa ne" "kaga kujerun Baba? Wannan in inna ta zauna ba zata iya tashi ba" Sumayya ta fada tana tsokanar Inna, Inna ta harare ta tace "ai dai kinsan ba daga ruga aka dauko ni ba ko? Sai dai ki fada wa zazzagawa sune basu saba hawa manyan kujeru ba" Baba yayi shiru bai kula ta ba duk da ya fahimci tsokanar sa take yi, shi wannan lamari da yaran nan suka kawo masa yana da girma sosai, gida kuma? Har da dakuna kowa da nasa? Da bandakuna na zamani da palo mai kujeru da talabijin? Anya kuwa abinda yaron nan yake yi bai yi yawa ba? Anya kuwa ya dace ya karbi wannan kyautar? In ma zai karba ai kamata yayi ace sai bayan biki tukunna sai ya iya karba a matsayin surikin sa amma yanzu gani yake yi anytime yaron zai iya zuwa yace ya fasa auren. Inna tace "Baban biyu, nima gaskiya ina tsoron karɓar gidan nan, daga yadda suke kwatanta shi kasan ba karamin gida bane ba. Ya bar mu anan din mu tunda gashi nan har kana kokarin yin katangar nan" yace "har plaster nake so ayi wa dakunan nan ayi musu penti kafin bikin" yaran duk suka fara bata rai "dan Allah Baba, dan Allah Inna yace fa da sunan ka ya sayi gidan nan, kyauta ya baka shi, bana jin ko ba'a yi auren ba zai dawo da kalaman sa baya" Sumayya tace tana karya wuya. Sulaiman da Zunnur suka durkusa kusa da ita suna hade hannayensu "dan Allah Baba ka karba, dan Allah Baba ka karba".
Baba yayi shiru yana kallon su yana tunani sannan yace "shikenan ki ce wa Hassana ta kira min shi tace in ya samu dama yau da magariba yazo ina son magana dashi..
Sakon yana zuwa kunnuwan Hassan ya gane cewa akan maganar gida ne, ya shirya ya taho yana addu'ar Allah yasa ba rejecting gidan Baba zai yi ba. A tsakar gida aka shimfida musu tabarma suka zauna daga can bakin kofar shigowa. Hassan ya gaishe shi cikin ladabi da jin kunya, Baba ya amsa sannan yace "jiya yara suka zo min da wani lamari mai girma, shine na kira ka inji daga bakin ka" Hassan yace "gaskiya ne abinda suka fada baba, ina kuma fatan ba za'a ki karba ba kamar yadda aka ki karbar kuduri na na bada jarin sana'a, yadda na hakura na bayar da aiki ina fatan wannan karan nima za'a dube ni a karbi wannan din. In ba'a karba ba gaskiya zanji babu dadi, zanga kamar......" Baba yace "kamar an raina?" Hassan yace "a'a kamar ba'a sona tunda ba'a son abin hannuna" Baba yace "ba haka bane ba, son naka da nake shi yasa nake maka haka. Bana son in cutar da kai" Hassan yace "ta yaya zaka cutar dani Baba? Karbar wannan kyautar ai faranta min zaiyi ba bakanta min ba" Baba yace "haka ne, amma ina matukar jin kunyarka" Hassan yace "Allah yasa hakan yana nufin za'a karba" Baba yayi ajjiyar zuciya yace "na karba Hassan. Allahu yayi maka albarka ya baka masu yi maka kaima a lokacin da kake bukata" Hassan ya sunkuyar da kansa, fuskarsa tana nuna irin jin dadin da yayi yace "Nagode sosai Baba, na gode da karamcin ka da soyayyar ka" Baba ya dago kai yana kallon sa, yaron kirki ne, sam bai dace da Ruqayyah ba, sai yaji kamar baiyi masa adalci ba.
Hassan da kansa ya turo da driver ya debe su zuwa sabon gidan su. Kafin su tafi duk suka shiga gidajen unguwa suka yi musu sallama tare da basu kwatancen sabon gidan su. Kayan sakawarsu kawai suka dauka da dan abinda suka san zasu bukata a sabon gidan sannan suka rufe dakunan su suka rufe gidan suka tafi, zuciyoyin su fal da mabanbantan feelings.
Yaran suna jin feeling na murna sosai, suna ganin sun taka wani babban matsayi a rayuwa kuma suna ganin wannan wani chanji ne mai kyau a rayuwarsu yayin da iyayen suke jin rashin dadi na barin gidan da suka yi shekara da shekaru suna zaune a ciki, suna kuma alhinin shiga wata sabuwar rayuwa wadda basu san menene a boye a cikin ta ba.
Ruqayyah kuwa a nata bangaren, ji take yi cewa wannan chanjin kamar misalin wanda zaije sama ne sai ya taka dutse, wannan ba komai bane a gurin ta, wani step ne da ta taka zuwa gaba.
Wannan kenan...........
A bangaren Gimbiya Fatima kuwa shirye shirye sun kankama sosai, a da lokacin da aka saka bikinta wata takwas ji tayi kamar ta dora hannu aka tayi kuka saboda ganin tsayin lokacin da kuma zakuwar da tayi na ganin ta kasance da hasken idanunta, Hussain. Sai gashi yanzu har watan bikin ya kama. Tana ta shirye shiryen ta iyayenta suma suna yin nasu. Duk tsarin gidan Hussain babu abinda bata sani ba dan tare suka tsara kayan su, sun kuma shirya duk events din da zasu yi. Ita a bangaren ta zata yi bridal shower a gidan babban yayan su a nan cikin garin kano, sai kuma kamu da yini da za'a yi rana daya anan cikin palace ranar Friday, ranar Saturday kuma za'a yi grand dinner da maimartaba ne da kansa ya shirya musu kuma har da ango da abokan sa da yanuwansa duk za'ayi. Ana saka ran zasu zo su wuni ranar Saturday din da daddare ayi dinner sannan su kwana sai da safe a daura aure su tafi da amaryar su zuwa Kaduna.
Duk wasu ashobis sun fitar uta da kawayenta wadanda yawancin su tare suka yi jami'a a Europe, sai wadanda suka yi secondary school tare a Abuja, sai kuma family friends dinta. Sun gama tsara komai kuma Hussain ya sakar musu kudi wanda wani lokacin har sai ta daga masa hannu dan bata son kawayen natakuma su mayar dashi saniyar tatsa dan shi duk abinda suka ce ya basu basu kawai yake yi. An aika an gano gida kuma kusan komai an gama siya jira kawai akeyi bikin ya kara matsowa sai aje ayi jere.
Sakamakon binciken da Hassan ya tura ayi masa a kano a kan Adam ya fito, kuma kusan komai yayi tallying da abinda ya fada banda abu daya. Hassan ya dago da kansa daga karatun report din yana shafa sajensa, fuskarsa da alamar damuwa. Ya dauko form din daya cike biography din Adam yana kuma dubawa dan yayi confirming maganar, sai kuma ya dauko wayarsa ya saka number din da Adam din ya bashi ya kira.
Adam ya ciko mota passengers yana tukin sa a nutse kamar kullum, yaji vibration din yawarsa da take ajjiye akan dash board, ya kalle ta, sunan daya gani ne ya saka shi daga kafarsa yana kara rage gudun motar sannan ya sauka gefen titi yayi packing yana cewa "excuse me Please, I have to answer this" sannan ya daga wayar da sallama.
Hassan yayi mamakin sallamar da yaji amma sai ya maze yace "kazo gobe, around noon ina son ganinka" Adam yace "yes sir. Insha Allah" Hassan ya katse wayar still yana noticing insha Allah din da Adam yace.
A ranar da daddare Hassan yaje zance gurin Ruqayyah, suna zaune a dakin su Sulaiman kamar yadda suke zama kullum. Tana ta so ta shigar masa da maganar shirin biki amma ta rasa ta yadda zata fara ba tare data bata pentin da tayi wa kanta a gurin sa ba. Sumayya ta shigo da sallama ta zauna a hannun kujerar da Ruqayyah take zaune, ta gaishe da Hassan ya amsa yana tsokanar ta. "Ance min kina ta kuka wai ba kya son rabuwa da friends dinki" tayi ajjiyar zuciya, ita duk ba wannan ne problem dinta ba, ba shine abinda yake hana ta bacci tunda suka dawo ba.
Tace "yaya Hassan, dama tambayarka zanyi......." Ya gyara zama yace "ina jinki" tace "yaje kuwa? Yaje office din naka kuwa?" Ruqayyah ta juyo tana kallon ta tace "wa? Waye zaije gurinsa?" Sumayya ta dauke kanta daga kallon ta ta sake mayarwa kansa tana jiran amsa, ya danyi murmushi duk da ya fahimci wa da take nufi amma sai yace "wa kenan fa?" Ta dan vata fuska tace "mutumin ranar nan" ko da wasa bata son Ruqayyah ta san maganar Adam.
Ruqayyah ta sake cewa "wai waye kike magana akan sa? Bashi da suna ne?" Sumayya tace "shi yasan maganar wanda nake yi ai" Hassan yayi yar dariya, ya fahimci Sumayya tana boyewa Ruqayyah wannan Igbon. Ya gyara zama da dariya a Muryar sa yace "yes, na gane wanda kike nufi, and yes, yaje munyi magan dashi" cikin zakuwa Sumayya tace "and?" Yace "and, sai gobe zai dawo mu karasa maganar" Sumayya tayi ajjiyar zuciya tace "okay, thank you. At least nasan yaje din, ina ta tunani ne kuma bani da hanyar sani shi yasa na tambaya" yace "kar ki damu. I have his phone number if you want" Sumayya tayi saurin miko wayarta da Baba ya dawo mata da ita bayan sun dawo sabon gidan tace "yauwa saka min Please" yana dariya yace "ko kunya babu" ya karba yana saka mata Ruqayyah tayi mata alamar tambaya da hannunta ita kuma sai ta dauke kai kamar bata gane me take nufi ba, ta san dai yau sai sunyi rigima a daki".
Yana gama sakawa ya miko mata, tayi saving sannan tayi masa godiya ta fita, Ruqayyah ta jiyo tana kallon sa da alamar tambaya sai yace mata "wani aboki na ne". Daga nan bata iya ce masa komai ba duk da bata yadda da amsar daya bata ba.
Sumayya direct dakin da yake matsayin nasu ita da Ruqayyah ta zarce, ta rufe kofa sannan ta zauna a bakin dago ta kira number din da aka saka mata. Ring biyu ya dauka da sallama kuma a take ta gane muryarsa. Yace "who is on the line please" sai data dan jima sannan tace "someone, da ka manta" ko a cikin mafarki ne zai gane muryarta. Ya matsa daga gurin da abokan su suke hira yana cewa "Sumayya? Ke ce da gaske? A ina kika samu number ta?" Bata bashi amsa ba sai kuma yake "ohhh I get it. Yazo zance....." Ya fada da dariya a muryarsa.
Ta dan bata fuska tace "ni da na damu da inji yadda kake ai na ajiye kunya ta a gefe na nemi number dinka" yace "oh dear , you have no idea sau nawa nake zuwa unguwarku a rana. Sumayya kullum sai naje, kawai dai na kasa samun courage din da zan aika a kira ki tunda ranar nan kince min za'a yi miki fada, bana so ayi miki fada, bana so in jawo miki trouble. In naje kawai hoping nake ko zan ganki an aike ki ko kin fito unguwa"
Ta lumshe idonta tace "ni ba'a aike na, ni babu inda nake zuwa, sai in kwana biyu ban fita daga gida ba, dama zuwa school ne kuma yanzu bama zuwa, islamiyya ma a gida muke yi anan muke daukan karatu kuma mu dora wa yaran unguwa karatu" yace "wow, har karatu kuke koyarwa?" Tace "gidan mu ai makaranta ce, makarantar addini ce" sai taji yayi shiru har sai da tace "hello?" A hankali yace "zan iya shiga nima? Makarantar gidan ku zan iya shiga?" Tace "ban gane ba, ba ka yi sauka ba ko akwai littattafan da kake son sani?" Sai da ya danyi shiru sannan yace "banyi karatu ba ni. Bani da ilimin addini ni"
Overlook the typos please.
Wannan littafin na siyarwa ne, in kina so kiyi min magana ta wannan layin. 08067081020
Nineteen: The Real Princess
An kusa zuwa dai dai gurin. Lol
Jin tayi shiru bata ce komai ba ya saka yayi saurin chanza topic din. "Ina son ganinki sosai Sumayya, amma ban san yadda za'a yi in ganki ba. Ko kina da shawara?" Ta girgiza kanta tana kokarin kawar da shock din waccan maganar tace "bama gidan da ka sani yanzu mun tashi" ya ce "what? Kina nufin duk zaryar dana ringa yi da karawa wuyana tsaho ko zan hango ki a banza nayi ta kenan?" Tayi dariya shima yayi sannan tace "mun tashi daga unguwar" yace "to ina kuka koma?" Tace "naji Hassan yace gobe zaku hadu dashi, ka tambaye shi sai ya baka full address din, ni am not familiar with unguwar har yanzu dan haka ba zan iya yi maka kwatance ba" yace "wannan mutumin? A gurinku ne fa ku yammata yake sakin fuska har da dariya. Da naje office dinsa har na fito banga hakorinsa ba" Sumayya ta sake dariya tace "haba dai, yana da kirki fa sosai. Shi ya siya mana sabon gidan nan da muka dawo" Adam ya taya ta murna sannan ya bata labarin yadda suka yi da Hassan a office dinsa ranar nan, sannan ya kara da cewa "yace gobe inje in same shi. Maybe ya gama binciken nasa ne zan je inji result. Pray for me please"
Tayi masa alkawarin addu'a da kuma fatan alkhairi, a ransa yana so ya tambaye ta game da hadin Ruqayyah da Hassan da har zai siya musu gida amma sai yaji kamar yin haka zai zama stepping on the boundary tunda dai ba abinda ya shafe shi bane ba. Sun jima suna hira, yana ta bata labarin yadda yake zuwa unguwar su nemanta baya ganinta. Tana ta yi masa dariya yace "ni ko? Zan rama ne. Dadinta ma kema gashi kin kasa hakuri kin nemi number ta kin kira ni. But Wait, wai layin kine wannan?" Tace "oho maka. Tunda gori zakayi min" yace "to ko ba layin ki bane ba kiyi wa mai layin albishir cewa baccin sa is now limited, dan zanyi ta kira ne ba kakkautawa" sun jima suna hirar su freely like old friends, har sai da ta ji alamar shigowar Ruqayyah palo sannan tayi masa sallama ta kashe wayar, amma ta kasa cire murmushi daga fuskarta.
Ruqayyah ta shigo tana binta da kallo, sannan ta kalli wayar tace "sai yanzu kika gama wayar? Tun dazu wayar kike yi" Sumayya tace "a tambayo" tace "wa za'a tambaya? Ke nake tambaya ai" Sumayya tace "shi bai gaya miki number din waye ya bani ba?" Ruqayyah ta zauna tana cewa "ina zai gaya min? Shi bayan maqon kudi ma har maqon magana yake yi. Kwaji dashi daga ke har shi, shi ce min yayi wai wani abokin sa ne ni kuwa nasan ya za'a yi ni bansan kowa a abokan sa ba amma ke ki sani har kuke exchanging numbers" Sumayya bata kula ta ba ta fara chanja kayan ta zuwa na bacci, sai data gama sannan ta zauna a bakin gado tace da Sumayya "Sumayya so nake in ya sake dawowa jibi ki je gurin sa dan Allah kuyi maganar bikin nan, ni bansan me yake shirya wa ba kuma kinga lokaci yana ta kurewa. So nake ya bayar da kudin da za'a siyawa kawayen mu anko kowa a kai mata ba wai ace mutum ya siya ba, nima kuma ya bani kudin kayan fitar biki. Sannan kuyi maganar events din da za'ayi, da event centers din da za'a kama tunda kinga gidan nan ba zai isa ba. Ku dai yi maganar sosai Sumayya ni na kasa yi masa".
Sumayya ta tashi zaune tana cewa "to baki sani ba ai koya gama shirya komai. Amma dai zanyi masa maganar ai. Ke ma tun tuni nake miki maganar kawayen nan a samu a gaya musu, a fitar da anko kin ƙi" Ruqayyah ta tabe baki tace "ni so nake yi in na samu aka sai musu ankon sai a kai musu har gida, ai yafi a mutunce. Zan baki list din wadanda za'a siyawa sai ki fada masa number din, in aka yi musu kala biyu ai ya ishe su ko? dasu za'a yi duk events din".
Washegari da wuri Adam ya shirya ya tafi office din Hassan, tun kafin 12 din tayi dan kar yayi late ya kara laifi akan wanda yasan already ya riga yayi, dan yasan Hassan ya samu labarin da baya so ya samu din. Yau bai jima yana jira ba, 12 din tana yi aka aiko kiransa. Ya shiga da sallama sannan ya zaune, still fuskar Hassan ba yabo ba fallasa ya mika masa hannu suka gaisa sannan yace "kamar yadda nace maka zan sa a yi min background check to anyi din kuma zance kusan komai yayi dai dai da abinda ka gaya min except your name, ance ba sunan ka Adam ba, traditional name dinka Gbenga, Christian name dinka Joseph. To bansan inda ka samu Adam din ba" Adam yace "it is my Islamic name" Hassan ya daga kafada yace "but baya reading a duk takardun ka" Adam yace "zan gyara ai, so nake in na samu shiga makaranta zan gaya sai in cigaba da using" Hassan yace "it is okay, kawai dai so nake inyi confirming cewa kai din ne ba using info din wani kai ba, duk da dai description din duk irin naka ne sai dai wancan is a Christian kai kuma musulmi. Or aren't you?" Adam ya bata fuska, ransa ya fara baci yace "I am" Hassan yace "an samu misinformation kenan. Sai na dauka cewa ko ba dai dai naji ba sanda kace min you are a muslim, saboda wancan is a Christian daga shi har parents dinsa". Ran Adam ya kara baci yace "to amma shi mai baka info din bai gaya maka cewa Joseph yayi converting to Islam ya chanja sunan sa zuwa Adam sannan ya bar gida two years ago ba? Maybe you should dig dipper" Hassan ya danyi murmushi kadan sannan yace "nasan wannan, just want to confirm, kuma an gaya min Joseph yana da bad temper" Adam ya mike tsaye yace "so does Adam" sannan ya juya ya fice daga office din tare da bugo kofar.
Ransa a bace yake har yaje gida, bai san neman aikin zai zamar masa terere ba da bai fara ba tuntuni. Yasan dole zai digging that