Showing 30001 words to 33000 words out of 300844 words

Chapter 11 - Tagwaye Book 1 Hausa Novel Complete

22 Dec 2024

2036

Watakila ma ba musulmi bane ba".

Ruqayyah tayi ta saka ran taji Baba ko Inna Ade sunyi mata maganar abinda bakuwarsu tace amma sai taji shiru, in ta taso da maganar sai Inna Ade tayi saurin chanja topic saboda bata son sauran yaran su san da maganar, Ruqayyah ta cika tayi ta kumburin ta sai duk suka shareta saboda dama ta saba fushin ta ita kadai.

Sai da dare bayan duk yara sun watse sannan Inna Ade tace wa Baba "Baban biyu ka fahimci inda maganar bakuwar na ta dosa kuwa? Ka gane abinda naso na gane?" Yayi ajjiyar zuciya yace "na fahimce ta uwar biyu, kawai dai nayi shiru ne kuma kema ina son ki cigaba yin shiru akan maganar saboda bama bukatar wani yazo ya gaya mana cewa mutanen nan ba sa'annin auren yayan mu bane ba, bana fatan yiwa yayana aure a gidan da za'a wulakanta su duk da dai su wadannan naga kamar ba irin sauran masu kudi bane ba, ni nafi son suyi karatu su nemi nasu na kansu ba wai su jingina da wani ba. Sannan kuma ita matar nan zata iya yiwuwa kawai nata ra'ayin ta fada bawai ra'ayin shi yaron ba, in yaron yana so da kansa zai zo ya nema. Dan haka mu bar maganar, muyi ta addu'a,idan yazo ya nema din kuma an samu daidaito tsakanin sa da yarinyar sannan mun bincika mun tabbatar da nagartarsa to alhamdulillah sai mu bashi ita" Inna Ade tace "to Allah ya shi ge mana gaba, ni ba wai maganar auren ce ta bani tsoro ba halin Ruqayyah nake gudu,dama Sumayya suka ce da sauki"

Baba ya kalle ta kawai ya dauke kai, amma maganar ta ta tsaya masa a rai. Tabbas gaskiya ta fada, duksu biyun yayansa ne amma suna da banbanci kwarai da gaske ta fuskar halayya.

A ɓangaren su Aunty bayan kuwa bayan sun koma gida su Nafisa suke ta zancen gidan. Hassana tace "Amma Aunty mutanen nan daga ganinsu suna da hali na gari, kinga yadda suka tarye mu da kulawa da karramawa? Basu da kudi amma tabbas suna da kamala" Safiyyah tace "suna kuma da addini, yanayin shigarsu da nutsuwar ƴaƴan ta birgeni" Khadijah tace "da tsaftar gidan, har muka fito banga datti ko digo ba, kayan sawarsu sun tsufa amma babu datti a jikin su" Nafisa tace "gasu kyawawa, kai twins din nan akwai kyau. Wato in suka samu kulawa sai an jinjina irin kyawun da zasuyi" Zulaihat tace "a yanzun ma ni banga alamar yunwa a tattare dasu ba, basu da rama kuma basu da datti. Hoda kawai suke bukata da jambaki" duk suka kwashe da dariya. Aunty tace "nima nutsuwa da tarbiyyar yaran ta bani sha'awa. Allah dai yasa yarinyar nan rabon Hassan ce dan ni kam nayi masa sha'awar ta sosai. Gata yarinya karama yadda juya ta ya kuma tarbiyyan tar da ita yadda yake so"

Wannan yasa washegari tana tashi ta kira Hassan, Hussain ni ya dauki wayar suka gaisa sannan ya bawa Hassan da yake kwance yana ta juyi. Ya karba ya gaishe ta sannan tayi masa bayanin zuwan da tayi gidan su Ruqayyah

"Jabir ne ya karbo min address din a gurin police, gaskiya Hassan naji dadin ganin yaran nan da iyayensu. Alamu na zahiri sun nuna cewa mutanen kirki ne, badini kuma Allah ne ya barwa kansa sani" Hassan ya shafa sajen fuskarsa yana murmushi a ransa yana jin kamar an yaye masa wani nauyi yace "naji dadi sosai Aunty, naji dadi da kika yaba dasu" sai kuma ya danyi shiru cikin jin nauyin Aunty yace "kin ganta?"

Sai da tayi dariya sannan tace "na gansu, su biyu ne ita da husainar ta. Kamar su daya komai nasu daga, daga dukkan alamu basu kammala secondary school dinsu ba dan ba gansu da uniform" ya gyada kai yana tuno fuskar Ruqayyah sanda take daure masa ciwon sa,ya lumshe ido ya bude yace "Nagode Aunty" suka yi sallama ya ajiye yana kallon Hussain take ta zabga masa harara, ya dga kafada yace "me nayi?" Hussain ya gyara zama yace "sai wani murmushi kake yi wai kai nan kayi budurwa. A dai bi a hankali" Hassan yayi dariya har sai da yaji wuyansa ya amsa sannan yace "oho dai" Hussain yace "wai yarinyar da ka hadu da ita cikin mintinan da basu wuce talatin ba, sannan kuma cikin tsakiyar dare ita ce kake ta kwarara wannan murmushi saboda ana yi maka maganar ta" ya danyi dan karamin tsaki.

Hassan ya mike daga kwanciyar da yake yi ya hade rai yace "ai ba mintuna ko lokacin da muka hadu ɗin ne madu muhimmanci ba, abinda tayi a cikin mintinan shine abu mai muhimmanci, ni na kasa gane kan ka Hussain, yarinyar nan fa rayuwata ta ceta, I owe her my life. Amma maimakon ace ka kasance mai farin ciki da ita sai kake furuci masu daci a kanta. It hurts me wallahi, and it makes me question matsayi na a gurinka"

Hussain ya ajiye magazine din hannunsa yace "haka ne, I should be grateful to her, but bansan me yasa ba nake jin something odd about her ba, kawai ji nake sam ban yarda da ita ba" Hassan yayi murmushi yace "kamar yadda nima farkon soyayyar ku da gimbiya nake jin ban yarda da ita ba, gashi yanzu na fara sabawa da ita har muna zama muyi hira, kamar yadda na yarda da gimbiyar ka kaima one-day zaka yarda da tawa gimbiyar".


Sai da suka yi sati uku a can sannan suka dawo Nigeria, a lokacin Hassan ya warware sosai har ya maida kibar sa kuma yayi haske abinsa, Hussain wata daya yaso suyi amma Hassan yaki yarda dan shi Allah Allah yake yi su dawo yaje yaga Hassanar sa. "Kar tayi fushi, tace naki zuwa"

Ai kuwa Ruqayyah tayi fushin, tun tana kirga kwanaki har ta koma lissafin sati, gashi iyayenta sunki kwata kwata suyi mata maganar, Sumayya ma ta share ta. She became very edgy daga an taba ta sai bala'i har yan gidan duk suka share ta suka daina shiga harkarta. A haka har suka kammala neco dinsu, shikenan suna daina zuwa makaranta tunda ba waec zasu yi ba. Wannan zaman gidan shi ya cigaba da frustrating Ruqayyah, har mafarkin Hassan take yi wai ya dawo daga kasar waje ya siyo mata sabuwar waya mai kyau ƴar yayi.

A ranar kuwa ya dawo kasar, washegari ya taho ganin ta. Drivern da ya kawo su Aunty shi ya saka ya rako shi gidan tunda ba zai gane ba. Suna yin packing yabi katangar gidan da take rabi ta langa langa da kallo yana tuno memory din ranar nan sai ya jinjina hikimar ubangiji, ya tuna sanda ya shiga gidan ta tsakanin langa langa ya kwanta a toilet din gidan yana birgima saboda azabar ciwon da yake ji a kafarsa da jinin da yake zuba a wuyansa.

Ya tuna sanda ta shigo toilet din tayi fitsari a gabansa ba tare da tasan yana gurin ba, yayi murmushi tare da alkawarin wata rana sai ya tsokane ta da abin, ya lumshe idonsa yana misalta yadda zata ji kunya ta kifa kanta a kirjinsa tana cewa "kaga bana so, ka daina tsokana ta, Allah zan rama nima" ya sake yin murmushi shi kadai yana girgiza kai, yasan da Hussain yana kusa dashi da sai ya dungure shi yace masa "idiot".

Drivern ne ya fita ya nemo yaro sannan ya tambayi Hassan "oga Hassan wa za'a ce ana kira?" Ya sake murmushi kamar idiot sannan yace "Hassana. Kace Hassan ne yazo yana son ganin Hassana" yaron da drivern duk suka yi dariya sannan yaron ya shiga ciki.

Wanke wanken kwanuka take yi tana mitar Zunnur da ya ki cin abinci dare da Sulaiman ya zuba nasa daban ya kara mata kayan wanke wanke. Sumayya tana dora wa yara karatu akan baranda Inna kuma tana ruɗa tuwo. Yaron ya gaishe da inna sannan yace
"Inji wani mai babbar mota yace wai Hassana tazo inji Hassan"

Karaf a kunnuwan Ruqayyah, ta saki kwanon hannunta tana juyo wada sauri idanuwa a waje, suka hada ido da Inna, sai ta mike da sauri tana wanke hannunta da ƙafafuwan ta. Inna ta ajiye muciyar hannunta sannan ta bita dakin, kafin ta shiga har Ruqayyah ta birkito dukkan kayan su na cikin bagko tana neman wadanda suka fi ko wanne kyau. Inna ta tsaya tana kallonta tace "gashi kuma baban ku baya nan ballantana a tambaye shi izinin ki fita gurinsa"

Ruqayyah ta yar da rigar hannunta ta juyo idonta har ya ciko da kwalla "Inna yanzu kuma jira zai tayi a waje har sai Baba ya dawo? Baban da bamu san lokacin da zai dawo ba? Inna tunda ke kina nan ki bani izinin mana, in Baba baya nan ai ke ce wakiliyarsa" Inna Ade ta girgiza kanta tana tabbatar wa da kanta hasahen da tayi akan Ruqayyah dai dai ne, sai dai kuma abinda Ruqayyah ta fada gaskiya ne, bai kamata abar bakoa waje yana jira ba kuma ita bata da waya ballantana ta kira baban biyu ta gaya masa labarin zuwan bakon.

Sai tace "bana son ku tsaya dashi a waje, bana son kuma ku zauna a cikin motarsa, gashi kuma bamu da soro ballantana ya zauna. Abinda za'a yi bara in sallami yaran nan sai ayi masa shimfida a tsakar gida ku zauna ku gaisa, dake da Sumayya zaku je. Ni kuma zan zauna a daki. Ki kiyaye ni Ruqayyah, in kika nuna masa halinki wallahi xan saka baban ku ya gaya masa kar ya sake zuwa gidan nan" Ruqayyah tayi saurin gyada kanta, ta yarda, ta yarda da ko wanne sharadi in dai za'a bata wannan chance din. Wannan chance ne one in a million ta samu kuma ba zata yi wasa da shi ba.

Tana cikin shirya wa Sumayya ta shigo itama ta wanko fuskarta, duk basu yi kwalliya ba sai mai da suka shafa suka saka kaya da dogayen hijabs dinsu. Sannan Sumayya ta shimfida tabarmi guda biyu a kasan bishiya sannan ta shimfida sallaya a saman tabarma daya. Ruqayyah kuma ta dauko sabon kwanon shan ruwan Inna Ade ta debo ruwa ta ajiye sannan ta dora kofi akai.

Sumayya ce ta fita kiransa. Yana motar dai a zaune suna hira shi da drivern, lokaci zuwa lokaci yana kallon kofar shiga gidan zuciyarsa tana son ganin fitowarta. Sai ga Sumayya ta fito, idonta ya sauka kan motar amma da yake tinted glass ne bata hango na ciki ba amma shi ya hango ta, yaji bugun zuciyarsa ya karu, ya dakata da hirar da yake yana samun damar kare mata kallo tare da tunowa da waccan fuskar da ya gani ranar nan. Abinda ya fara fahimta a tare da ita shine yadda take tafiya cikin nutsuwa. Ta tsaya a gaban motar cikin yanayin rasa abinyi. Sai kuma tayi sallama tare da knocking window din. Yaji dadin sallamar da yaji tayi. Ya sauke glass din window din a hankali sannan ya sauke idonsa cikin nata. Tayi murmushi mai fadi, ko ba'a gaya mata ba ta san shine wannan duk da cewa ranar nan bata wani ga fuskarsa sosai ba.

Ta dan durkusa kadan tace "ina yini, sannu da zuwa" ya jefa mata best smile dinsa yace "lafiya lau....." Sai ta katse shi "ammmm an ce ka shigo ciki, Ruqayyah Hassana tana ciki" ya kankance idonsa yana kallonta cikin mamaki, sai ta danyi yar dariya tace "ni sunana Sumayya...." Yace "Hussaina?" Ta daga masa kai ya bude kofar motar ya fito ya na kallon ta yace "gwara in gane ki sosai kar aje ayi min chanje"

ta sake dariya, ya fahimci tana da fara'a sosai tace "baza ayi maka bama, ka kwantar da hankalinka" suka jera yana cewa "amma kuna kama sosai fa" tace "haka ake cewa, amma if you get to know us zaka gane banbancin mu" ita ta fara shiga sannan shi, abinda ya fara lura dashi shine tsaftar gidan da kuma alluna alamar ana koyar da karatu a gidan. Sai kuma yaga shimfidar da akayi masa sannan yaji kamshin tuwon da yake kan wuta. Ya zauna akan shimfidar sannan Sumayya ta durkusa ta sake gaishe shi, ya amsa mata cikin kulawa sannan ta tambaye shi mutan gida.

A lokacin Ruqayyah ta fito daga dakin su, kanta akasa, hannayenta a boye a cikin hijab dinta, fuskarta cike da wani yana yi mai wahalar fassara. Tun da tayi taku na farko taji idonsa ya saukaa kanta, sai taji wani irin yanayi ya lullube ta taji abin duk ba yadda tayi tsammani bane ba, taji ta kasa dago kai ta kalle shi, taji kuma tana son ta kalle shi din.

Kan daya tabarmar taje kusa da Sumayya ta zauna tare da gaishe shi murya can kasa " ya jikin? Allah ya kara lafiya" ya dan kalli dakunan d aduke gefe, ya san akwai mutum a cikin dakin dan haka dole yayi ajjiyar kalamansa sai wani jikon kuma. Amma shi kam yasan zuciyarsata tafi ga wannan yar karamar yarinyar da take kokarin gaisheshi. "Ya naki jikin? Ina fatan ranar nan baki ji ciwo ba" ta girgiza kanta tace "babu ciwo, Nagode" ya sunkuyo yana kokarin kallon fuskarta sai ta kara jawo hijab dinta ta kara rufe fuskar, ya danyi murmushi mai sauti yace "kin gode da me?" Tace "da ka damu dani har ka tambayi lafiya ta" yace "lallai ke ɗin ta daban ce tunda har zaki yi min godiya bayan nine ya kamata inyi miki godiya. Ki sani Hassana, bana jin akwai abinda zanyi miki wanda zai nuna irin godiya ta gare ki, duk abinda zanyi kwatanta wa ne kawai amma ninba zan iya biyan ki ba, Allah ne kadai zai biya ki. Ina kuma fatan ya biya ki da aljannar firdausi"

Sumayya tace "ameen, tare da mu baki daya" ya sake kallon dakin yana feeling uncomfortable, akwai maganganu daya ta tsarawa tun a India amma duk ba zai iya fadin su ba a wannan setting din, dole ya bar wannan ziyarar a matsayin ta godiya kadai in yaso in ya kuma xuwa ya fara kafa gwamnatin sa. Amma duk da haka zai gwada ko dan kadan ne, at least dan asan inda ya dosa.

Ya kalli Sumayya yace "kinga har na gano banbancin ku da Hassana ta" Sumayya ta bude ido tace "menene banbancin?" Yace "Hassana ta ta fiki nutsuwa, ta fiki kunya tunda gashi nan ta kasa kallona har yanzu kuma ta kasa bari in kalli fuskarta. Ki roka min ita ta kalle ni ko da sau daya ne kar ta saka yau in manta hanyar gidan mu in dawo nan in kwana"

Sumayya tayi dariya tace "in kai ka manta drivern ka aishi ba zai manta ba" ya dafe kai yace "haka ne fa. To amma ai na kasa bacci ko? In banyi bacci ba kuma kinga ba zan samu karfin da zan dawo gobe in tambayi Baba ya bani izinin fara zuwa zance gurinta ba" Sumayya ta sake dariya, Ruqayyah ma ta danyi dariya a cikin hijabin ta, tana kallon saitin fuskarta ta cikin hijab din yace "kuma na sake gano wani banbancin naku, ta fiki kyau, dan na hango dogon hancinta ta jikin hijab" Ruqayyah tayi sauri ta kuma jan hijab din gaba yadda fuskarta ba zata fito ba.

Yayi gyaran murya yace "abinda duk nake nema zan iya cewa na same su gabaki daya a gurin ki Hassana. Addini, tarbiyya, kunya, nutsuwa, kyau duk kina dasu. Ni na riga na samu mata Ruqayyah in dai kin amince kina sona ni da gaske nake aurenki zanyi in dai har iyayenki zasu bani ke" ya sake rage murya yace "amma ai ba zaki amince ba in nayi miki, ba zaki gane nayi miki ba kuma sai kin kalle ni" Sumayya ta kuma yin dariya, sai yaga tana tuna masa da Hussain ta bangaren fara'a. Sai ya samu kansa da fara yi mata hirar Hussain.

Ruqayyah ta dan bude fuskarta kadan ta mike ta zuba masa ruws a kofi tace "ga ruwa, ka sha" ya karba yana cewa "nagode sosai" sannan ya kalli Sumayya yace "kinga inda aka damu dani an fahimci ban sha ruwa ba, ke kuwa sai magana kuke saka ni" Sumayya tace "to bara in tashi in tafi in ya so sai kuyi hirar kurame tunda na fahimci ba magana zata yi maka ba" ya shanye ruwan ya ajiye cup din yace "kiyi zamanki, nine dai zan tafi. Ki mika min gaisuwata a gurin Mama sannan ki yi kokari gurin kafa min gwamnati na, ki fara da Foundation mai kyau dan ginin da nake so inyi na har abada ne"

ya mike sannan yace "in Baba ya dawo ki gaishe min dashi sannan ki gaya masa in babu damuwa gobe da kamar wannan lokacin zan dawo ina son magana dashi" ta amsa masa da insha Allah, sai ya dauko daurin kudi ya ajiye akan shimfidar yace "gashi ki sayi sweet, dan naga alamar kina da kwadayi"

Ranar Ruqayyah bata iya bacci ba. Tana ta sakawa da warwarewa.

Washegari ya dawo kamar yadda yayi alkawari. Baba kuma already yana zaune yana zamn jiransa kuma ya yanke shawarar abinda zai gaya masa, danda aka aiko ya zo sai Baba ya saka Sulaiman ya shimfida musu tabarma a waje daga gefe inda mutane ba zasu dame su ba, sannan ya fita gurinsa.

Ganin haka yasa Ruqayyah ta kira Zunnur ta tambaye shi a inda suke, ita kuma ta tafi dai inda suke daga cikin gida tayi shimfida ta zauna tana yanke farcenta. Kawai haka nan taji zuciyarta tana son taji maganar da zasu yi.

A waje Hassan ne tare da Jabir, yaso Hussain yazo du taho tare amma sai ya kirkiri wani excuse ya kawo amma Hassan ya fahimci zuwa ne baya son yi kuma yaji babu dadi. Bayan sun gaisa cikin mutunci da girmama juna, sun kuma yo doguwar godiya a bisa taimakon da aka yiwa Hassan a gidan sai Jabir ya shigar da maganar kudirin Hassan na neman izinin fara neman auren Ruqayyah.

Baba ya masu kudurin su cikin nuna jin dadin wannan karramawar amma kuma sai yace "amma wani hanzari ba gudu ba, ni


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login