Showing 120001 words to 123000 words out of 304445 words
ce min. "Akwai matsala ne matar Yarima Salmanu Faris." Girgiza kai nayi nace mishi. "Na gode!" "Yawwa me yasa bakya son daukar number na." "Ina da aiki Please!" Na faɗa ina tashin motar, "kina tsoron Mijinki ne? Ikhlas auren nan anyi shi da wata manufa ne, Sannan mutumin da ya iya ajiye mata irin Nadiyyah Jamil Chiroma, sannan har yau ." Murmushi yayi yana kallon yadda na rud'e don ban tab'a tsayawa da wani namijin ba sai Uwais sannan ina gudun, iyayena su ji wannan labarin na shiga uku da sauri na ja motar, ina isa cikin gida na sauke ajiyar zuciya, na fita daga motar, masu tsaron babban kofar gidan nan suka taso, suna gaishe ni. "Ko zaki taya ni shiga da kayan nan bangaren Mai Babbar daki?" "Haba ranki shi dade, Wajibi ne a kanmu, Allah ya bada zaman lafiya da zuri'a dayyiba!"
Murmushi nayi tare da cewa Amin Ya Allah, sannan muka cikin gidan da kayan. Har parlourn Mai Babbar daki, tana sauraren Tafsirin Sheikh Bin Muhammad, rage karar sautin tayi tana amsa sallmarmu. Ganin yadda ake ta ajiye mata kayan a hankali, zama nayi ina sauke ajiyar zuciya. "Barka da hutawa, Ummi ya Ibada?" "Alhamdulillahi, amma yau kin san kina da aiki kika zauna biyu saura?" Ita dai bata iya ganin abin arzikin mutum. "Kiyi hakuri na tsaya Sallah ne." Na faɗa ina gyara zamana na jingina da kujeran da take kai. Duk sai na kasa magana na tura baki ina jin kwalla yana shirin zubo min, da ta share ni kamar bata damu ba amma ganin ina jan hancina al'amar zan fashe da kuka yasa ta ce. "Wannan kayan albarkan fa?" Tuni na nime kukan na rasa na sake murmushi na ce mata. "Kayan shan ruwa na kawo miki." Murmushi tayi irin na ban mamaki, domin bata taɓa zatan zan jawo mata ba, wani abu da na ƙara fahimta a tsakaninmu shine yadda ni da Mai Babbar daki muka yi mugun shakuwa, idan nace shakuwa ina nufin bata iya jure ganin na dauki fushi ko yayya ta gani shiga niman hanyar da zan manta da abinda ya faru. Abu daya shine kiyayyar da take min da jin zafina, ya juya ya koma kauna da kyautatawa, yadda take kallon kayan cike da kauna yasa na fahimci tana son kayan. Haka na janyo mata su gabanta daya bayan daya. "Mai kitsonki ta tambaye ki, a kira ta ne?" "Sai dai ko gobe!" Na bata amsa. "Akwai mai gyaran jiki da zata zo daga Maiduguri, na bata kudin kayanki ina kina so?" Ta fada tana d'aga lafayya da na saka mata, "Duk abinda zai fito daga gare ki ina so Ummina!" D'ago kai tayi tana kallona. "Ba zaku makara ba?" "Eh mun rage aikin ina zuwa hada aikin zan yi." "Yayi kyau, dama Mai Kano da Bauchi suke saya min kayan shan ruwa tow ban ga ni ba har yanzu shine nace ko sun mata ne, ashe Gimbiyar Zanzabira ce zata kawo min!" Ta fada cikin kulawa, mikewa nayi ina faɗin. "Ummi su Sailuba sun tafi ko?" "Eh!" "Na barki lafiya!" Na mata sallama. Ina isa gidan na samu yaran nan a waje Ijlal ta hana su shiga, Nady bata nan komawa wurin Sarkin kofa nayi nace mishi. "Ta fita ne?" "A'a nima na buga taki budewa, buga kofar gidan nayi amma taki budewa don haka na tura mishi da sakon. *Please ko zaka roki matarka ta bude min gidan na shiga nayi aiki ba don na isa ba* minti talatin a tsakanin sai gashi tare da Mai Babbar daki, suka shigo idan na ji dadin wannan lamarin wallahi nayi karya, muna tsaye suka zo suka buga, Amma Ijlal taki budewa, cikin fushi ya bangaji kofar gidan amma yaki budewa. "Kyale ta, na kira Uwarta!" Kiran Hajiya Mardiya tayi kafin minti arba'in ta iso ita ce ta buga kofar gidan tare da kiran sunanta, sai gata ta fito a guje ta bude tana yatsina fuska. Mai Babbar daki ta kalli Hajiya Mardiya ta ce mata. "Dauki yarki, ku tafi idan ita ce autar Mata Salmanu ya hakura da ita, ka saka a ranka sai ka sake ta." "Ummi a dai hakuri bamu san hujjarta na rufe kofar ba, Amma saki is too early a sake yar shekaru goma sha bakwai zuwa sha takwas." Ya fada yana wucewa cikin gidan, na bi bayanshi Hajiya Mardiya ta rufe ta da duka babu wanda ya bi kansu ina muke da lokacin.
Idan na gaya muku aikin nan sai da ya dauke mu karfe shida da rabi ba zaku musanta min ba, na sadaka aka fara fitarwa sannan aka fitar da na cikin gida, sannan sai namu aka jera a dinning room, kafin asha ruwa na turara gidan da turaren wuta, ni kaina wanka nayi na chaba kwalliya, anan shan ruwa ya turo min sako ga baki yan shan ruwa nan zuwa. Kara gyara ko ina nayi, mun yi abinci kala hudu ne, da na sahur da na daura. Na sallami Sailuba da Wildat, ni kuma na karasa sauran tuwo miyar ayoyo, wanda nayi daga daddawa sai attarubu, sai stew da nayi na naman rago, sai farfesun kaza. Nady ta rigamu zuwa dakin. Ni sai da nayi sallah, lokacin da bakin suka iso na zuba musu kunu da tea asalin ghawa, wanda yaji kayan kamshi, baki ne kusan kuma Family friend dinsa ne. Sai Salim da ya zo jiya.
Haka na zuba musu na debi nawa na bar dakin zuwa dakina. Ijlal ko taji kunyar abinda ya faru ne sai bata fito ba, haka suka ci abinci suka bar gidan kusan rabin hiran da Nady.
Ni dai ban san kome akan turaka ba, na dai gama na asuba, sannan na wuce dakina na kwanta, gajiyar exam da aiki ya taru min dole na kwanta na kama barci. Cikin barci nake jin wani irin bakon lamari, abinda ya shiga birkita min lissafina, bude idanun nayi a matuƙar razane na kwace jikina daga abinda yake min zuciyata tana wani bugawa kamar mai yin tsere da dawakai, a razane na ke kallonshi. "Why?" Ya tambaye ni, wani razanannen kallo nayi mishi ina kara yi baya. Jikina yana kara rawa, "fitsari fitsari! Nake ji!" Na faɗa da sauri ina sauka a gadon na nufi ban daki. Ai naki fitowa sai da ya buga min kofar. "Ko na shigo ne?" "A'a gani nan!" Na fito ina yin baya kaɗan. "Kin manta cewa, yau kece da miji?" Yadda yayi maganar yasa ni kara rudewa, kamar doluwa haka na koma bakiɗaya na ƙasa fahimtar kome akan maganar da yake, nufo ni yayi da nayi baya tare da dunkule kaina wuri guda. Jikina yana wani irin rawa. "Don Allah kayi hakuri ni ban shirya ba!" Na faɗa ina me damke kaina. Zama yayi a gabana yana kallon yadda na takura kaina a wurin. "Me yasa tow?" "Ni ban shirya ba!" Na faɗa murya na yana rawa. "Na zata nayi miki wani laifi ne kike guduna, Zainab ba kwadayinki kawai nake ba, abubuwa dayawa ina son ki sani a kaina da rayuwata, amma kike kin bani damar haka me yasa tow?" Shiru yayi kafin ya cigaba da cewa. " Ko don ni ba Uwais ba ne? Ni ba matashi ba ne ko don ba saurayi ba neko? Tow ki yi hakuri nayi kuskure sosai, sannan ban san ta inda zan gyara ba. Amma kuma ba zan iya sake ki domin zan iya kashe duk wanda ya kuskura ya kusanci inda kike da kalmar so! Bana jin akwai wani ingantaccen hujja da zai saka na sake ki ko na kyale ki. Amma zan baki wani dama daya da labarina idan kin ga yayi miki tow idan bai miki ba zan iya rabuwa dake amma ba ina nufin na sake ki, ki tafi ba wallahi ba zan iya ba." Wani irin takaici ne ya cika min rai. "Tow me zai saka ka gaya min.....
*Account Details:*
*08130269641"
*5921536136*
*RAMLAT MANGA ABDULRAHMAN*
*Moniepoint MFB*
My book isn't Free! 500N
[7/26, 10:02 Safiya] Ramlat Manga41: 39
Abinda bana bukatar sani, ni barci nake ji!" Na mike zan nufi gadona ya dawo dani sai da na zube a jikinshi. Dauke ni yayi cak ya daura ni a jikinshi yana murmushi. "Gaya min me kike so sani yau ga Salmanu Faris a gabanka." Yadda ya rungume ni da jikinsa yasa ni kasa motsi ina zare idanu. "Me kike bukata sani a kaina." "Me kake ji a kaina?" "Son kasancewa da ke, ina son ki zauna by my side har abada!" "Ni ina son nayi rayuwa kamar kowa me yasa ba zaka barni na fita a rayuwarka ba?" Murmushi yayi ya ce. "Why are you changing the topic?" "Saboda nasan sha'awa ta kake ji taya zai saka na cigaba da sauraren labarinka.?" Hannunshi ya kai cikin rigana yana shafa cikina zuwa cibiyata. Zabura nayi na ce mishi. "Don Allah ka kyale ni." "Zan kyale ki, da gaske ina sha'awarki?" Ya kuma tambayata. "Ina zan sani tunda ka saba da mata biyu ni kuma ban saba ba,balle nace zan iya sanin kome akai!" Murmushi yayi yana faɗin. "Yanzu baki san yadda ake jin dadi ba?" Ya rike bakinshi. A yanayinsa kamar zai yi zafi amma is too cool, yana da kalamai masu sanyi da kwantar da hankali. A hankali na fara ƙoƙarin zamewa, riko ni yayi da kyau. "Na gaya miki wani abu?" Lumshe idanuna nayi a kirjinshi. "Ina jin kamar na cinye ki!" Ya faɗa yana shafa bayana. "Sake don Allah na kwanta!" Na faɗa ina ƙoƙarin tashi daga jikinshi. Gyara murya yayi a hankali ya fara magana kamar yadda ban yi tsammanin zai bude bakinshi ba.
16-2-1999
Ranar sha shida ga biyu shekarar aladari tara da casa'in dai-dai. Wanda yayi daidai da saura wata daya Mahaifina Alhaji Attahiru Shehu Yayari, zai cika shekaru goma sha daya da hawanshi Sarkin Zanzibara, sai dai kuma an samu wasu abubuwan kasancewar haduwar abokai hudu masu karfi da iko!" Shiru yayi kafin ya taune bakinsa ya cigaba da cewa. "Ni Salmanu Faris Attahiru Yayari na kasance na farko a cikin gidan nan, sannan bani da kiriniya irinta sauran Yaran kasancewar daga mai babbar daki zuwa mai Martaba suna mu'amala da ni kamar babban mutum ne, tun kafin na shiga makaranta ake gaya min ni Babban mutum ne da zan iya zama shugaba a cikin garin Zanzabira da sauransu. Haka yasa abokaina Mutane biyu ne Abid da Walid, karamin cikinmu shi ne Uwais shi kusan kanine mana sosai, Daga Abid sai Walid sune abokaina, amma Walid yafi Abid kusanci da ni, yayi da Abid muke abokai ne, a gaban iyayenmu duk na fusu hankali." Murmushi yayi yana shafa kasumbarshi. Kafin ya cigaba da cewa. "Duk da yadda nake da hankalin nan bai hana a cikin gidanmu a tsane ni ba, idan na cire miki Mai Babbar daki da Abba da yan dakinmu kowa kika gani a cikin gidanmu dama daya tal yake nima ya cutar da ni! Saboda wancan throne din." Ya fada yana matse hannuna cikin nashi. "Mun fito makaranta kasancewar muna cikin Yaran da aka saka mu a Elementary school zanzabira, kuma a lokacin makarantar turawa suke koyarwa. Ranar da ba zan manta da shi ba a cikin rayuwata shine ranar da aka dauke ni, domin mun tashi daga makaranta Aneesah ta ce ta yi mantawa sanin cewa Sarkin mota baya jira domin mutum daya daga cikin matan gidan nan ce, yasa yana zuwa baya tsayawa jiranmu yake tafiya, sai na koma cikin makarantar na dauko mata kwandon abincinta domin lokacin zan tafi Aji hudu na secondry school ne, Abid aji uku shi da Walid. Koda da zuwa cikin makarantar da fitowata ban wuce minti uku ba ashe har ya dauke su abinsa. Kuma Mai Martaba ya ce kada na sake dauko hanya na dawo gida ba tare da na jira an dauko ni ba. Haka yasa na zauna ina jiranshi, ga yunwa ga rana haka na ci-gaba da zaman jira, kaina a sunkuye daya daga cikin manya Fada wanda idan na gaya miki shi ya dauke ni zuwa hannun yan ta'addan da Mai Martaba ya kora zaki iya cewa karya nake mishi bai cancanci na mishi kazafi ba, shi ya dauke ni ya ce min. "Ya aka yi ba tafi gida ba?" "Sarkin mota ya zo bai tsaya ba." Na gaya mishi murmushi yayi ya ce muje, Zainab ina gaya miki ne don kada wata rana ki ji an kawo gawata ki ce wani abu kashe ni suka yi ba mutuwa nayi ba. Kawai abinda ya daure min kai me yasa mutanen nan suke jikin Abba kuma suke cutar da shi? Saboda Allah ya fifita shi akansu, Allah ya bashi damar da suke nima shi kuma abokai suka tsaya mishi tare da Ikon Allah. Kawai sai ya wuce da ni dokan daji a madadin gida, lokacin da muka isa ya ce na jira shi zai zo yanzu nan, Zainab tun karfe biyu nake jiranshi har karshe goma na dare yunwa ya galabaitar da ni, nayi suma a wurin. Ban kuma sanin kome ba sai washi gari na bude idanuna akan wani katon mutum mai kamar da dodo, kallona yayi na kalle shi. Tura min abinci yayi. Ban ci ba ya sake tura min da kafa na mai mishi kayansa. Ina kallonshi cikin idanu ban san tsoro ba, ban kuma san fargaba ba. Haka nayi kwana biyu sai ga wannan mutumin ya zo, ina jin muryanshi ya ce su kashe ni domin matuƙar na rayu zan zame musu fita. Basu ki ba amma kuma daya daga cikinsu ya ce musu kashe ni a cikin zanzabira zai tona musu asiri don jinina yana da karfin da yafi na mahaifina sannan abinda suke bukata matukar ina raye dole sai sun rasa akwai wani abu da ya kara min mamaki shine ambaton daya daga cikin abokan Abba da ake ce ya duba cikin su hudun nan akwai wacce dole a sadaukar da jininta, domin kuwa zamu haɗu da ita haka yana nufin ko ban zama sarki ba zan iya hana su samun damar a rayuwarsu sannan suka saka aka fito dani, suna cigaba da jaddadawa junansu tabbas zan zama Sarki amma a lahira don ni masifa ce a gare su. Don taurarin yarinyar da zasu kashe iri daya ne da nawa, kai ita nata hasken rana ce ni kuma wata, ban yarda da maganar ba domin ina ganin karya ce shi yasa ban tab'a ji a raina gaskiya ne ba."
"Yanzu sun kashe yarinyar?" Na tambaye shi a dan tsorace. "Zainab ina niman yarinyar ce ko zan dace domin ba zan bari su kashe ta ba. Zan nime ta dare da rana don na same ta haka ne kawai zai saka na kare ta, sannan sun tabbatar a cikin Yaran abokan Abba hudun nan ne. Kin ga idan na cire Iman da Ikram, zai kasance cikinsu su biyu ne!" "Aure zaka kara kenan?" Na tambaye shi a hasale. "Ina tsammanin haka." Murmushi yayi ya cigaba da cewa. "A daren rana na uku suka fitar da ni zasu kashe ni!" "Ina dai basu kashe ka ba?" Wani irin sansayar dariya yayi ya ce min.."tow dawa kike magana?" "Kuma haka ne fa!" Na faɗa ina sosa kaina.. "Musu ce ta kaure a tsakaninsu. _Cikin tsananin dare wanda ake kira sulisin, wanda baka jin motsin kome sai na kwari da duhu me tsananin gaske! Anyi ruwa gari yayi tsit baka fahimtar kome. Takun mutane ne dasu ka haura goma karti majiya karfi da lafiya. A gaban wani tsohuwar mota suka tsaya! Kasancewar wutar motar tana kunne! Fitowa wani mutum yayi! Ya tsaya a gabansu! Zubewa suka yi a gabanshi tare da dukar kirjinsu! "Mun mika rayuwarmu da mutuwarmu gare ka Gwaska dakare!" Suka fada tare da dukar kirjinsu! "A kashe shi a shafe min tarihinsa" ya fada kafin ya koma cikin motar ya zauna sannan aka tashi motar daga dajin! Sai da ya bar wurin sannan suka mike sannan suka nufi gaban bukkarsu! "Me yasa kuka kama ni? Me kuke so nayi?" "Shamuwa kai da Ungulu ku karasa kome!" "An gama dokaji!" Daukar shi suka yi suka fita sai da suka yi tafiyar awa uku wuraren asuba. Abokin tafiyar ya rike shi da wanda suka dauka ya ce. "Shamuwa idan muka yi haka bamu yi adalci ba! Eh an yi mana laifi amma kashe Yaron nan ba shine mafita ba, mu kyale shi ya rayu amma kada ya dawo Zanzabira!" A razane ya ce mishi Shamuwa ya ce mishi. "Hauka kake? Kashe mu zasu yi!" Dariya ungulu yayi ya maida mishi da cewa "Allah ba zai basu nasara ba! Kashe Yaron ba shine zai bamu yadda muke so ba!" Musu ce ta kaure a tsakaninsu. Yana jin su, "tow me kake so mu yi?" Inji Shamuwa "Yawwa kasan me zamu yi? A gaban kaɗan akwai inda iyakar Zanzabira da kasar Chiyya! Mu san yadda zamu yi da shi!" Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce mishi! An gama_ ina jinsu bani da karfi amma kuma bani da yadda xan iya da su, haka ƙaddarata tazo min. Sai goshin asuba suka wurgani iyakar Chiyya da Zanzabira wanda ruwa ne ya raba mu, Ban san me ya faru ba sai dai wani masunci ya dauke ni nayi jinya na tsawon kwanaki a gidansa, kafin na warke Baba Garba na zauna a wurinsa amma ban jima ba, saboda kashedin da suka min idan ban bar garin ba zasu dirka kan iyayena da kannena da masoyana, na tafi na b'ata a ce na mutu ma, haka na rayu gani a zahiri mutum ne ni amma na mutu a idanun duniya. Nayi tafiya daga wata nahiya zuwa wata nahiyar, ban tsaya a iya Afirika domin na fada hannun yan safara da fataucin mutane ne, ban san iya bakar wahalar da na sha ba, domin na rayu a cikin matsanancin wahala da rashin gata, nayi