Showing 36001 words to 39000 words out of 300844 words
sai a hada bikin mu nan da wata biyar" ya zaro wayarsa yana bude lock din yace "ki saka min number dinki sai in bata ta kira ki ku gaisa" ta karbi wayar tana kallon hoton da yake kan screen din. Hoton sa ne tare da wata kyakkyawar yarinya wadda kallo daya tayi mata ta san ta fita komai, taji wani abu ya tsaya mata a wuyanta yana so ya kawo hawaye cikin idonta
Ta yi sauri ta mika masa wayarsa tace "bani da waya ai ni" Sumayya tace "kasan yanzu ne muka gama secondary school, Baba kuma dama yace sai mun gama zai siya mana waya" ya dan bata rai yana tunani yace "ku ka gama ko zaku gama? ai ba'a gama exams ba an dai yi neco saura waec. Ba zakuyi waec din ba?" Suka yi shiru duk su biyun, sai ya fahimci bashi da amsa dan haka yayi saurin chanja topic din da cewa "amma dai zaku cigaba da karatu ko?" A tare suka ce "eh" yace "good, Allah ya taimaka".
A lokacin ne yaro yazo ya kawo masa lemo da ruwa a jere akan karamin faranti tare da kofi akai. Sumayya ta karba sai ta bude motar ta ajiye masa sannan ta rufe. Yace "Nagode sosai. Dama kishirwa nake ji. Bara inzo in tafi kar in gajiyar daku da magana, ni bana gajiya da magana. Sai dai kuma gashi ban kawo muku komai ba" da sauri Ruqayyah tace "lah, babu komai, ai zuwan shine mafi muhimmanci akan wani abu" Sumayya ta kalle ta da mamaki sai kuma tayi saurin gyara fuskarta tace "haka ne" yace "a'a ba haka bane ba, ita kyauta ai abu ne mai kyau saboda tana kara soyayya a zukatan mutane, ko mai kankantar abu in aka baka shi kyauta sai kaji wanda ya bakan ya kara samun daraja a gurinka. Nima kunga yanzu ruwan da kuka bani ai naji dadi har cikin raina. Koda mutum ya fika komai na duniya in kuka hadu samu wani abu ka bashi, zaka kara daraja a gurinsa"
Ya cigaba "wannan yasa duk wanda na hadu dashi ina kokari inga na bashi wani abu da zai ke tunawa dani kuma yaji yana son mu sake haduwa. Ku ma kuma ba zaku zama exceptional ba. Ban taho da leda ba amma na san a jikina ba za'a rasa wani abu ba, ko cash ne" sai ya fara laluben jikin sa, yayi tsaki "these days sai mutum ya duba jikinsa yaji wai bashi da kudi".
Ruqayyah ta sake cewa "ba wani abu fa, ka barshi kawai".
Sai ya bude motar ya bude aljihun mota, sai gashi ya dauko rafar farare bugun Abuja, ya fito ya miko wa Sumayya, ga wannan kwa sayi jambaki" Ruqayyah tayi saurin rike hannun Sumayya duk kuwa da cewa sumayyan ba wai miko hannun tayi ba tace "uhm uhm, ba zamu karba ba gaskiya." Da mamaki yace "saboda me?" Ta sunkuyar da kai still hannunta rike dana Sumayya Tace "kawai dai. Babu abinda zamuyi dashi. Mungode"
Yace "ban taba jin yammata sunce babu abinda zasuyi da kudi ba sai yau. Ni sisters dina kullum complain suke kudi yayi musu kadan, kullum suna cikin siyan kayan kwalliya, jaka takalmi, da sauransu" Ruqayyah tace "mu duk wannan basu dame mu ba"
Yayi ajjiyar zuciya sannan ya jefa kudin cikin mota, Ruqayyah taji tamkar zuciyarta ya ciro ya jefa a mota amma ta maze, yace "ban taba yin kyauta an dawo min da ita ba sai yau. Amma babu komai, nasan ta inda zan bullo muku" duk suka yi murmushi. Yayi musu sallama ya shiga mota suka matsa ya tafi.
Sumayya ta juyo gurin Ruqayyah "what? Kece kika mayar da wannan kuɗin da kanki?" Tayi ajjiyar zuciya "kar ki kara min bakin ciki akan wanda nake ji already. Ke fa kika yi min wa'azin in chanja hali, to halin nake chanja wa" ta wuce ciki a ranta tana mitar yadda Hussain zai dauki wannan uban kudin a motar Hassan yayi kyauta dashi, Allah kadai yasan irin barnar kudin da yake yi masa.
Hussain yana kallonsu ta mirror har suka shiga gida sannan ya mayar da hankalinsa fully kan tukinsa, ya girgiza kansa, shi har yanzu bai ji tayi masa ba duk kuwa da cewa bashi da wani dalili na feeling like that. He test them with money kuma sunci jarabawar amma still.......
Ya dauki wayarsa ya kira Hassana (kanwarsu) "zan turo miki kudi yanzu kije ki fitar ki danyo min siyayya irin taku ta mata, kaya masu kyau, komai guda biyu iri daya. Zan kuma yi miki aike sai ki hada da kayan ki bawa drivern da yasan gidan su Hassana akai musu ita da yaruwata".
Bayan sun gama wayar ya kira wani dealer na waya da yake kawo masa wayoyi yace "ina son wayoyi guda biyu, latest. Ka aika min dasu gida".
Da daddare suna zaune a tsakar gida suna cin tuwon shinkafa miyar taushe har da nama, duk a cikin kudin da Hassan ya ajiye ranar nan ne. Gaba dayansu su hudu a tray daya Inna kuma da Baba suma suna ci tare, ga maganin sauro an kunna a gefe ga iska tana kada su. Baba yana basu labari "wato gobe akwai drama, an sake aiko mana fa mu koma wannan inta uku din nan. Gashi yaron nan Hassan naga alamar bai san dani a ciki ba sai dai kawai ya ganni" a lokacin suka ji tsayuwar mota sannan aka yi sallama. Sulaiman ne ya fita, an jima kadan sai gashi da bagco guda biyu da kuma karamar leda yana ta washe baki.
"Wato yammatan nan sai kun bani tukuici, wai wannan kayan sako ne inji Hussain yace ace muku "asha yammatanci lafiya".
Wannan littafin na siyarwa ne, in baki sani ba kika karanta a rashin sani to yanzu kin sani. In kina son cigaba ki nemi wannan number 08067081020.
Episode Fourteen : The Gate man
Da sauri Ruqayyah ta mike, zuciyarta fara kal kamar takarda, it is about time daya kamata suma su fara shigowa gari. Wannan talauci haka har ina!
Ta tari Sulaiman a hanya tana karbar karamar ledar cikin zumudi tace "inji Hussain ko inji Hassan?" Ya dan dakata yana tunani sai kuma yace "kamar dai Hussain yace min, oga Hussain, haka yace. Amma bara in koma in sake tambayar sa" ya ajiye kayan zai juya Inna Ade tace "kai! Dawo nan. In Hassan in ma Hussain menene abin tambaya? Duk daya ne in daya ya bayar tamkar dayan ya bayar ne "
Ruqayyah ta bude ledar hannunta, jikinta har rawa yake yi, tayi arba sa kwalayen waya guda biyu "wayyo Allah na" ta fada tana rungume kwalin wayar a kirjinta "Sumayya wayoyi ne, handsets ne ta so ki gani!" Sumayya ta ajiye cokalin hannunta ta mike da sauri tana karbar guda daya a hannun Ruqayyah sannan suka saka ihun murna suna rungume juna. Samarin kuma suka bude jakankunan suka fara fito da kayan ciki. Kayan sawa ne da sauran kayan bukatu na mata. Zunnur yace "wannan duk sanda ya sake dawowa sai naje na gaishe shi nima na samu rabona".
Baba ya daga murya yace "lafiyar ku kuwa? Menene haka kuke yi? Menene wannan din?" Inna Ade ta karbe wayoyin hannunsu Ruqayyah sannan ta ja jakar zuwa gaban Baba, Ruqayyah ta biyo ta tamkar magnet, Inna tace "kaya ne baban biyu, Hussain ne dazu da bakanan ya zo yaga yaran nan shine yanzu ya aiko musu da kaya. Ta fada tana kokarin firfito masa da kayan, ya hade rai yace "kayan lefe ne?"
Ta yi dariya "kayan lefe kuma Baban biyu? Kayan lefen ne za'a aiko driver ya kawo?" Yace "to kayan menene?" Tace "kyauta ce kawai yayi musu" ya kuma hade rai "gaya masa sukayi suka ce basu da suttura? Ko kuma sutturar jikinsu ya raina" Inna ade tayi shiru, ya juya kan yammatan, "rokonsa kuka yi kuka ce ya siya muku?" Da sauri Ruqayyah, cikin rawar murya tace "wallahi Baba ba rokonsa muka yi ba, daya bamu kudi ma cewa muka yi bama so, shine kawai ya aiko mana" ya juya kan Inna Ade "to ba da ni za'a yi wannan abin ba. Yanzu me kike tunanin zai faru idan Hassan din yace ya fasa aurenta? Ya zamuyi mu biya su kayan su? Gidan nan zan saka a kasuwa?" A hankali Ruqayyah tace "ba zai ce ya fasa ba" ya juyo yana kallonta yace "to fitsararriya, ina magana kina mayar min ko? Ta yaya kika san ba zai ce ya fasa ba? Kin san abinda gobe zata zo dashi ne?"
Inna Ade tace "amma Baban biyu bana jin irin mutanen da zasu yi mana haka ne, in sun fasa ma bana jin zasu ce a biya su kayan su, kuma ma ai ba rokonsa suka yi ba" yace "to kaddara ma ba zasu ce a biya su ba. Yanzun in kika bawa wannan yarinyar" ya fada yana nuna Ruqayyah data rungume kwalin waya a kirjinta idonta ya kada yayi jawur "wannan wayar, kika kuma bata sannan leshin ta saka, idan ba'a yi auren ba ta yaya zata cigaba da girmama wannan" ya nuna wayar hannunsa "da kuma wannan" ya nuna kodaddiyar atamfar jikin Inna.
Ruqayyah ta maimaita "ba zai ce ya fasa ba" yayo kanta "in kika kara Magana sai na kakkarya ki a gurin nan na zubar da kasusuwanki" Inna Ade ta shiga tsakani tana bashi hakuri "dan Allah kar ka taba ta Baban biyu, dan girman Allah kar ka dake ta" ya juyo kanta "ki tattara kayan nan ki nemi gidan wata kawarki ki kai a ajiye, duk ranar da akayi auren sai a dauko su a basu"
Ruqayyah ta durkusa "Baba dan girman Allah kar ka karbe kayan nan, dan Allah ka bar mana abin mu, na tuba Baba wallahi na daina duk abinda baka so, dan Allah ka bar min kayana Baba" Inna Ade ta taya ta roko "ko ba zaka bar musu wayar ba ka bar musu kayan suma su samu suyi kwalliya, ba rokon su suka yi ba kyauta ce suka basu kuma shima Hassan din ai zai so ya ganta fes fes, gashi yan'uwansa suna zuwa, dan Allah Baban biyu kayi hakuri ka bar musu" yace "wato da saka hannunki kenan ko? Shikenan, su rike kaya amma babu ruwana"
Ya juya ya saka takalmi ya fita, Inna Ade tasan fushi yayi amma kuma bata son abinda zai kara hargitsa tsakanin sa da Ruqayyah, kuma ita tana ganin babu laifi in an karbi kayan.
Bayan ya tafi suka zauna suna dudduba kayan duk da dai duk jikinsu a sanyaye yake da fadan da Baba yayi, banda Ruqayyah da take ta lissafin wanne tailor ne yafi kowa iya dinki a kaduna? Gurinsa zata kai dinki. Ta dora wata doguwar riga kenan a cinyarta sai wata envelope ta fado daga cikinta, ta duba ta lura babu wanda ya gani sai ta zare ta ta saka a rigar ta. Tasan kudi ne a ciki, maybe kudin dinki, Bata so Inna Ade ta gani dan in ta gani karba zata yi kuma ba zata bata wani abin kirki ba kamar yadda wancan dubu ashirin din da Hassan ya ajiye musu duk Baba aka bawa ya siyo musu kayan abinci.
Bayan sun gama suka tattara kayan suka mayar ,inna tace sai da safe sai su dauki wanda zasuyi amfani dashi su kai gurin dinki "sai dai kuma sai an nemo kudin dinkin" inji Inna.
A daki bayan sun kwanta ita da Sumayya ne tace "Sumayya, kina ganin Hassan zai iya cewa ya fasa aure na?" Sumayya ta juyo tana kallonta tace "me yasa kike tambaya?" Tace "kawai dai. Baba baya son auren nan. Bansan me zai faru ba, ina jin tsoro" Sumayya tace "ki ji tsoron Allah. Kiyi ta addu'a" suka yi shiru kowa yana tunanin sa, har bacci ya fara daukan Sumayya sai Ruqayyah ta kuma cewa "Sumayya? Ya kika ga Hussain dazu?
Sumayya tace "ya kuwa na ganshi? He is okay" Ruqayyah tace "ba haka nake nufi ba, ina nufin yafi Hassan haduwa ko?" Sumayya ta mike zaune tana kallon ta tace "no......bai fishi haduwa ba, kar ma ki sake wannan tunanin dan Allah" Ruqayyah ta mike itama zaunen tace "ba wani abun nace ba ai, kawai dai kamar ya fishi....." Sumayya tace "gayu? Ko kuma bagu da mota da kaya masu kyau da sababbin kudi" Ruqayyah ta fadi abinda yake ranta "ya fishi kyau" Sumayya ta runtse idonta tana jin zafin abinda yar uwarta take neman yiwa Hassan tace "bai fishi kyau ba. Ya dai fishi fari" Ruqayyah tace "ya fishi fari ko kuma dai kice shi fari ne shi kuma baƙi?" Sumayya tace "fari da baƙi duk halittar Allah ce, amma ni personally ma nafi son bakin mutum akan farin. Sannan ni bayan kalar fata banga wani banbancin halitta a tsakanin su ba dan kamannin su har abin mamaki ne dashi, hanci, baki, ido, shape din fuska, tsaho kirar jikinsu duk iri daya. Kuma Hassan yafi kama da matured kamilallen mutum shi kuma Hussain yafi kama da ladies man, ni in nice da zabi zan zabi Hassan sau goma kafin in zabi Hussain sau daya" ta koma ta kwanta tare da juya wa Ruqayyah baya cikin jin zafin maganar ta. Tana jin Ruqayyah tayi addu'a sannan ta kwanta, sai kuma tace "har dimple ne dashi"
Sumayya ta kuma juyowa cikin fushi tace "gaya min gaskiya Ruqayyah, zaki juyawa Hassan baya ne ki ce hussainin sa kike so kuma? Kina ganin hakan mai yiyuwa ne?" Ruqayyah tace "Ni haka kika ji nace miki? Dan Hussain ya fishi kyau ai ba wai ya fishi komai ba ne ba, Hassan shine babba, sannan shine mai kudin," Sumayya tace "wrong. Wannan ba shine dalilin da ya kamata ki fada ba na zaben Hassan, ya kamata ki zabi Hassan ne saboda Hassan shi yake sonki ba Hussain ba, Hassan shi ya kamata ki so ba Hussain ba" Ruqayyah tace "shi nake so ɗin ai. Amma dai ai ba haka aka so ba kanin miji yafi miji kyau".
Sumayya ta runtse idonta tana hana zuciyarta rinjayar ta gurin juyowa ta rufe Ruqayyah da duka. Sai taji cewa ta fahimci menene problem din Ruqayyah, ba wai bakar zuciya ko fada, ko son abin duniya ne da ita ba. A'a rashin godiyar Allah ne da ita. In taga abu zata kwallafa ranta akan tana sonsa amma da zarar ta samu to kuwa ya zama banza abinda ya fishi kuma take hari. And now she have her eyes on Hussain, and Sumayya knows that abinda yasa kawai ba zata rabu da Hassan ta makale wa Hussain ba shine saboda kuɗi, saboda tana son kudin Hassan din. Sai Sumayya taji tana tausayin Hassan. Tana kuma tausayin Ruqayyah saboda karin maganar hausawa da suke cewa "duk wanda bai gode Allah ba to kuwa tabbas zai gode wa azabar Allah".
Washegari da sassafe Baba ya fita yace musu ya tafi gurin interview, suka yi masa fatan alkhairi ya tafi.
A bangaren su Hassan kuwa suma da sassafe suka fita. Hassan ya kai Hussain airport ya tafi China zai siyo injinan da wancan karon bai samu damar siyowa ba, dama kudin su ne ya hada da kudin da yake account dinsa ya bayar kudin ransom din Hassan, yanzu kuwa tunda alhamdulillah kuɗin sun dawo shine zai koma ya siyo duk da cewa yasan ba zai same su a wadancan price din ba.
Daga airport shi kuma Hassan gurin interview ya zarce, dan yasan cewa yanzu mutane suna nan sun taru suna jiransa shi kuma baya son ya bar mutane suna jiran sa.
Baba yana zaune akan layi tare da sauran mutane, wani ya fara mita "haka kawai bayan mun riga munzo munyi interview din nan, sai da akayi wata guda kuma sannan sai a dawo a sake cewa muzo mu kuma yin wata? Shikenan yanzu a duniya masu kudi basa tausayin talakawa? Wannan ai zalunci ne, gashi kuma mum zo din sannan an shanya mu a waje kamar wasu kayan wanki".
Baba yace "haba bawan Allah, ba ka san abinda ya samu mutumin nan bane ba? Masu garkuwa da mutane ne fa suka sace shi da kyar ya tsira da ransa" wasu a gurin suka fara jajanta abin wasu kuma suka ce "ina ruwan mu to mu, mu muka sace shi ko kuma mu aka bawa kudin diyyar? Ai irin wannan abin da masu kudi suke yi wa talakawa yana daya daga cikin abinda yake jawo musu irin wancan balain"
Sai Baba yayi shiru kawai ya barsu, dan wadansu mutanen ko yaya ka kai da bayani ba zasu bude kwakwalwar su ba ballantana su fahimce ka. A lokacin ne Hassan ya shigo gurin da saurinsa, Baba ya lura da yadda yake amsa gaisuwar mutane cike da kulawa sannan ya dan bada hakurin jiransa da akayi sai kuma ya shige ciki. Sai Baba yaji dadi a ransa, yaji yana alfahari da shi yana kuma kara saka ran ya zamo surikin sa dan ya yarda dashi, sai dai ita yar tasa ce bai yarda da ita ba.
Akayi ta kira ana shiga ana fitowa har aka zo kan Baba. Ya shiga da sallamar sa. Hassan ya amsa tare da dago kai, suna hada ido da Baba sai ya mike. "A'a, Baba, sannu da zuwa." Ya fada yana shafa kai, Baba ya zauna sannan shima ya zauna yana gaisheshi sannan yace "Baba ai da an kira ni ni sai inzo gida ba sai anzo nan ba" Baba yace "a'a, ai ba wani abin bane ba, maganar aikin nan ce ta kawo ni an kira mu ance mu sake dawowa za'a sake gwada mu" Hassan ya danyi shiru yana tunani sannan yace "wai wannan aikin dama kaima kazo wancan watan?"
Baba yayi murmushi yace "nazo mana, ai ba zaka gane ba tunda mutanen da yawa" Hassan yayi shiru yana tunani, shi dai ba zai iya hana Baba aikin nan ba ba kuma zai iya bashi ba. Aiyukan na labourers, messengers da kuma na masu gadi ne, ba zai iya saka Baba aiki ba, ba zai iya aikensa ba ba kuma zai iya kullum yana bude masa kofa in zai shigo ba. A matsayin sa na surukinsa hakan bai dace ba.
Ya gyara zama