Showing 84001 words to 87000 words out of 355604 words
so, to baki ɗauke ni a matsayin uwa ba kenan" shiru Rimsha ta yi bata sake yin magana ba.
Ita kuma Kausar ta miƙe ta nufi ɗakin nata tana turo baki tana faɗin "Ke ma Iya da son kalen dangi, yaushe kika taɓa ganin wani daban ya ɗauki wata a matsayin uwa, tab to idan ba ki sani ba ma, har zagin ki ake yi" "Ni dai kaya na ce ki ɗauko mini ba surutu ba".
Wucewa ta yi sai cika take tana batsewa, ita a dole an bata mata rai.
Kasan cewar tasan Rimsha bata son kananan kaya dan mugunta sai ta ɗauko mata, Rimsha kamar zata yi kuka ganin kayan da a ka ɗauko mata, ga shi kuma bata son yiwa Iya gardama ko dan saboda alkhari da ta musu. Jinin Nawazudden basa manta Alkhari komai kankantarsa, haka suke, haka iyayen su suka koya musu.
Iya da kan ta ta sanya mata wandon. Sai bayan ta sanya mata wandon ne tazo zata zuke zip ɗin rigar, a zafafe Rimsha ta damki wuyar rigar, kada Iya ta cire mata kaya a gaban su Kausar, ga shi ba wani vest ne ta sanya a ciki ba.
Abinma dariya ya bawa Ayla da Iya, sai murmushi suke yi.
"Rimsha dukkan mu fa mata ne kuma yan uwanki ne, me abin ɓoye ɓoye?". Cewar iya, girgiza kai Rimsha ta yi tana faɗin "A'a Iya mum ɗina ta faɗa mini idan yara suna kanana kana cire musu kayansu a gaban juna, hakan yana sanyawa yarana sha'awar lesbian, idan kuma mazane luɗu, haka zalika idan yan matan suna cire kaya a gaban juna shima yana sanya musu sha'awar lesbian, kuskure ne ka cire kayan ka a gaban koma waye, ko mahaifiyar ka, idan ba wata lalura ba kada ka cire kaya a gabanta, kuma ko a addinance ma yin hakan haramun ne, ganin tsiraicin ɗan uwan ka Allah ya haramta, ai ba'a banza Ubangiji ya haramta ba, saboda tsiraici yana sanya sha'awa in ma mace ko namiji, to yanzu an mai da abin kamar wasa, sai kaga yan mata da girmansu suna wanka tare su biyu a toilet ɗaya, sheɗan kuma yana daga gefe yana kallonsu, kuma hakan ya samo asaline daga laifin uwa, ita take cire musu kaya a idon juna tun suna yara, kuma idan zata yi musu wanka tana kai su cikin banɗa ki tare ta yiwa ɗaya wanka ɗayar na tsaye tana kallonta, bata damuwa saboda za ta yi tunanin ai dukkan su mata ne, ko kuma dukkansu maza ne, bata san babban kuskure take yi ba, a kwai wani hadisi da na karanta, in da annabi (SAW) yake tsawatar wa da nana Faɗima a kan yiwa Al Hassan da Al Hussaini wanka a tare, so cire tsiraici koma a gaban waye kuskure ne, dan yana sanya sha'awa ko ba ka yi niyar yin abu ba, shaiɗan zai buga maka ganga ka yi ba tare da ka sani ba, kuma Mum ta ce wani karin kuskuren ma da iyaye suke yi, sai su bar ƴara mata da maza suna kallon irin Indian Film ɗin nan, ana kiss ana runguma dukka a gaban su, kuma suna ganin mace da namiji keyin hakan, ai dole suma su ɗauki hanya".
Zuba mata ido kawai suka yi har ta kammala sannan Iya ta ce "Kina da gaskiya Rimsha, mu iyaye bamu damuwa ba, muna yin hakan, mu na ɗaukan kamar yara ne shiyasa muke haɗa su a toilet mu yi musu wanka, kuma idan misali a ce yara uku ne, sai ki ga mun yi wa biyu wanka mun baro su a ɗaki muna yiwa ɗayan wanka, kawai dan son jiki, muna bin sauki muna ɓata yaranmu da kanmu, wani lokaci kuma zaki gani idan kika gama yiwa ɗayar na karshen wanka kika fito zaki samu su biyun nan ɗaya na wasa da gaban ɗaya, idan maza kenan, a tunanin mu yara ne, so kawai ya ɗauki abin kamar abin wasa ne, shiyasa bamu wani mai da hankali a kan hakan, amma tabbas yanzu da kuka faɗa na gane yin hakan babban kuskure ne, shike ruguza al'umma, sai kaga ka dage ka bawa yar ka tarbiya, sai ka rasa ta ina ka samu tangarɗa idan ta lalace, ashe baka sani ba tun farko kake lalata farkon ginin, wani lokaci ma ƴaƴan namu mace ce da na miji ne, amma haka muke haɗe su muna musu wanka a tare, saboda shegen son jiki, ba zamu hakura mu fara yi wa daya, mu gama mu shirya shi tsab sai mu zo nu yiwa ɗayar ba, wani sain kuma sai ki ga uwa tana cire kayanta a gaban yaro, a tunaninta yaro ne bai san komai ba, duk wayan nan kuskure ne, ko kasa ɗan ka matashi ya yi wa kanwarsa mace wanka, Allah dai yasa mu ji mu gyara, amma Rimsha kin bani mamaki waye ya koya miki wannan dukka abin"
Yar murmushi ta yi har sai da dimple nata ya lotsa, "Mum ɗina ne ta koya mini, kuma ai na karanta su Fiqhu da sauransu, na san abubuwa da dama, kuma mum tana karamin haske har shima dad, sannan ni ina da yawan tambaya idan na ga abu, kalmar lesbian ma ni a wani kittafi na karanta shine naji kalmar ta mini wani irin, sai na je na tambayi mum, shine tamin bayani dalla dalla, har na gane nima nake yi wa mutane"
Leƙo fuskar ta Iya ta yi tana faɗin "Eyee da mum tana gaya miki ya kika ji sarkin kunya" rufe ido tayi da hannunta tana dariya kasa kasa.
"Kai gaskiya ba zan yarda ba, Rimsha dole mu yi sauri mu miki aure dan ke ai kin gama sanin komai". Cewar Iya, cikin sauri Rimsha ta ce "Kai Aure kuma Iya?"
Gyaɗa mata kai iya ta yi tana faɗin "Sosai aure kuwa, ai kin gama sanin komai ne, dole mu kai ki daga ciki" wucewa Rimsha ta yi ta shiga cikin ɗakin Kausar hannun ta riƙe da rigar tata.
Bata son tsayawa magana da Iya, dan kada Iya ta bawa zancen auren karfi, dan ita bata da wani buri da ya wuce ta je ta ga mum ɗin ta da Jehan ɗin ta, kuma ita bata son aure.
(Tofa Rimshan mu ma bata son aure, a'a lallai banga laifin Jehan ba)
Tana shiga ɗaki ta sanya rigar sannan ta yi zaman ta saman gadon Kausar tana tunanin GAR, ba abin da yake mata yawo a ƙwaƙwalwar ta fa ce yadda ya matso zai yi kissing nata, a hankali ta kai hannunta saman lallausan laɓaɓɓan ta, mai kama da fure, ta shafo lips ɗin nata tana murmushi ita kaɗai, daga bisani kuma sai ta maida hannun tata saman kirjinta tana shafa sunan Lion, lokaci guda wani tunani ya faɗo mata, idan ta koma gida Mum taga wannan zane fa, ya zata yi, ta sani ko Jehan ce ta ga wannan zane ba zata taɓa barinta ta zauna lafita ba bare kuma mum.
Miƙewa tsaye ta yi a zabure, tana tunani tare da danasanin me ya kaita ta zana sunan wanda ba Musulmi ba a girjinta, bayan ba musulmi bama bai san da zaman ta a duniya ba, sunan Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya kamata ta rubuta ko sunan dad da mum ɗin ta, wai shin me ya shiga kanta ne, har ta aikata hakan. Sai tunani take yi, tunanin da ba shi da amfani, domin suna dai ya riga da ya zanu ba gogewa, ba ta tashi sanin kuskure ta aikata ba, sai yau da ta tuna da littattafan musulunci.
(Lalai Rimsha kin shahara, to ni dai na kwashe kaya na, na wuce gidan Abba)
💖💖GIDAN ABBA💖💖
Yau tun safe su Akil suka wuce kano shi da Imran da Irfan, kamar yadda suka yi sammakon safe zuwa garin Kano, haka ita ma Hajiya Umaiya ta dakawa Umaisha sammako da uban kayan wanki. Umaisha ta sha mamaki, ta ce ga engine wanki za ta yi amfani da shi, amma Ammie ta hana ta, ta ce ai tasan da washing machine ɗin, ta ce ta mata wanki da hannunta, har ga Allah Umaisha bata iya wanki ba, bata taɓa yin wanki ba, ko kananan kayan ta irin su pant breziya ba ita take wanke wa ba, mai aiki ke wanke mata, haka suka taso, ba abin da suka iya, kayan sawan su akwai mai wanke musu namiji ne.
Tun karfe shida na safe take wankin uban kayan Ammie, tana yi tana kuka har karfe 1 na rana, abin haushin ma shine jijjiƙa kayan kawai ta yi, ta kara musu datti, ba abin da ya fita, hakan kuma ba ƙaramin haushi ya bawa Ammie ba, cikin zafin nama ta hauta da faɗa da masifa, ta ko'ina ɗura mata zagi ta ke yi ba sassauci, sai da tayi zagin mai isarta, sannan ta sa ta a kan ta sake faro wankin daga farko, sai ta wanke kayan sun fita fes idan tana son zaman lafiya, ga shi bala'i yinwa take ji, kuma Akila ta kai mata takeaway ɗaya ɗakinsu kafin ta wuce school, amma Ammie ta ki barinta ta je ta ci abinci, ga kukan yinwa ga na wahala, ta yi har ta ga ji.
A wannan hali su Aafia suka tarar da ita, Aafia tare da Rufee da Anisa ne suka zo, Irfan ne ya sa driver ya kawo su, tun kafin su wuce kano, dan Akil ya gaya masa yana son Aafia ta je ta taya Umaisha kwana tun da kwana za su yi a Kano, kuma daman Umaisha ta matsa masa a kan ya ɗauko mata Aafia. Sai dai da driver ya ɗauko ta ne, sai ta ce ya biya su je su ɗauki Rufee da Anisa, idan yamma ya yi sai ya mayar da Rufee da Anisa gida, Irfan ya hana Aafia tuki yanzu duk in da zata je kai ta a ke yi a ɗauko ta.
Ganin Umaisha na wanki a tsakar gida, da ruwan famfo duk ta rame, hakan yasa Aafia banko wani uban ashar wadda baki ba zai iya faɗin shi ba.
"Kutumar uban can, ke Umaisha wani dakikin bagidajen ya saki wannan ɗan iskan aikin?!!"
Kasa magana Umaisha ta yi, ta kuma kasa miƙewa ta je wajen su, sai kara sautin kukan ta da ta yi. Aafia da Anisa har suna rige-rigen karisowa wajen ta, ita kuma Rufee sai bin gidan take da kallo, taga tamɓatsetsen gidan da ya ci uban nasu Aafia a komai da komai, ta saki baki galala kawai tana kallo.
(Kai Rufee akwai son duniya)
A tare Aafia da Anisa suka ɗago Umaisha, duk ta rame ta ba kyan gani. "Ba kuka zaki yi ba Umaisha, ki faɗa mana waye yake baki wahala haka?" Cewar Anisa.
Cikin kuka da kyar ta iya buɗe baki ta ce "Ammie yaya Akil ne, ita ce wlh kullun take azabtar da ni, Aunty Afi dan Allah ki mai dani gida, idan ba haka ba, zan iya mutuwa a nan".
Wani sabon ashar ɗin Aafia ta sake wulwulowa, tare da jawo hannun Umaisha suka nufi cikin gida, tana faɗin "Ke mara mutuncin mata ina kike?".
Ummi na zaune saman sofa, palonta sai kamshi yake zubawa Umaisha ta gyare ko ina tsab, ta ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya tana kallon Tv ta bar baiwar ta Umaisha a waje tana tikar aiki.
Jin hayaniyar su Aafia ya sa ta juyo tana kallon kofar shigowa, ganin su yasa ta ja tsaki tare da mai da kallonta kan Tv.
Gabanta Aafia tazo ta tsaya rike da hannun Umaisha tana faɗin "Ke dai wlh anyi azzaluma muguwa, annamimiya, yanzu uban me Umaisha ta miki ki ke azabtar da ita haka?" Anisa ce ta karɓi zancen da cewa "Baiwa ce ita da zaki saka ta wancan uwar aikin? To wlh muna baki last warning idan kika sake saka ta aiki sai kin yabawa aya zakin ta, ai ba baiwa aka kawo miki ba".
Miƙewa Ammie ta yi tare da riƙo wuyar rigar Aafia ta dalla mara maruka masu kyau guda biyu, sannan ta ce "Ke wlh da alama sai na koya miki tarbiya, to shi bappan naku ma me a ido na bare uban ku bare kuma ku? To wlh tun wuri ku fita mini a gida tun ban muku dukan mutuwa ba, banza ye marasa tarbiyya".
Sanin su Akil basa nan ya sanya Aafia ta yi kokarin ja da Ammie, sake riƙota Ammie ta yi zata dake ta, daidai lokacin Rufee ta shigo, cikin sauri ta tarewa Aafia tare da riƙo wuyar rigar Ammie tana faɗin "Ke tsohuwar kilaki, ashawo, ki kama kanki wlh, idan ba haka ba zamu nuna miki mun fiki zama tantiran ƴan bariki, yanzu sai mu miki dukan kawo wuƙa a cikin gidan nan, muga uban da zai karɓe ki, muguwa azzaluma, kin tasa karamar yarinya a gaba sai zaluntar ta kike yi, idan kin kai shegiya, ai manyan yan duniya zaki samu irin mu sai mu buga game ɗin, ba karamar yarinya kamar Umaisha ba, wadda kin kusa jika da ita, dan da ga gani ke old woman ce sosai".
Idan kaga Rufee yadda take tarewa Aafia faɗa sai ka yi zaton da gaske tsakani da Allah take yi, amma azahirin gaskiya ba haka bane, kawai dan taga Ammie ta mata kama da matar gidan ne hakan yasa ta zage take cin mutuncin Ammie sosai, dan a cewarta gidan ya mata, ta samu wajen zama.
(Tof fa, lallai Rufee ai in dai gidan Abba ne, Bismillah zoki zauna, duk wanda ya ci tuwo da gidan Abba wlh miya ya sha, bake yar son duniya ba Bismillah to)
Dun wani baki na Ammie yau sai da Rufee ta kashe mata shi, tatas ta mata, har sai da Aafia ta tsorata ta fara ce mata ta yi shiru, tana tsoron kada Ammie ta gaya wa su yayan Akil su ci ubanta. Amma ina Rufee ta ki yin shiru, tsab ta wanke Ammie, wankin babban bargo.
Idan kaga yadda yau Ammie ta yi shiru ta nitsu sai ta baka tausayi, gaba da gaban ta, yau ta haɗu da jiga-jigan yan bariki, wayanda suka fita gogewa a fannin iskanci da iya shege, wato Rufee da Anisa, dan Anisa ma ba baya ba wajen baki da iya faɗa, sai dai ita tsakani da Allah take tare da su Aafia, ba da wata manufa ba, kuma ita bata bin maza, cikakkiyar budurwa ce, amma ta iya faɗa.
Sai da suka tabbatar sun rufe bakin Ammie sannan suka wuce part ɗin Akil, Umaisha ta musu jagora.
Kwafa Ammie ta yi, a ranta tana faɗin "Kun jawo wa yar uwarku bala'in da sai ta gwammaci mutuwa"
Toh fa, su Aafia suna tunanin sun kashe wuta, basu san kara hura wutar suka yi ba.
(To mu dai koma Washington DC kafin mu dawo wata kila abubuwa sun ɗan gwaru a nan)
💖💖Washington DC💖💖
After some day's👌
A yanzu Tyrone ya samu sauki kuma ya dawo bakin aiki gadan-gadan.
Zaune suke a palon kasa, Michael ya tada kai da cinyar Uncle ɗin James wato Musharraf, yanzu Michael ya samu sauki sosai, sai dai ba gaba ɗaya ba, amma an samu cigaba sosai da sosai, yanzu yana iya tantance daidai da ba daidai ba, kuma ya fara koyan karatu da wasu abubuwan, sai dai shagwaɓar nan tasa tana nan.
Yanzu ma sai zubawa Uncle ɗin James shagwaɓa ya ke yi, Musharraf na biye masa, a yan kwanakin da suka yi, sun saba sosai, sun shakuda Michael fiye da yadda suka shaku da James, duk da cewa lokacin da James yake nan Musharraf baya iya tafiya, hakan yasa basa wasu wasannin tare, yanzu kuma yana iya tafiya, James baya nan, sai Michael ya maye masa gurbin James ɗin, idan kana son ku yi faɗa da Michael to ka taɓa masa uncle ɗin James ɗin sa, nan fa zai gwada maka shi Triplets ɗin The General of The Army ne, tuni zai ɗauko gun ya saita maka hanya, dan ma dai Lion ya tattare pistol dake cikin ɗakinsa dukka ya canza musu wajen zama saboda Michael, amma gaba ɗaya sojoji da bodyguards dake gidan, har wani girmama Musharraf suke yi, har sara masa suke yi idan zai wuce, kuma duk saboda Michael ɗan lalele.
Lion Tga Tyrone, tsaye suke gaban wani makeken desktop computer dake cikin ɗakin binciken su.
Tga da Tyrone sanye suke da Army trousers da kuma Army t-shirt, while shi kuma oga Lion yana sanye da irin wandunan nan masu aljihu dayawa a jikinsu, har ta gefen gwiwar su akwai aljihu, da kuma kyawawan ijiyoyi masu kama da igiyar boot, daga ta sama kuma yana sanye da farar t-shirt mara nauyi yar shara-shara, ya saki kyakkyawar gashin kansa, bai ɗaure ba, wannan guntu gashin na gaban goshin nasa yana nan, yar ramar da ya yi tasa idanuwansa sun kara girma.
Tsaye suke sun zubawa computer ido, Lion nata faman hargitsa dark black curly hair sa, alamar zuciyar sa na masa zafi, sai cizan red lips nasa yake yi.
Sun jima tsaye suna kallon yadda computer ke tariyo musu bayanan da suke bincike a kai.
Tga ne ya ce "Amma Lion wai wannan binciken na waye ne haka?" Shiru Lion ya yi na tsawo mintoci.
Har su Tga sun cire rai da zai yi magana, sai kuma suka ji sexy voice nasa yana faɗin "James ya yi kuskure, ya jefa kansa a in da mawuyacin abune ya fita, ko kuma ya rayu".
A sukwane Tga da Tyrone suka zaro ido suna kallon Lion, a tare kuma suka mai da kallon su kan desktop computer ɗin, dan su kara ganin abin da suke gani shin da gaske ne ko dai gizo idon su ke musu.
Sun jima sosai dukkansu a tsaye, sun yi mutuwar tsaye, dan sun kasa yarda da abin, sai wani gwalo idanuwan su suke kara yi ko zasu samu damar ganin akasin result da suke gani a system ɗin, amma ina wannan result da suka gani da farko shine dai a wajen.
Ganin haka yasa Tga ya ce "Amma Lion ba last month kasa su Tyrone sun tarwatsa kungiyar *I .D .A. E .S. A* ɗin nan ba?".
Dogon numfashi ya ja tare da sauƙewa a hankali, sannan ya fara magana a nutse.
"James ya sa na yi bincike a kan su, saboda na samu wasu abubuwa na tambarin kungiyar nasu a ɗakin sa, *I .D .A. E. S .A*