Showing 180001 words to 183000 words out of 304445 words
parlourna ta zauna, shiru tayi kafin ta ce min. "Ina son zuwa wurin Abbanki " "By ra'ayin can" wani irin rufewa idanuna yayi ko gani bana yi, cikin wani irin tsawa na daka mata. "Ficce min da gani Uban nawa ? Kin manta malamin tsubu ne? Ko kin manta abinda kika faɗa ne Nadiyyah wallahi idan baki fita ba sai na illataki;" ihuna mijinta ya ji ya fito da sauri jikinshi duk kumfa alamar wanka yake, idanuna sun yi jajjur. "Fitar min da tsiyarki da mijinki bai bani ba bai hana ni na rayu ba, balle kuma da zaki kawo min da sunan zaki ganin mahaifina, wallahi kika sake kika je kofar gidanmu ni da ke ne a gidan!" Kallona yayi sai yanzu ya fahimci asalin rigimar, amma da yake yana son bani haushi sai ya ce mata. "Ki shirya gobe zaki sai tayi abinda zata yi!" "Wallahi baka nemi zaman lafiya a gidan nan ba! Kuma ta je gidanmu sai na mata rashin mutunci sai dai idan ba ta je ba!" Dama daure yake da towel. "Fita a parlourn ki ja min kofa!" Ya fada yana kallona, tsabar masifa ko damuwa ban yi ba, haka ya ja ni har uwar dakina. Ya shiga ƙoƙarin raba reni da ni, domin sake towel din yayi mysterious Giant dinsa ya bayyana. Cak naji lissafina ya dawo dai-dai jin yadda abin yake tsakanin cinyoyina zuwa jikina, sai gani cikin rawan murya na ce mishi. "Allah sai ya saka min domin kasan kana cikin kwanakin Ijlal ne, nan zata zo tana cin zarafina. Nayi magana ka shigarwa matanka saboda ni bani da galihu, idan na nuna ayi min ba daidai ba, sai ka kira Maluma ta dake Ni!" Na fada ina kuka tare da kawar da kaina can gefe. Yasan tayi gaskiya kawai sai ya kyaleta. Ina jin ya mike na cigaba da kwanciyar a wurin ina kuka, har ya fita a bakin kofar ya sami Ijlal zata masa hauka ya ce mata. Nuna mata hanyar waje yayi kuma tasan sarai zai aikata, wannan shine abinda ya faru yau. Duk suka watse suka bar ni can sai ga kiran Yeemar Yazid zai kawo ta, ina cikin murna sai ga Aunty Shukrah itama wai tayi missing dina. Sai naji dadi ya lullube ni, duk yadda Aunty Shukrah taso ta ji me ke faruwa a zamanmu ban gaya mata ba, har gara Yeemar ta san wasu abubuwan. Yarinyar nan mahaukaciya ce, kayan mata tayi ta ciro min a cikin wani jakar da ta zo da shi tana faɗin. "Lokacin bikinki nasan ba a gyara miki zama ba, amma ga wannan ko zaki sha in sha Allah zaki sha mamaki!" Ture kayan nayi ina faɗin. "Ina kika samo kayan nan kada na sha ya saka ni ciwo." Ajiye Sabayar Oum Adnan tayi tana faɗin. "Wannan sabayar ba iya gyara nono yake ba, ba a bawa mace ke ciki saboda zai karawa nonuwarta girma, zai dame ta gaskiya sannan mace mai goyo idan bata PF tow tana sha zaka abin mamaki domin.tana wasa zai wuce mata sai ciki, ke kuwa idan baki da ciki wallahi da pad zaki na yawo idan kina ganin karya ne ki gwada." Ga number Oum Adnan(+234 813 555 1205 only whatsp) Turewa nayi yanayina ya sauya Aunty Shukrah ta dauka tana faɗin. "Yeemar zuba min na gwada!" Haka ta zuba mata, wani bakin ruwa mai kauri Yeemar ta mika min tana faɗin. "Wannan baure, zuma, garin kwakwa garin dabino, mazarkwaila, kanunfari citta cennomin aka da wasu natural Herbs aka hada su bakiɗaya aka dafa, ke har da goran tula. Yadda zai kara gyara jikin mace. Alhamdulillahi domin ina jin daɗinsa." Mai da mata nayi na ce mata. "Wani lokaci sai da nutsuwa ake zaman lafiya har asha bidiri, ni kuma Allah ya gani bani da wannan nutsuwar please ajiye shi idan Allah ya nufa zan gwada amfani da shi, zan tambaye ki ma." Kallona suka yi kowacce tana son jin meke faruwa. "Meke faruwa ne?" Haɗe hannuna nayi wuri guda na ce musu. "Babu kome!" Hawaye na zuba min, "Bestie meke faruwa?" Kuka ne ya kwace min na kifa kaina akan cinyata ina kuka. "Bestie!" D'ago kai nayi ina kallonsu. "Baya sona, baya kaunata kullum niman hanyar da zai kuntatta min yake ban san me nayi mishi ba." Shiru nayi kafin ka cigaba da kukan da nake yi cikin shashekar kuka na cigaba da cewa. "Idan matanshi suka min abu goyan bayansu yake, ni kuma ya nuna ba ni da wata daraja a idanunshi, a wurin Mai Babbar daki kawai nake jin sauki amma daga shi har yan uwansa da Matanshi kamar na tsare musu wani abu." "Bestie ya batun shimfid'a?" Inji Yeemar tana kallona, sannan ta cigaba da cewa." Bestie kin sauke hakkinsa da yake kanki? Idan har kin sauke hakkinsa da yake kanki yake miki haka tow bai kyau ba, bai miki adalci ba idan kuma kin san har yau ke da shi kallon hadarin kaji kuke yiwa juna tow ba makawa Allah zai saka mishi kuma don ya miki haka ban ga laifinsa ba, Bestie shirunki ya nuna min cewa har yau baki bashi damar zama ke ba, kina guduna. Sai kace 19 century Fisabiilillahi ace ka auri mace sama da watanni takwas har wata a bayanki tana da ciki kina gudunsa Uban me yake miki kai amma wallahi kin fadi ba nauyi gara da yake miki haka ko fahimci yadda yake ji!" Sai kunya ta kama ni tare da mugun danasanin mara iyaka. Wai sai ka rasa me zance musu na kare kaina. Aunty Shukrah kallona tayi ta rasa maganar da zata yi can ta ce min. "Da gaske Auta babu abinda ya tab'a haɗa ku?" Sunkuyar da kai nayi ina me haɗe hannuna wuri guda, hawaye na zuba min. Sai kuma suka dawo rarrsshina. "Ko kina da wata matsala ne a jikinki?" Girgiza kai nayi ina jin wani irin kuka na zuwa min. "A'a kawai ban san me yake faruwa ba!" "But baki san me yake faruwa ba kike irin wannan abin?" "Idan yazo muka fara wani abu sai a samu matsala!" Na faɗa ina sunkuyar da kai. "Like how? Me ke faruwa?" A hankali na basu labarin yadda aka fara wasu abubuwan. "Kishi yake damunki!" Kai tsaye Aunty Shukrah ta fada tana kauda kanta, tana me mikewa ta ce min. "Allah ya kyauta, ga wurare inda zaku ji dadin baje hajjarku, idan kuma a gidan ne bakya so sai ku bar gari ya dauke ki zuwa Honeymoon!" Inji Yeemar, girgixa mata kai nayi ta cigaba da cewa. "Wallahi mutumin nan yana sonki haka Allah yayi shi bai da zafi amma da wani ne fyade zai miki shegiya munafuka da duwawu kasa-kasa kamar agwagwa, inji Yeemar, wunin ranar gyara bayin nan suke min tare da gaya min abinda zan yi, magani kuwa akan idanunsu n afara sha, Yeemar ta ce. "Kafin girki ya dawo kanki jikinki zai yi kyau, duk da mutumin nan yana ƙoƙari har maganin infection yasa aka baki fa."
Rike baki Aunty Shukrah tayi tana make yi, a ranar a gidan suka wuni suka ci abincin rana da dare, bayan isha mazajensu suka zo daukar su, nayi ta godiya, kafin Yeemar ta tafi ta tura min wasu DRW, na rasa inda xan cusa kaina da kunya, kafin ta bar gidan ta saka ni tura mishi.
*I know you wanna see me Naked i'm ready👙* na saka mishi da hoton, duk wai tana son a samu kyakkyawar dangantaka amma na san shi ba zai dawo min da sakona ba, bayan tafiyarsu sai gashi tare da Matanshi, Allah yasa ina daki suka dawo shi ya shigo ya zauna yana kallon yadda nake cin popcorn, wnada Yeemar ta kawo min, ina ji ina kallon tv. Sako naji ya shigo min wayata. *I want to see please now!* Karantawa yayi yana kallon yadda fuskata, tayi irin surprise din nan. Tashi nayi na wuce daki, dawowa nayi na kashe wutar parlourn, sannan na koma wani Changuan sexy Illusion bathroom lingerie na saka, sai da na saka black sexy pant a ciki ba bar sama babu bra, sai rigar a hankali na dauko wata heel shoe baki, mai igiya na rike a hannuna. Shegiya Yeemar zata mai dani yar iska. Ina rike da takalmin yana zaune a kujeran, hannuna dauke da waya na tura mishi. *Hi Boy* juyowa yayi tana kallon yadda nake tsaye a bakin kofar, wutar dakin yana hasko ni, gyara zama yayi tare da saka fuskarshi a saman hannunsa tare da hannunsa da ya saka a saman kujeran kamar yayi tagumi, takowa nayi gabanshi na saka takalmin tare da kallonshi na d'aga kafana na daura a kirjinshi. Ba musu ya shiga daure min takalmin. Na kuma mika mishi dayan ya daure min, sannan na mika mishi bam din hannuna shima baki, ya amsa na zauna akan cinyarsa, ya tattaro gashin ya daure min kafin ya kwantar da kanshi a bayana. "Gurl!"
"Hmm!"
I wanna na see naked please off it'!" Jim nayi kafin na mike tsaye na kwab'e kayan tare da zama a gabanshi. "That's my Gurl!" Ya fada yana shafa kaina zuwa fuskana. Janyo ni yayi a hankali, ya dauki hannunsa ya daura a kirjina. Kirjinshi yana shafa wani irin beating more and more! Bakin mu na hada wuri guda, ina mishi wani jahilin kiss, ni dai ban san yadda aka yi na hau dukiyarshi ba, amma na gaji da min wulakancin da yake min, rike ni yayi gam, yana kallon yadda nake mishi, kalaman Yeemar ya dawo min.
_Ko ki bashi hakkinsa ko kada ki bashi yana da masu bashi fresh fruit! Ba irin naki ba idan zaki ajiye iskanci ki kama Mijinki a hannu ki ajiye idan har yarinyar da Ubanta ya gama lalata yaran mutane a waje ta san yadda zata kama miji amma ke kike zaune zance kin yi asarar kudin tara, idan har yarinyar da bata kai ta kawo ki ta iya hakuri idan ya mata wulakanci bata yarda a ji kansu sai da ke take haukar wallahi kin yi asarar rayuwarki kin ga wallahi kin bani mamaki more than I expected daga gare ki! Jami'a fa kika yi ita rashin nutsuwa ko secondry bata gama ba amma ta iya haukata shi bayan yasan kome a kanta ke dai ko Allah ya kyauta amma da na zage ki wallahi!"_ sai nayi wani irin kunya ta kamani na adarar da nayi tare da kasa yin kome idan Nady tayi min na share ita Ijlal samuna tayi da shi fa. Mijina nane fa na bata aro kuma take min iskanci take min bita da kulle. Haka yasa na kasa hakuri na cigaba da mishi wani munafikin kiss wanda na hada da tun daga bakinshi har zuwa wuyarshi. A hankali nake ɓalle bottom dinsa. Na bude kirjin rigar bakina na kai kan nipples dinsa, na fara lasa ina tab'a dayan. Rike ni yayi tare da hura min iskar bakinshi. "Calm down Baby gurl! Gobe zan koma hannun Nadiyyah!" Ya fada yana shafa kirjina zuwa cikina, "ki adana min kanki zan dawo! Zan zo gare ki kada ki yarda wani ya b'ata miki rai....
08130269641
[7/26, 10:02 Safiya] Ramlat Manga41: 60
Idanuna a lumshe, kanshi ya kai wuyana ya rike fatar wuyana da hakorinsa, "Ashhhhh!" Na faɗa yayi murmushi. "Ina son kowa ya ga wuyarki ko ni na gani nayi ina craving dinki, a duk lokacin da na ga red mark naji am the who bite you!" Bakinshi na kama ina tsotsa anya ba Aljanu aka saka min ba, eh tow wani abu nake ji yana yawo a jikina, tare da wani Strong feel, rungume ni yayi yana shafa bayana. "Is okay!" Ya fada yana hura min kunnena. Daukata yayi muka wuce dakina, ya kwantar da ni tare da zama ya tofa min addu'a. Yana shafa hannuna yana murmushi. "Ina fatan wannan shine karshen matsalarmu!" Gyada kai nayi ina rike hannunshi. "Thank you!" Ya fada yana kallon yadda nake kallonshi. Haka ya zauna a gaban gadon har na fara barci, sannan ya mike tare da kashe wutar dakin, ya dawo Parlourn ya kashe wutar parlourn ma, sannan ya dawo dakin ya kalleta ya gyara mata kwanciya, yana fita ya hango Ijlal da gudu ta shige bangarenta, mamakin yadda take iya lebe yake. Bai kulata ba ya wuce dakinsa yayi wanka da alola sannan ya wuce ya ɗakinta, tana ganinshi tayi kamar tana barci. "Ijlal!" Tashi tayi zaune tana tura baki. "Me yasa kike haka?" "Amma ai ranar girkina ne!" "Ita da kika bani abinci ranar girkita tayi miki magana ne? Ko da kika kyale ni na zauna a dakinki baki ji yadda take ji ba ne?" "Ai haka ne yasa na ki magana don kada a ce na shiga hakkinta!" Tsaki yayi ya kwanta. Idan ya bi nata sai ya mata duka ya lura da ita ba wani abu ba ne don an mata duka, kasa barci yayi yana juyi domin baya sha'awar Ijlal ita kuwa kamar mayya haka tayi ta shige mishi, yana ture ya daga karshe dai ya bada kai bori ya hau, haka dai aka gama shi.
***
Underworld
"Nafi'u har yanzu jinin ya gagara ne? Jinin yarinyar nan take buƙata, kasan jinin Salmanu Faris ba zai tab'u domin abu uku ke tare da Yaron nan, Uwarsa na biyu addu'ar da take mishi ba dare ba rana, haka kuma akwai wani abu a cikin inuwarshi, tun yana Yaro na hango inuwarshi biyu ne, don haka idan kana son zaman lafiya ka kawo min yarinyar ko da kuwa na wata watan ta ne!" Ya fada yana kallon Rilwanu Yayari. "Ai na gaya maka zaka yi bakin jini me yasa kake tsammanin zasu so ka? Ba kai kaɗai bane mugu a cikin masarautar hatta yan uwan Attahiru mata sun tsane shi, balle kuma Matanshi kana tsammanin zasu so ka ne?" Murmushi yayi yana juyi ya ce mishi. "A cikin gidan da kake zaune an tashi wata tsinuwa tana nan tana niman inda zata zauna, ka kiyayye kanka domin hatsarin da take d shi yafi hatsarin da Mai Babbar daki take da shi, sannan ita tsinuwar tana lullube a bayan wata mace ce a cikin gidan sannan tana bibiyar Rayuwar Salmanu Faris, idan ka tab'a shi zaka iya rasa kome nata, kamar yadda Uwar tace bata son ya shiga harkan mulki tow kuwa kada ka sake haka ya haɗa ku!" Gyada kai yayi ya kalli Nafi'u. "Kada ka tab'a yarinyar akwai lokaci duk wani abinda kuke kullawa ina sane da ku kada ku sake ku yi tari! Domin kai Nafi'u baka da hankali zaka iya aikata kome, amma akwai iyakar da nake son ku kiyayye domin sake wani abu ya kara faruwa na an tab'a Salmanu ni da ku. Sannan Gwaska dakare ba zai tab'a fitowa ba, ku yi kome a tsannake domin yana fitowa zai tsaya ne akan aikinsa."
Juyi yayi yana masifar jin ciwon jikinsa, don ba karamin azaba yake yi ba shi kaɗai yasan irin zafin da yake ji. "Na sanka nasan halinka, sannan kai ka saka danka ya tura Yara gidan Salamanu Faris su dauko Matarsa, hmmm kana hauka ne na gaya maka ita yarinyar da nake so ba haka kawai zaka same ta ba,.amma kai lissafinka ta yara ce babu mata ne a gidanka?" Girgixa kai yayi yana faɗin. "Gaskiya ban san yadda xan ce maka ba, amma ni ban saka su kashe kowa ba, shi ya nuna musu tsageranci." Alama yayi musu da hannu su tafi kawai shi yasa yadda yake ji, haka suka fita suna masu son ganawa da juna, kowa hanyar shi daban. Bayan sun fita Alhaji Nafi'u ya kira shi. "Kana ina?" "Ina kofar gidana da yake Sultan road!" "Ok gani nan zuwa." Bayan kamar minti goma sai ga Alhaji Nafi'u suka shiga kasar wata rumfa suka zauna." Shiru ya ratsa tsakaninsu. Kafin Alhaji Nafi'u ya ce mishi. "Kace hakimai da dagatai ne suka gana da Maryamu?" "Eh!" "Tabbas sun kira ruwa!" Abinda ya faɗa kenan yana faɗin.."Ka bani sunansu zasu dan da ni suke ba da kai ba!" "Ka manta abin ya ce ne?" "Wanann matsalarmu ce bata shi ba!" Ya fada yana kallon wayarshi kiran Musharraf yayi ya gaya mishi abinda yake so sannan a cikin awa ashirin da hudu ya bashi oda a sauke goma cikin hakimaia dakatar da dagatai, haka da suka yi wai don su cusa tsoro a zukatan nan sarakunan nan ne, sunan goma ya kira aka tura mishi.
Ya bawa Alhaji Nafi'u, a cikin abinda bai wuce awa daya ba aka tabbatar a cikin waɗanda aka sauke har da Alhaji Mamman Yayari a muƙaminsa, sai Alhaji Kabiru Hamud Yayari, shima aka sauke shi. Sannan aka kago musu karya da wani zancen cin amana.
Washi gari
Wurin mai babbar daki aka kawo maganar, ta kira shi bai dauka ba, sai ta kira Faruq. Cikin yan mintuna sai gasu tare da shi, ya zauna yana kurban tea da ta haɗa musu. Suna sha a hankali cikin nutsuwa suna kallon juna ta ce mishi. "Ka ji labarin abinda ya faru!" "Ban gane ba?" Ya tambaye ta, murmushi tayi ta labarta mishi abinda ya faru. Sunkuyar da kai. "Me kike so yanzu?" Ya kuma tambayarta a karo na biyu, "so nake ka shiga lamarinsu, idan har ka kyale su gobe kai zasu tab'a, idan suka cire masu ƙarfin gefenka waye zai iya taya ka yaki? Ban ce kayi yaki domin niman wani abu ba, amma ka tsayawa mutanen da basu da karfin tsiyawa kansu! A lissafinsu zasu shigar da lamarin kotu ne amma na dakatar da haka na ce zaka shiga maganar." "Ummi me yasa kike shiga abinda bai dame ki ba ne? Ni ban ga wani amfanin shiga abinda babu ruwanki ba!" "Wadannan mutane da aka sauke da dakatar d asu, ba iya kai suke karewa ba, har da darajar Mahaifinka." Sunkuyar da kai yayi