Showing 24001 words to 27000 words out of 300844 words

Chapter 9 - Tagwaye Book 1 Hausa Novel Complete

22 Dec 2024

2032

gardi a dakina. Jama'a ku taimaka min jini ne a jikinsa"!

Ko daga bacci aka tashe su sun san muryar Ruqayyah ce. Inna Ade tace "Ruqayyah! Baban biyu wannan ai muryar Ruqayyah ce. Daga ina take wannan ihu? Yaushe ta fita daga gidan nan?" Baban biyu ya shige ciki yana tallafo fuskar Hassan, kallo daya yayi masa ya gane shi, ya kuma gane dankwalin Ruqayyah da yake daure a wuyansa. A take ya fara guessing abinda yake faruwa. Amma kuma hankalin sa ya tashi saboda fahimtar hadarin da Ruqayyah take ciki.

Hassan ya bude ido a hankali yana kallon baban biyu, cikin magagin ciwo yace "Hussain? Ku kaini gurin Hussain" shima kuma yaji muryar da take ihun daya cika gabaki dayan unguwar. Yaji kamar yasan muryar, kamar muryar wacce tace zata taimaka masa, wacce ta haura katanga saboda shi, saboda Allah tace zata taimaka masa ba dan komai ba. Ya fahimci mai take cewa a ihun nata kuma ya gane mai take yi, tana kiran mutanen da suke nemansa ne away from him and toward her, tana jawo danger away from him and unto herself. So selfless, so brave.

A lokacin suka ji mutanen da suka shiga makota suna nemansa sun fito da gudu sun tafi inda take ihun. Hassan ya runtse idonsa, Inna Ade ta saka kuka "wayyo Allah na, wayyo 'yata". Sai suka ji ta daina ihun, sannan kuma suka ji karar harbin bindiga, karar data cika unguwar baki daya.

Sumayya ta kwalla kara "Hassana!!!" Hassan ya maimaita a hankali "Hassana!" Yaji sunan ya zarce zuciyarsa ya zauna a gurin da wani abu bai taba zama ba. Sunan mahaifiyarsa ne, sannan kuma female version of his own name. Ya tuno fuskarta sanda ta durkusa tama daure masa ciwonsa. So Young, so beautiful, so brave, so selfless. Sai yaji a ransa cewa zai iya bayar da tasa rayuwar saboda ita, me yasa ya gudu har ya shigo gidan nan ya saka yarinyar nan in danger? Me yasa bai tsaya kawai mutanen can sun harbe shi kowa ya huta ba? Ya fara addu'a a hankali "ya Allah indai wani zai mutu Allah ka dauki raina ka bar yarinyar nan. Allah ya bani dama da kuma ikon kwatanta sakawa yarinyar nan da kwatankwacin abinda tayi gare ni. Allah ka .........."

A lokacin suka ji jiniyar police ta cika unguwar, sai kuma harbe harben bindiga ya biyo baya. Sannan kuma shiru. Shiru except for kukan Sumayya da Inna. Sai kuma kamar daga sama suka ganta ta durgo daga katanga. Duk suka juya suna kallonta ita ma tana kallonsu. "Hassana?" Baban ya fada. "Hassana" Hassan ya maimaita yana mika mata hannunsa kamar mai kiranta zuwa gare shi. Ta taho straight ta durkusa a gabansa tace "it is okay, yan sanda sun kama su. It is over"

*************************************************************************************************

Hassan ya sauke idonsa daga kallon agogon daya kafawa ido kusan mintina ashirin da suka wuce, ya gaji da kallon kofar ya koma kallon agogo kuma zuciyarsa tana bugawa tare da kowanne bugu na hannun agogon. It is already after 3am. Tun 1am yake zaune a guri daya yana jiran shigowar Hassan kamar yadda kidnappers din suka yi mishi alkawari "zai zo gida da ƙafafuwan sa" they said, but he was a fool to believe them. Ta ya akayi ma ya yarda da maganar barayi? Barayin ma na mutane.

Ya cire hular sa ya ajiye a gefe, duk ta dame shi ciwo take sakawa kansa yana yi. Ya cire agogon hannun sa shima yayi jifa dashi, ji yake komai ya fita daga ransa dan uwansa yake so ya gani, gabansa faduwa yake yi, ji yake kamar ya dora hannu aka yayi ta rusa kuka amma kuma sai ya tuna da cewa shi fa Hussain ne. Jarumi ne shi.

Sanyi yaji ya fara ratsa shi, irin sanyin da yake kadawa idan assuba ta gabato. Ya lumshe idonsa sai yaji wani ruwa ya zubo daga idon nasa zuwa kan kuncinsa. Yayi sauri ya goge. Ba zai iya tuna ranar da ya taba yin kuka ba. But he can't take it anymore. He just can't allow himself to think, baya son yayi imagining wani abu ya faru da danuwansa, yayi komai da suke bukata ya cire police ya kai musu kudi shi kadai yayi isolating kansa duk a banza? For the first time in his life da yayi abu with care kuma shine zaiyi failing?

Wayarsa tayi kara a gefensa, ya juya slowly yana kallon screen din "commissioner of police" ya gani. Innalillahi wa inna ilaihir rajiun, ya fada ya sake fada, sai da kiran ya katse wani ya sake shigowa sannan ya dauka. Bai iya yin magana ba. Commissioner yace "yalllabai albishir nazo dashi. Mun samo Hassan" ya fada muryar sa cike da farin ciki.

Wani sanyi ne ya taso daga kafafuwan sa ya dire har kansa. Sannan kuma wani dumi mai dadi ya ratsa zuciyarsa da kwakwalwar sa ya fara saisaita masa tunanin sa. Ya mike tsaye "a ina? Yana ina? Lafiyar sa kalau? Is he okay?" Ya jera tambayoyin da suka saka commissioner din yin murmushi sannan yace cikin kwantacciyar murya "dan uwanka yana raye, kuma alhamdulillah mun samu nasarar kama barayinsa, sannan mun karbo maka kudinka daga hannun su" cikin zakuwa Hussain yace "bar maganar barayi da kudi, ina Hassan yake?" Commissioner yace "muna asibiti yanzu tare dashi. An shiga dashi theater room" Hussain yace "asibiti kuma, wani abin ya same shi ne?" Commissioner yace "a'a, kawai dai ya danji ciwo ne kadan, but it is not that serious. Na kira kane saboda nasan zaka so a fito dashi kana gurin, shima kuma nasan zai so yana fitowa ya ganka" Hussain yayi murmushi, rabon da yayi murmushi tun sayi daya daya wuce "na gane. Nagode. Gani nan zuwa".

Ya ajiye wayar yayi kamar zai je dakinsa sai kuma ya fasa ya koma dakin Hassan ya dauko key din mota ya fito ya dauki hularsa ya fita da sauri, har yaje gaban mota kuma sai ya koma cikin gidan da sauri ya hau saman Aunty yana bin kofofin kannensa yana knocking cikin sigar kida, kudan duk a tare suka fito tunda ba wani dogon bacci suke samun yi ba. Fuskarsa kawai suka kalla suka rude da ihun murna, gabaki daya suka rungume shi shima ya bisu daya bayan daya yana rungume wa.

Aunty ta fito tana kallonsu, sannan ta daga hannunta sama tace "alhamdulillah. Allah mun gode maka".

Sanda aka fito da Hassan, duk family dinsa suna bakin kofa suna jira amma shi bacci yake saboda allurar baccin da akayi masa. Wuyansa a nade da bandage, kafarsa ma haka. Aunty ta fara sharar hawaye, Hussain yana kallon doctor yace "akace min minor ne ciwon, menene haka?" Doctor yayi murmushi yace "ba wani abu yallabai, bawai ciwon bane yasa kuka ganshi haka wahalarda yasa ne, daya kwana biyu zai warware, harbinsa akayi a wuya amma bullet din bai shiga ba gogar gurin kawai yayi. Kafarsa kuma targade ne sai kuma ciwo da yaji a kafar itama. Duk it has all been taken care of".

Da kyar Hussain ya iya sakin hannun Hassan yaje yayi sallah, yana dawowa ya koma ya zauna ya cigaba da rikon hannun. Sauran yanuwan a zagaye dasu. A haka Hassan ya farka ya gansu.

Daya bayan daya yake binsu da kallo, duk suma suna kallon sa da murmushi a fuskokin su har ya iso kan Hussain. Ya lira da yadda yayi baki ya rame, ya danyi masa murmushi yace "hello bro" Hussain yace "hi bro. Welcome back" Hassan yace "na dawo gida, amma kafin in dawo na samo matar aure a inda naje" duk suka bude ido suna kallonsa cikin mamaki. Hussain yace "matar aure kuma?" Safiyyah tace "tare aka kama ku?" Khadijah tace "a ina take?" Nafisa tace "ya kamannin ta suke" Zulaihat tace "yaya sunanta?"

Yayi murmushi yana kokarin mike wa zaune yace "no ba tare aka kama mu ba, a can dai unguwar take, she is the most beautiful, brave, and selfless person I have ever met" ya juya yana kallon Hussain yace "sunanta Hassana and she saved my life".


Anan muka kawo karshen free Episodes na littafin tagwaye. Anan ne kuma muka fara labarin. Wannan tafiyar ba irin sauran ba ce ba, wannan tafiyar da zafi muka debo ta.

Ga dai Hassan da hassanar sa (Ruqayyah, Rukee) ga kuma Hussain da gimbiyar sa, sannan ga Sumayya a gefe.
Shin yaya wannan tafiyar zata kasance?
Shin cikin wadannan su wanene iyayen Amir?
Shin menene ya faru har Amir ya samu kansa a yashe a kofar gidan marayu?
Wacece matar data kira Amir zata bashi labarin iyayensa kuma menene alakar sa da ita?
Yaya zata kare tsakanin su?

Zaku samu amsar wadannan tambayoyin in kuka turo kudinku ₦300 ta account
GT Bank
Account Name : Nafisa Usman Tafida
Account Number : 0139433741

Sai su turo shaidar transaction din ta hanyar WhatsApp zuwa wannan layin
08067081020

Wadanda basu da account zasu turo katin MTN na ₦300 zuwa wannan layin
08067081020.

Nagode, sai na jiku.


Episode Eleven : The two sides of a coin

Hussain ya kama Hassan yana mayar da shi kwance, yana cewa "wannan Hassana ba dan sunan ta ba da na fara kishi da ita tun yanzu" Hassan ya runtse idanunsa cikin nuna jin zafin ciwon wuyansa yace "ba zata kula ka ba, komai neman maganar ka ba zata kula ka ba. Ita kamilalliyar yarinya ce" Hassan ya nade hannayensa a kirjinsa yana bata rai yace "me kake nufi da kamilalliyar yarinya ce? To waye kuma ba kamilallen ba?" Aunty ta matso tana dariya tace "zaku fara ko? Hussain sai kace ba kai bane mai kuka kana neman Hassan ba shine daga dawowarsa zaku fara musu. Ni na dauka in ya dawo ba zaku kara rigima ba" duk suka yi murmushi Hussain yace "ban fa yi kuka ba Aunty, kar ki sa ya raina ni mana. Kawai dai ina mamakin yadda mutum zai shiga irin halin da ya shiga sannan the very first thing da zai fada bayan ya dawo hayyacin sa shine wai ya samu mata" ya karasa maganar yana rike baki "mata fa? Hassan din? Ni na dauka duk macen da Hassan zai kira da mata sai tayi passing through different stages na gwaji. Ko guda daya ta fadi kuwa to an cire ta a list amma wannan cikin dare daya har tayi passing? Ni nafi tunanin zafin ciwo ne ya saka shi wannan maganar" Hassan yana daga kwance ya harare shi yace "ko kakan zafin ciwo ba. Nasan abinda nake yi kuma nasan duk mutumin da zai saka rayuwarsa on the line to save someone da bai taba gani ba a rayuwarsa to kuwa tabbas dole a kira shi dukkanin suna na gari da yake available. Like I said, she saved me. Nasan Allah ne mai raya wa kuma na yarda Allah ne yasa ka zan ga yau, zan ganku, amma through Hassana taimakon Allah yazo min. Don't you think this means something?"

Aunty tayi replacing kujerar da Hussain ya tashi daga kai tace "ban san yarinyar da kake magana akanta ba, amma na san ka Hassan, nasan kuma duk abinda ka zaba kuma har ka yaba dashi to kuwa abu ne mai kyau. Dan haka bani da kokwanto cewa duk sanda naga yarinyar nan nima zan yaba da ita"

Hussain ya kalli agogon sa yace "don't stress yourself da tunani, rest, ka koma baccinka. Ni zan je gurin police suna ta jirana tun dazu suna so suyi briefing dina akan case din. In ma dawo kuma zan samu doctor muyi maganar fitar da kai waje dan kafi samun cikakkiyar kulawa" daga haka ya bar dakin. Zuciyarsa tana cike da farin cikin dawowar danuwansa amma kuma bai san dalilin da yasa yaji hankalin sa bai kwant da maganar da dan'uwan nasa ya dawo da ita ba.

A gurin police ne ya kuma samu wani shock din, shock din ganin Salisu a zaune a kasa duk rigarsa jini, kafadarsa daya a nannade da bandage. Yana ganinsa yace "Salisu? Me kake yi anan? Ciwon menene kaji haka a hannunka? Salisu ya sunkuyar da kansa kasaya kasa dago kai su haɗa ido. Hussain ya kalli dan sandan da yake wajen yace "me yake yi anan gurin ga kuma ciwo nan a jikinsa? accident yayi? A kaishi asibiti mana" police din ya saka kafa ya daki Salisu a bayansa yace "juya ka bashi labarin a inda kaji ciwon jikinka?" Salisu ya sake dunkule wa guri daya sam ya kasa dago kansa. Hussain ya rike dan sandan da sauri "ya zaka dake shi, ga ciwo a jikinsa ga kuma duka? Wanne irin police ne kai?" A lokacin commissioner ya fito, suka zazzauna shi da Hussain suka gaisa ya kuma taya Hussain murnar warwarewar lamura sannan yace "ka san wancan yaron?" Ya fada yana nuna Salisu, Hussain ya hadiye abinda yaki tafiya a makwogwaron sa saboda fara fahimtar inda maganar ta dosada yayi. Yace "yaron mune, a gidan mu aka haife shi a gidan mu ya taso, a hannun mu yayi karatunsa, a yanzu haka mahaifiyar sa tana cikin gidan mu tana shirya mana abinda zamu bukata in muka koma gida" commissioner ya girgiza kansa yace "am sorry to inform you cewa shine mastermind na wannan kidnapping din" Hussain ya mike da sauri kamar wanda aka yi wa allura, Salisu ya fara kuka yana rarrafe ya rike kafar Hussain "oga Hussain dan Allah kayi min rai kayi hakuri, wallahi sharrin shaidan ne oga Hussain, nayi nadama ba zan sake ba. Ba hali na bane ba ka sani sharrin shaidan ne" Hussain ya saka kafa ya doke shi tare da ja da baya kamar wanda yake gudun ya sake taba shi yace "sharrin shaidan? Salisu? Wannan shine sakayyar soyayyar da muke yi maka ni da danuwana? Wannan itace muguntar da zaka saka alkhairin mu da shi? Dama yanzu duniya har ta kai wannan lalacewar Salisu? Dama yanzu har dan Adam bai mayar da saka alkhairi da mugunta komai ba a duniya? Dama yanzu duniya ta zama babu wanda zaka yarda dashi komai kuwa kyautatawar ka gare shi? Shikenan komai dan adam ya aikata sai ya kira shi da sharrin shaidan. To auzubillahi minash shaidanir rajim. A yanzu mutane sune shaidanun kansu basa bukatar taimakon wani shaidan wajen aikata ta'asa" commissioner ya jashi ya zaunar dashi a kujera yana bashi hakuri. Hussain ya sake cewa "Hassan fa, rayuwar Hassan yayi wasada ita, har harbin Hassan fa akayi ba dan yana da sauran kwana ba da yanzu mun dawo daga sutturar sa" Salisu yace "wallahi oga Hussain bansan zasu cutar dashi ba. Alkawari suka yi min cewaba zasu cutar dashi ba. Nayi kokarin hana su cutar dashi shine suka harbe ni su suka yi min wannan harbin sannan suka bishi" commissioner yace "kadan ma kenan, dama ai karshen irinku kenan. Wadannan mutanen sun saba kashe mutane akan kudin da bai kai wannan yawa ba ma. Ko ba dan ka shiga tsakaninsu da Hassan ba dama kashe ka zasuyi su raba kuɗin a tsakanin su. Kai da tunani kake xasu baka? Kuma su barka da raj ayi tracing dinka ka tona musu asiri? Ai anyi irinka da yawa kuma basu kai labari ba" Hussain ya mike yana cewa "babu hannuna a cikin case dinka Salisu, ban sanka ba daga yau, danuwana ma bai san ka ba. Ko an sallame ka kar kabi koda hanyar gidan mu ce. Babu mu babu kai har abada" Salisu ya fara kuka wiwi yana bada hakuri, commissioner yace "ballantana ma ba za'a sake shi din ba, za'a hada shi da sauran a tura su court a yanke musu hukunci dai dai da laifin su".

Da wannan Hussain ya bar Salisu. Bayan cike ciken takardu da yayi da kuma sauran abubuwa sai ga kudinsa an dawo masa dasu cif ko kwandala bata yi ciwo ba. A ciki ya fitar ya bawa police kaso mai tsokar da yasa duk sai da suka ji sun kasa rufe bakunansu saboda murna, sannan kuma yayi alƙawarin biyan hospital bill din police guda daya daya samu rauni.

A hanyarsa ta komawa asibiti ya kira gimbiya ya gaya mata duk halin da ake ciki, tun daga muryarta ya fahimci cewa tana cikin farin ciki sosai. Shima sai yaji duk damuwar da take ransa tana wucewa tana tafiya tare da sautin dariyarta. Yayi dariyar shima. Tace "kasan wani abu? This is the first time da naji kayi dariya tun ranar da aka dauki Hassan. Lallai ba karamin so kake yiwa Hassan ba, Allah ya bani, ko ince ya bamu ni da matar da Hassan zai aura ikon cigaba da karfafa kaunar da take tsakanin ku" sai yace "kinsan kuwa daga farkawar sa har ya fara xancen aure? Wai ya hadu da wata yarinya ta taimaka masa kuma wai ita zai aura" Fatima tayi dariya tace "anya kuwa Hassan din mu ne ba'ayi mana chanji a can ba? This is something that you would do, not him" yayi dariya yace "nima abinda nace masa kenan. Mr Careful is now not being careful" tace "amma nasan ai ba wai direct kawai za'ayi auren ba. Nasan zasu samu time together su dan fahimci junan su kadan. Hey! Why not a haɗa da namu kawai ayi tare?" Ya danyi tsaki yace "ke ma kin fara biye masa kenan ko? Ni kuma na rasa dalili nine yau nake zama Careful din akan maganar" tace "what happened to the Hussain I know, the Hussain that just go with the beating of the drum, relax and chill"

A asibiti ya tarar Hassan ya kuma tashi, har Aunty ta na bashi abinci a baki yana ci. Ya leka bowl din hannunta yaga fruit salad ne yace "kai da zaka ci abincin da zai saka ka ciko ka mayar da jikinka ina kai ina fruits?" Aunty tace "a yanzu ai lafiya yake nema ba wai kiba ba, yana bukatar alot of vitamin c" Hussain ya shafa kafadar Hassan da fatar duk ta fara yamushe wa yace "and alot of meat. Me suke baka ne a wajen?" Hassan ya doke hannunsa yana hararar sa yace "what I need is a deep bath, in na gaya maka rabona da wanka sai kayi dariya dan haka ba zan gaya maka ba" Hussain ya toshe hanci yace "shi yasa atmosphere din


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login