Showing 42001 words to 45000 words out of 300844 words
daya kamata. Yana yi yana mata bayani dalla dalla na yadda zata yi operating komai.
Sai da ya tabbatar ta gane sannan yayi kamar zai mika mata sai kuma ya juya wayar ya dauke ta a hoto. Ya jima yana kallon hoton sannan ya miko mata, itama ta kurawa hoton ido, camera din ta fito da fuskarsa sosai tayi kyau, ga background na mota mai kyau, ga kuma kyakkyawan murmushi a fuskarta, sai taga kamar ba ita ce ba, sai taga kamar irin yayan masu kudi din nan wadanda basu da matsalar komai a rayuwa. Yes, that's who she wants to be, yes, that's who she is now.
Da yamman ranar ta shiga makotansu gidan su Minal, a tsakar gida ta same ta taba kwance tana daddanna wayarta. Ruqayyah ta zauna tana cewa "albishirinki Minal" sai ta mika mata sabuwar wayarta. Minal ta karba sannan ta mike zaune baki da ido a bude. "Na shiga uku! Ruqayyah a ina kina samu wannan wayar" Ruqayyah tayi dariya tana jinta tana yawo a saman gajimare. Sai dai tayi plan din ba zata gayawa friends dinta ba tukunna, so take tayi surprising dinsu, so take kawai sai dai su ga iv.
Tace "a inda nasamu bashi da muhimmanci, abu mai muhimmanci shine na samu din" Minal ta kuma juya wayar a hannun ta sannan tace "Ruqayyah wannan fa babbar wayar mijin Aunty Hafsa ne. Irin wannan din yaso siya ya kasa shine ya sayi karamarta " (yayarta, wadda da kudin mijinta suke ji a gidan su' Ruqayyah ya kara kumbura tace "kuma gashi ni nayi ta ba. Kinga, ni zuwa nayi ki bude min irin su facebook din nan da sauran su. Ni na kasa gane yadda zan bude"
Nan take Minal ta bude mata facebook account, tayi mata komai sannan tace "saura hoton da za'a saka miki" Ruqayyah tayi sauri tace "akwai wani hoto, zaki ganni a cikin wata mota shi zaki saka min" Minal ta budo hoton sannan tace "wannan motar kuma fa, motar waye?" Ruqayyah ta juya idonta tace "ina ruwanki, in ba zaki saka min ba ki barshi" sai Minal tace "daga tambaya? Ke fadan ki bw matsalar ki. Kinga, a shawarce kar ki saka hotonki, saboda shi facebook guri ne na maza da mata gabaki daya, kinga babu dadi ki saka hotonki maza suna ta kallonki, gwara ki saka wani abu haka" Ruqayyah ta gyada kai tana daukan shawarar ta, yasan Hassan ba zai kasa yin facebook ba, kar yaje ya ga hoton ta kuma a samu matsala, amma kuma taso yin fafa da wannan hoton, sai dai dole ta hakura.
Tana komawa gida ta tarar da Sumayya a zaune a daki ita kadai, daga ganin fuskarta tasan akwai problem, tace "ke kuma fa? Lafiya?" Sumayya ta dauko farar envelope ta miko mata tace "wannan kudin na gani a cikin rigar ki, kudin menene" Ruqayyah ta bata rai tana miko hannu tace "kudi nane, bani abina? Sumayya tace "a ina kika same su? Yaushe aka baki su" Ruqayyah tace "a cikin kayan nan aka sako su, inna tana gani nasan Baba zata bawa ninkuma ina bukatar su shi yasa na boye" Sumayya taji ranta ya kuma baci tace "tun yanzu? Tun yanzu Ruqayyah har zaki fara boye abin duniya dan kar family dinki su mora, nan gaba me zai faru kenan?" Ruqayyah ta warce kudin tace "ai na bayar da wancan, wannan kuma ina bukatar sa kuma bazan bayar ba" Sumayya tace "kin duba kinga yawan kudin nan kuwa? Na tabbatar kudin sun isa ayi katangar gidan nan dasu, kinga ai kema in Hassan yazo ba zaki ji kunya gidan ku babu katangar arziki ba" Ruqayyah ta daga kafada tace "a haka ya ganni, a haka kuma yace yana sona. In baya son gani gidan nan ya gina mana wani".
A ranar bayan Baba ya dawo gida Sumayya ta dauki wayarta ta kai masa "Baba ga wannan, ni babu abinda zanyi da ita kuma naga kamar zata yi tsada sosai, a siyar da ita mu gani ko kudin zai isa ayi katangar gidan nan" Baba ya karbi wayar yana jujjuya ta sannan yace "Nagode sosai Hussaina. Allah yayi miki albarka".
Kwana biyu bayan nan Hassan ya zo gurin Ruqayyah zance, sai yayi mata bayanin cewa a karshen satin nan suke saka ran zuwa Gombe gabaki dayansu shi da yan'uwansa, idan kuma sunje zai shigar da maganar auren su dan azo a nema masa.
Ruqayyah murna kamar tayi rawa amma ta maze tace "da wuri haka? Da ka bari ai an dan kara kwana biyu mun kara fahimtar juna ko?" Yace "menene baki fahimta nawa ba in fahimtar dake yanzu? Ni dai a bangare na babu wani abu da nake ganin ya kamata in kara sani, abinda na sani ya gamsar dani sosai"
Kamar ranar nan, suna yin sallama tana shiga gida sai ga Adam a tashi motar yayi packing a kusa da Hassan. Hassan ya gane motar, Adam kuma ya gane Ruqayyah duk da bai ga fuskarta ba, a ransa yace "ta tabbata zance yake zuwa" ya fito kamar ranar nan suka gaisa da Hassan sai yace "ashe zance kake zuwa gidan nan? Gurin Ruqayyah" Hassan ya rungume hannunsa a kirjinsa yana studying yaron gabansa yace "kai kuma zance kake zuwa gurin Sumayya" Adam yayi dariya "noo, ba zance nake zuwa, na shigo ta nan layin ne kawai dan maybe in samu in ganta, but in na aika ba lallai ma a barta ta fito ba dan ranar nan ma da kyar aka barta ta fito" Hassan yace "and you want to see her?" Adam yace "yes, I do. I really do. But I guess babu bahaushe Musulmin da zai bar yarsa take kulani ko".
Hassan yace "no, no, no. Kar kace haka. Babansu yana da kirki sosai. In baka shawara? Kayi kokari ka ganshi ka gaya masa abinda yake ranka, bana jin zai ki amincewa. Ina iyayenka?" Yace "basa nan" sai ya dauke kansa gefe, Hassan yace "a ina kake da zama" yace "daki nake renting, ni da friend dina" Hassan yace "school fa?" Adam yace "na gama secondary, zan cigaba in na tara kudin".
Hassan ya dauko wayarsa ya kira layin Ruqayyah. "Sorry na danyi mantuwa. Turo min Sumayya Please" sai ya kashe ya mayar da ita aljihu yace "gata nan fitowa, you can see her" Adam yayi murmushi, Hassan yana lura da yadda yaji dadi sosai.
Ruqayyah ta ajiye wayar tana cewa "yes! Sumayya kije waje Hassan yana kiranki, sako zaki karbo min" Sumayya bata ce komai ba ta dauki hijab dinta ta fito, har yanzu haushin yaruwarta take ji na hana babansu kudi duk da tasan yana bukatar su.
Tana fitowa taga Adam a tsaye tare da Hassan, take taji bakin cikin ta ya yaye farin ciki ya maye gurbin sa, ta rufe baki tana dariya, shima dariyar yake yi yana tahowa inda take. Sai Hassan yaga sun bashi sha'awa sosai, Sumayya tace "Adam? You are here" yace "yes am here, na shigo layin, hoping to see you sai wannan bawan Allah ya taimake ni ya kira min ke. Da fatan ranar nan ba'a yi miki fada ba" tace "no, ai cewa tayi kar in dade kuma ban dade ba"
Ta juya tana kallon Hassan tace "ina yini" yace "hmmm. Sai yanzu kika ganni? Ai ni har nayi fushi" ta karaso tana cewa "ayi hakuri babban yaya, ya zanyi in kasa ganinka bayan gaka a gabana?" Yace "na sani ko wani ya rufe miki ganin ki?" Ta danji kunya kadan tace "haba dai".
Ya danyi murmushi sai ya dauko complimentary card dinsa ya mika wa Adam yace "come to my office duk sanda ka samu dama, I might get something for you" ya karbi katin yana kallon sunan sai yayi dariya yana rike baki, ya juya kamar wanda zai rungume Sumayya sai kuma ya rungume hannunsa, yace "thank you sir, thank you so much. Amma bani da credentials din da zaka bani aiki dasu"
Hassan yace "I am already getting an idea na aikin da zan baka, ba ka iya driving ba?" Adam ya kalli motarsa yace "sosai ma kuwa" Hassan yace "hmmmm, then maybe it is about time da ya kamata Hussain ya samu personal driver. Yana dawowa daga wannan tafiyar zan zuga shi ince bai kamata dangoten Kaduna yake driving kansa a mota ba, he will like you, tunda naga kana da tsafta da gayu, a matsayin drivern Hussain zaka sami daki a gidan mu, zaka ke samun abinci kaga baka da wannan matsalar, Hussain ba mazauni bane ba, dan haka you will have alot of hutu im baya nan, in yana nan ma am sure sometimes mantawa zai ke yi da kai. Motar ka sai ka vayar ana yi maka haya ana kawo ma ka balance, that, plus albashinka and all the goodies da za kake samu daga gurin Hussain zai ishe ka kayi sponsoring karatun ka"
Adam daya kasa rufe baki ya juya ya kalli Sumayya ita ma da take ta murmushi yace "sai in biya mana makaranta ni da Sumayya mu tafi tare" Hassan ya gyada kai yace "I like you, I really like you".
Wannan littafin na siyarwa ne. In kina so kiyi min magana ta wannan number 08067081020.
WhatsApp only, banda calls please.
Sixteen : The Houses
Bayan Hassan ya tafi Sumayya tace wa Adam "ka je fa ka same shi din, yana da kirki sosai" yace "zan je, gobe weekend amma ranar Monday first thing in the morning zanje in same shi" ya sake jujjuya card din a hannunsa yace "H & H fa" tace "yes, tashi ce" yace "to who is Hussain?" Tace "dan gayun brother dinsa" suka yi dariya gaba ki daya.
Yace "yanzu in zan iya biya mana school tare, Baba zai barki ki je?" Tace "it is so nice of you to say that Adam. But bana jin Baba zai yarda ka ce zaka boya min. Shima yana da burin ya biya mana muyi karatu sannan kuma Baba mutum ne da bai fiya son ayi masa abu ba, yafi son komai yayi da kansa in dai zai iya" yace "Ruqayyah fa? Ita ma zata yi karatun? Naga....." Ya nuna inda Hassan ya tsaya, ta dan bata rai tace "tare muke da niyyar zuwa, but yanzu all of a sudden Hassan yazo da maganar aure kuma nasan ba zai jira ta gama makaranta ba, to gaskiya ban sani ba ko zai barta bayan aure ta cigaba da karatu"
Adam yace "yanzu misali, just for example, idan..... Idan na aure ki nima, kinga ai ni zan biya miki karatu ko?" Tayi dariya, "Adam kenan, aure fa kace" ya dan hade rai "aure fa, ko ba zaki auri Igbo ba" ta dago kai tana kallonsa, ita dai tun ganinsa na farko ta san ba Bahaushe bane ba amma bata iya tayi placing yarensa ba. Kuma bata tantance ko musulmi ne ko akasin haka ba. To yanzu gashi ya fada mata, Igbo. Akwai kabilar da suka fi Igbo samun sabani da hausawa kuwa?
Ta sunkuyar da kanta ai taji shima yayi shiru bai kuma cewa komai ba, ta dago kai sai taga bacin rai a fuskarsa, ya juya yana cewa "it is okay, bara in tafi before I put you in trouble" yayi taku biyu tace "Adam" sai ya dakata amma bai juyo ba, ta karasa inda yake ta zagaya ta gabansa tana noticing kirar jikinsa, tace "Igbo, hausa, fulani, yaroba, Igala, kanuri duk ba shine mai muhimmanci ba, babu wanda yafi wani muhimmin a gurin ubangiji sai wanda yafi tsoronsa" ya gyada kai yace "na sani, but a gurin ubangiji kika ce ai, ni kuma a gurinki nake tambaya, can you.......marry an Igbo guy".
Ta kuma sunkuyar da kanta kasa, maganar aure ba karamar magana bace ba, sai ta juya maganar tace "ba la san hausawa yanzu cewa suke auren wani yaren yafi dadi ba? Yace "hausawa ne suka fada ko ke ce kika fada? Ni view dinki nake son ji ai bana haudawa ba" da daga kai tana kallonsa a cikin hasken farin wata, ita dai tasan he is the most handsome man data taba gani a rayuwarta, fuskarsa irin fuskarnan ce da in ka kalla ba ka iya cire ta daga ranka.
Tace "my view, tribe doesn't matter, what matters is the person himself. In dai kasan mutumin da zaka aura kuma dabiun sa sunyi maka kuma shima haka, tribe dinku doesn't matter" yayi murmushin daya kara wa fuskarsa kyau yana kallon cikin idonta yace "then, nayi miki?" Tayi kokarin cire idonta daga cikin nasa amma sai taji ta kasa, sai taji bata so, she want to live there forever. Kasa kasa tace "I can't say, I don't know you" shima kasa kasa yace mata "I know you and I like you" taji maganar sa ta shige ta har cikin ƙafafuwan ta sai tayi saurin cire ionta daga nasa ta zagaye shi tana tafiya zuwa gida tace "good night Adam" bai juyo ba yace "good night Sumayya".
Taji sautin dariya a cikin muryarsa itama sai tayi murmushi. A tsakar gida still da murmushi a fuskarta suka kusan cin karo da Ruqayyah. Yace "na jiki shiru, nace bara inbi sawu inji ko lafiya" Sumayya ta wuce ta tana cewa "ya tafi ai yariman naki, tun dazu" Ruqayyah ta bita a baya "and? Ina sakon?" Sumayya tace ba tare data kalle ta ba "bai bani ba komai ba, gaisawa kawai muka yi, sai dai ki kira shi ki sake tambayarsa ko ya kuma mantawa ne". Ruqayyah tayi tsaki tana kananan maganganu ta wuce Sumayya ta shige daki.
Sumayya bata gaya mata zancen zuwan Adam ba kuma bata da niyyar gaya mata din saboda tasan zata iya gayawa Inna, ita kuma tafi son in Inna zata ji ma ya kasance daga bakinta zata ji bana wani ba.
A dakin su ta kwanta still da murmushi a fuskarta, idonta a lumshe tana tuno murmushin Adam, Ruqayyah ta kalle ta tayi tsaki tace "this one that you are smiling kamar wadda aka yiwa kyautar mota" Sumayya ta sake murmushi tace "abinda aka bani yafi mota muhimmanci a gurina. But I guess ke ba zaki fahimta ba".
Saturday family din Aunty baki dayansu banda Hussain da baya kasar suka tafi Gombe, a can suka yi weekend, a cikin weekend din ne kuma suka shigar da maganar neman auren da Hassan yake yi suka nemi alfarmar azo a nema masa officially. In kuma anje naman an bayar din suna so a saka rana ta zama daya data Hussain da kuma Hassana.
Ranar Monday suka dawo da safe, Hassan ne ya sama suka yi fitowar sassafe saboda yana so yaje office akwai abubuwa da yawa a gabansa. A office din ne bayan ya gama abubuwan da yake yi sai yaga kiran wani agent da ya saka ya samo masa gida. Ya daga a ransa yana tunanin an samu kenan. Dan yasan in baa samu ba mutumin ba zai kira shi ba tunda specifically ya yi masa bayaniy irin gidan da yake so, hatta girman gidan, yawan dakunan da tsarin dakunan sai daya lissafa masa. Shi komai nasa a tsari yake yin sa and he sticks to wannan tsarin nasa. Ba dan emergency yake neman gidan ba ma da gina wa zaiyi yadda zai yi exactly irin yadda yake so.
Tun sanda Allah ya hada shi da Ruqayyah da family dinta yake tunanin mai ya kamata yayi musu, farko yayi tunanin kudi, sai kuma ya fahimci Baba ba mutum ne mai son ake bashi kuɗi haka nan ba, ya san in zai karba ma sai sun kai ruwa rana kamar yadda suka yi ta yi akan aiki, kuma shi yana ganin girman sa sosai baya son yayi tayi masa musu.
Wannan yasa ya yanke shawarar siya masa gida saboda ganin yanayin yadda gidan nasu yake ciki. Dama yana da kuɗin sa da yake tarawa, kudin albashin sa a matsayin sa na chief of staff na H &H group of companies. Tun sanda Hussain ya bude kanfanin sa na farko ya bashi wannan matsayin kuma shi yake running kusan komai, ma'aikata da yawa basu san Hussain ba Hassan suka sani. Da yawa daga cikin su kuma suna yi masa kallon kamar shine mai gurin shi kuma bai taba tsayawa yayi wa wani bayani ba saboda yana ganin babu bukatar yin bayanin.
Albashin sa account dinsa yake shiga kawai, baya taba using dinsa sai dai in zai siya wa kansa wani personal abu kamar kayan sawa ko kuma in zaiyi wa wani kyauta, amma duk kudin da ake kashewa a gidan su, duk bukatun Aunty da yammatan ta, duk motar da take cikin gidan na Hussain ne, shi yake komai amma ta hannun Hassan, check book ya samu duk yayi signing ya ajiye a dakin sa yace da Hassan "duk abinda ake bukata kawai ka cike ka fitar ba sai an neme ni ba, ni bani da lokaci kar inje inke manta important things".
Amma Hassan bai taba cirar ko da kwandala yayi buƙatar kansa ba.....
Da lissafin sa shine zai yi amfani da kudinsa gurin siyawa kansa gidan da zasu zauna shida iyalinsa in yayi aure, amma kuma sai ga Hussain ya sai gida ya fara gina musu tare. Abinda ya saka baiyi rejecting ba shine idea din tayi masa kyau na zamansu tare, iyalinsu tare sannan kuma a kusa da su Aunty. Yana ganin wannan zai karfafa zumunci a tsakanin yayansu da matansu. Amma duk da haka sai ya kuduri aniyar gina gida da kudinsa ya ajiye shi a matsayin nasa in yaso ko haya ya bayar. Tunda dai gidan da zasu zauna din na Hussain ne dan bai furta yace ya bar masa kyauta ba, kuma baisan abinda gaba zata haifar ba.
Sai dai kuma yanzu ga Hassana ga iyayenta da kannenta, wanda Hassan yake jin yanzu kamar sun zama responsibilities dinsa. Dan haka yayi niyyar daukan kaso mai tsoka a cikin ajjiyarsa ya siya musu gida. Shi nashi ginin can wait.
Ya daga wayar yana cewa "an samu kenan" mutumin yace "an samu oga Hassan, naga kamar yayi dai dai da bukatar ka sai dai in ka samu lokaci sai inzo muje in kai ka ka gani kafin ayi finalising"