Showing 345001 words to 348000 words out of 438336 words
komai. Kamar yanda na faɗa muku sunana Murjanatu Usman. Teachen practice ne ya kaini asibitin kasancewar a bayyane duniya ta shaidashi da taimako wa talaka. Koda yake dama hakan shine burina. Dan a dalilin aikin ido da aka taɓama mahaifina ƙyauta a asibitin naji ƙarfin gwiwar yin karatu a fannin lafiya. Tare da alƙawarin neman aiki anan idan na gama domin hidima ga ƴan uwana talakawa nima. Hakan kuwa akayi, ana bamu zaɓin inda zamuyi practical ɗin na cike sunan asibitin. Na kumayi sa'ar aka turani can. A farkon farawa ban fuskanci kowace irin matsala ba, sai da na kusa cika watannin da suka kai gab da ƙarasa abinda ya kawoni, wani al'amarin daya gigitani ya faru. Mu huɗu ne baƙin masu koyon sanin makamar aiki, Dr Lawisa tai zaman meeting damu a satin kusan ƙarshe da zamu gama. Ta mana alƙawura masu yawa tare da ɗaukar mu aiki na dindindin da wasu abubuwa na ƙyautata rayuwa idan mun kammala karatun mu. Ƙarshen zancen shine tana son yin aiki tare da mu saboda ƙwazonmu. Harga ALLAH da farko bamu fahimci manufar aikin nata ba. Dan haka muka miƙa wuya. Rashin wayo kuma da jin ɓoyayyen aikin taimako ne da bata son kowa ya sani yasa data bamu takardar yarjejeniya akan da mun kammala karatu nan zmauyi bamuyi wani musu ba muka saka hannu itama ta saka tare da wasu mutane biyu da bamu san matsayinsu a wajenta ba. Tun daga nan muka fara aiki tare da ita. Sai dai a zahiri muna ma asibiti aiki ne kuma. Bayan kammala karatun mu muka dawo aiki gaba ɗaya, a kuma lokacinne aikin data buƙaci muyi taren muka fara shi. Tsagwaron tashin hankali muka shiga mu duka a ranar farko da muka fahimci minene aikin data kira na taimakon. Dan ba komai bane face cire ƙodar bayin ALLAH da basuji ba basu gani ba. Musamman ma talakawa da ke cikin matsanancin yanayin ciwon da ke buƙatar taimako. Sai ta katantance tace zata taimake su ta ɗakko wata cuta mai alaƙa da cikin ciki tace kana da shi sai an maka aiki. Idan aka saka kuɗin aikin ta yanke kaso biyu tace ka biya ɗaya asibiti zata biya sauran, sai ai amfani da wannan damar a cire maka ƙoda batare da ka sani ba. Nuna borenmu akan wannan al'amari yasa taima Safina allurar poison ta mutu. Ta kuma ɓatar da Pemi har yanzu babu wanda yasan inda yake. Kowa ɗauka yake ya mutu a gobarar data cinye gidansu. Ni da Sajida mun matuƙar razana, ta yanda har muka gagara iya nuna sake borenmu. A tsahon shekaru biyu kenan dana kasance a asibitin wlhy Ni kaina bazan iya faɗar adadin da matar nan ta cirema ƙoda ba. Tun daga kan yara ƙanana, manya, mata da ma tsoffi. Aikin kanso ya tashi wani lokacin asiri yay kamar zai tonu, sai dai tasan duk hanyar da zata bi ta daƙile komai ta cigaba da bizne mummunan aikinta. Badan muna so ba muke mata biyayya, dan wlhy yanzu haka Babana itace ta maida shi haka, hakama Yayan Safina ta maida shi gurgu. Dukkan motsin rayuwarmu tana biye da shi. Kusan mu goma ne ma'aikatan asibitin dake ƙarƙashin wannan mulki nata wanda dai na sani a bayyane, sai dai gaskiya sauran duk da amincewarsu sukeyi. Ni da Sajida ne kawai bama so. Rashin ƙarfi da hanya da tsoro ya hanamu fiddo zancen. Ba wannan bane kawai, hatta da mutun idan ya mutu akan yi saurin cire wasu sassan jikinsa sai dai wlhy ban san mi take yi da su ba. Hatta da ƙodar ban san wanda ake bamawa ba idan an cire. Sai dai akwai wata mata dake yawan zuwa wajenta Madam Jannifer, tana kawo yara itama ana cirar ƙodar tasu, a ɗan bincikena na gano itama tana safarar yarane daga arewaci da sunan aikatau. Sai dai idan ta kawosu sai ta saka wasu a karuwanci, wasu kuma ta rabama manyan mata ƴan lesbians. Wasu kuma a fita da su ƙasashen ƙetare. Ita ɗin matar wani babban soja ne daya rasu shekaru kusan goma sha bakwai. Tana da yara biyu amma duk basa Nigeria. Bayan mutuwar mijin nata ne tayi ridda daga musulimci ta koma kirista. Asalin sunanta Munnira ne, daga ita har mijin ƴan jihar Zamfara ne. A yanzu haka ma naga tana hannun hukuma an kamata da zargin kidnapping mijin ita Dr Lawisa. Sai dai abinda na fahimta tabbas da sanin Lawisa komai ya faru, dan shekaranjiya naji tana waya da ita sai dai ba komai na fahimta ba a zancensu. Sannan ana shigo da mugayen ƙwayoyi ana ajiyarsu cikin store ɗin asibitin nan da sunan kayan asibiti ne, ana kuma saida abubuwan asibitin masu muhimmanci suma. Wannan shine abinda na sani kawai Wlhy”..........✍️
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒔𝒆𝒗𝒆𝒏𝒕𝒚-𝒏𝒊𝒏𝒆_
.......Mu dukanmu salati kawai mukeyi da mamakin hatsabibanci irin na wannan mata. Sai kace ba mace da aka sani da taushin zuciya da tausayi ba. Lallai al'amarin na matar nan babbane. Tsahon lokaci babu wanda ya iya cewa komai hatta shi mai gayya da aikin. Sai da Jaga ya ce, “Humm ai dama na faɗa maka babban yaya. Akwai abinda take yi a asibitin nan shiyyasa ta bashi muhimmanci sosai. Dan matar nan ANGULU ce wlhy bata jewar banza. Shi kansa Commondo ɗin amfani kawai take yi da shi. Ai ko yanda kuɗaɗe ke shigar mata duk da tana ɓoyewa tuni ya kamata a zarge ta da hakan”
Cikin jinjina kai Hayatu ya ce, “Tabbas maganarka haka take Jaga. Dan ko shi kansa Baba yanzu na fara tunanin anya matar nan ba itace ke amfani da shi ba”.
“Zata yiyu bazata yiwu ba oga Hayatu. Saboda magana ta gaskiya shima tsohon nan hatsabibin kansa ne. Ko maganar saka yara a containers ɗin babban yaya na kwanaki wlhy ina da tabbacin yana da hannu a ciki. Dan ni na faɗa muku wannan Mr Paul fa abokin huɗarsa ne sosai. Sune ma suketa son jansa ya shiga siyasa yana ƙi, bakuga yanda aketa jan shari'ar ba ma. Yanzu dai gasu can na barsu a halin ruɗani da ƙaulanin kasa banbance ni fatalwar ne ko kuwa ina raye. Duk da dai nasan zuciyarsu tafi karkata ne a ni fatalwa ne. Amma a taron sunan nan na gobe zan tabbatar musu ni mutum ne. Ruɗanin da zasu shiga shi zai sa su fara neman hanyar tabbatar da gaskiya, babban Yaya kuma sai yay amfani da wannan damar. Ni wlhy so nake ma Babban yaya yasa a saki Commondo nifa nafi son na kashesa da hannun....”
Ya kasa ƙarasawa saboda kallon da Maash ya masa. Murmushi na ɗan yi da girgiza kai. Hakama Hayatu sai da ya murmusa kaɗan. Sai TJ ne ya furta, “In sha ALLAHU bazaka sake aikata wani mummunan aiki ba Muntari. Na baya ma ALLAH ya yafe maka tunda Alhamdullah bama ka taɓa yin kisan ba dai”.
“Hakane kuma Yaya Tijjani”.
Jaga ɗin ya faɗa fuska a marairaice kamar zai yi kuka.. Ni sai ma abin nasa ya bani dariya......
💦⭐💦⭐💦
Gaba ɗaya lissafin Baba prof ya gama rincaɓewa. Dan tunda Isma'il daya kawosa ya rakashi har Bathroom ya fita sai ma ya gagara yin wankan. Ga warin gudawar da yay a jikinsa na matuƙar damunsa. Amma ruɗanin ganin Jaga ya mantar da shi komai. Tabbas da farko zuciyarsa ta bashi Jaga fatalwa yay musu. Sai dai yanzu daya haɗa lissafi ya fahimci maganar Hajiya ƙarama gaskiyace kenan. Commondo na son cimma wata manufa shiyyasa bai kashe Jaga ba. Shiyyasa a yanzu ma da yake a hannun hukuma bai damuba, saboda yanada wanda zai masa aiki a waje. To amma Jaga sunan Awwab ya ambata ai. Ya ilahil alami. Shin ko dai Commondo shima ya koma ɓangaren Awwab ɗin ne? Tabbas idan hakanne zama fa bai gansa ba. Dole ne a gobe ayita ta ƙare kawai. Zaiyi amfani da taron da Nafisa ta sanar masa za'ayi a Mansion. Ƙasaitacen murmushi ya saki a hankali tare da sauke nannauyan ajiyar zuciya. Sai yanzu ne yaji ƴar nutsuwa na dawo masa. A gurguje yay wankan duk da jikinsa babu wani ƙarfi. Yau babu zancen shan barasa. Ɗakin sirrinsa ya shiga ya dinga haɗa duk wasu abubuwansa masu muhimmanci waje guda. Haka ya raba dare, sai da ya gama tsaff sannan ya bincika jirgin da zai iya tashi koma na wane ƙasa ne a gobe idan ALLAH ya kaimu ƙarfe huɗu. Yako samu mai zuwa Saudiyya, a take ya sayi ticket ta online ɗin. Bindigarsa daya jima bai yi amfani da ita ba ya ɗauka yayma zubin bullet taf sannan yay zaman yin dogon rubutu a takarda daban-daban kowanne da sunan ƴaƴansa. Suma ya kammala gab da asuba ya haɗasu ya ajiye. Sai lokacin ya samu giyarsa ya kwankaɗa son ransa sannan ya haye gado yay male-male.....
🌿✨🌿✨🌿
A lokacin da Baba prof ke wancan shiri anan Maash Mansion ma Hajiya ƙarama tunda ta samu ta sheƙama kanta ruwa akan batun Jaga sai ta fara samun ƴar nutsuwa. Ita dai tunaninta na nan akan Jaga fatalwa yay musu. Dan haka ta tabbatar ma kanta yin abinda ya dace kafin komai ya buɗe. Dan ta fahimci a yanzu Madam Jannifer da Commondo komai zai iya fita daga bakinsu. Hakama Baba prof a shirye yake da yin komai a kansu. Idan ko haka ne to batun ta kwanta a barci baima taso ba. Ita dama ta kammala dukkan shirinta game da kaf dukiyarta da harƙallolinta ta shirya ta yanda kota bar ƙasar zata cigaba da gudanar da komai a maɓoyarta. Hatta da sace Samraah ta gama da wannan matsalar, dan bazata taɓa barma Awwab ba, babu ruwanta da batun wani ƴar Abdul-wahab jirgin mota ce har yanzu tana sonta da kwaɗayin kasancewa da ita, ko cikin jikinta bai dameta ba zata zubar da shi da zarar sun bar ƙasar. Arwa kuwa da abarta zata tafi. Itama dai ticket ta siya ta online amma na ƙasar Dubai, daga can zata wuce ƙasar data gama tsarama kanta rayuwa da wani bazai taɓa tunanin tana a can ba saboda ƙasar ba wani wajen yawan zuwan mutane bane. Gaba ɗaya yaranta da ta gama shiryawa domin wannan yaƙi ta kira. Sai Marcel da shine uban tafiya. Abinda kawia ya banbanta shirinta da Baba prof ita sai nan da kwana biyu take shirin wucewa. Amma dai a gobe take son ai mata kidnapping duk wani wanda ke cikin list ɗinta. Saƙonta daga wajen Dr Khunal kuwa a daren yau zai iso Nigeria kamar yanda ya tabbatar mata. Dan tun ɗazu da sukai waya yace mata bazai ƙara minti goma da shi ba a hannu amma ya sake ninka mata kuɗin kuma a haka ta biya. Jirgin da ya taho da saƙon kuma da ayanzu haka yana a bisa hanya na tashi yay mata text da _Done_. Wannan ne ma ya bata ƙwarin gwiwar tunkarar Baba prof a ɗazun....
🤍💫🤍💫🤍
A nan ɓangaren Fahad da Hafizzullah kuwa su shirin shagalin sunan gobe in sha ALLAHU sukeyi hankalinsu kwance. Dan su kawai a rakwashe a ƙwalle a girgije shine nasu shirin. Ga mutanen Kano su Abba da wasu a cikin ƴan gwarzo na a hanyar zuwa a goben domin ganin Falaq da kuma halartar bikin suna duk da taso ace itace ta fara ziyartarsu amma sun dai ce sune zasu zo domin neman afuwar mama Balki. Dan hakama suka kwaɓeta gaya mata, hatta da Samraah ma bata san da zuwan nasu ba. Amma Maash da Hayatu duk sun sani, a jirgi ma zasu zo.
Abin da farko kamar wasa sai gashi dai gagarumin taron suna na niyyar haɗuwa. Dan daga abincin mutane ɗari da sukai niyyar yi sai Ummie tace a ninkashi ya zama na mutane dubu ɗaya za'a bada wani sadaka. Duk da ma bata san da zuwan baƙi daga Kano ba kasancewar har yanzu bata san alaƙar Hafizzullah da Samraah ba. Ba kuma tasan Samraah ɗiyar Jirgin Mota bace. Su Hayatu sun tsara sai a gobe zata sani in sha ALLAHU wajen taro. Koda Hajiya Mammah ta zagi Samraah da sunan ɗiyar driver a jiya kawai ta ɗauka hakanne amma hawai ta ɗauki abun da muhimmanci ba. Dan ko ɗiyar mai bara Awwab da Fahad suka kawo mata matsayin matansu zata goya musu baya kuma taso matan musamman idan sun kasance mutanen kirki masu tarbiyya.
Bayanin likitanta akan ba komai zai dawo mata kanta lokaci ɗaya ba kamar da, ba kuma komai zata zurfafa nazari ko maida hankali akansa ba yasa yanda take ɗaukar Hafizzullah ɗan Mama Balki yasa suka barta a hakan kawai. Dama kuma bata tambayi kowa ba akan hakan ma.....
💙💢💙💢💙
Zazzaɓin dana fara ji yasa muka baro guesthouse ɗin nasa muka nufi gida. Muna shigowa gidan muka tadda wani bala'in kuma. Dan tun a compound muka samu ma'aikatan gidan cirko-cirko maza. Daga ciki kuma ihu da kurkurwa ke tashi kamar muryar Hajiya Mammah. Har Maash yaja hannuna alamar muje ciki na girgiza masa kai. Murya a marairaice nace muje muga muke faruwa. Yaso tirjewa na sake shagwaɓe masa kamar zanyi kuka. Mun girgiza matuƙa da abinda muka samu yana faruwa. Wai baƙuwa Hajiya Mammah tayi tun safe sai kuma ga ƙawarta Hajiya Rubayya da daren nan. Babu wanda yasan miya haɗasu aka jiyo hayaniyarsu. Tun sunayi a ɗaki har takai an fito waje tare da hankaɗo baƙuwar Hajiya Mammah waje tsirara. Ita ma Hajiya Mammah ɗin daga ita sai zanin gado data cikuykuye jikinta a ciki. Yayinda Hajiya Rubayya ke riƙe da wuƙa tana rantsuwar sai ta kashe Hajiya Mammah tunda taci amanarta.
Cikin tashin hankali Maman Malika ke tambayar cin amana kamar ya. Babu ko ɓatan harshe Hajiya Rubayya ta saki baki tana kwarara bayanin aure sukai ita da Hajiya Mammah shekara biyar kenan. Amma sai gashi yau ta kamata da ƴar ƙanwarta da take riko a gado ɗaya. Babu wanda bai razana da wannan batu ba. Falon yay tsitt zuciyar kowa na bugawa da ƙarfi. Baka jin komai sai hayaniya da banbamin Hajiya Rubayya dana Hajiya Mammah da ke faɗin itama wlhy sai ta kashe Rubayya. Kafin kace mi sun farama juna fallasa.........✍️
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒆𝒊𝒈𝒉𝒕𝒚_
.......Hajiya Rubayya ta shiga faɗin, “Amma dai kin san ke ƙaramar ƴar iska ce Nafisa. Sannan a tafin hannuna kike wlhy. Ko kin ɗauka nima zaki iya yimin irin asirin da kikayi ma Mu'azz da babanku na mallaka domin gidan nan da komai ya dawo hannunki ki dinga juya kowa na cikinsa. Kullum cikin bankawa Maash asiri kike dan ya auri ƴarki ku mallake dukiyarsa sai wanda kika so yaci. Da kikaga kinƙi samun damarsa akan auren kin buga kin buga ya gagaresa sai kikaje kikayo masa asirin da yayma ƴar mutane fyaɗe. Kika kuma shirya tozarta shi wa duniya sai da kikaga kin gagara samun hanya kika dakata. Dai-dai da ubanki asiri kike masa ko na miki ƙarya?”.
Wani shegen zabura Hajiya Mammah tayi kan Hajiya Rubayya cikin kukan kura da wuƙa tsirara. Fashewa duk mukayi dan tsabar tsorata. Dan kowa ya gama sadaƙarwa za'ai kisan kai. Abunka da taron mata.
Wani ihun da Hajiya Mammah ta sake saki da faɗin, “Ka sakeni Awwab ka sakan. Wlhy sai na kashe wannan matar yau”. Yasa duk muka fahimci shine ya riƙeta. Duk abinda taken kuwa bai sake ta ba. Yana tsaye cak itako tanata fisge-fisgen son ƙwace hannunta. Sam ba ita yake kallo ba. Sai da mukabi abinda ya kafe da ido muka fahimci Paah ne tsaye a wajen ashe. Tsabar mamakinsa da firgici sai kawai mukaji Hajiya Mammah ta ƙwalla gigitacciyar ƙara, koda muka dawo da kallonmu kansu hannunta daya riƙe mukaga ta riƙe da ɗayan hannunta tana ihu ga hannun na jale-jale alamar ƙaryata yayi. Ko kallon inda wani yake kuma baiyi ba ya keta ta tsakkiyarmu ya gitta Paah ya wuce a binsa. Sai da yaje fita a kausashe ya furta, “Hayat! Securitys su kwashe min matar nan da dukkan muƙarrabanta” yay ficewarsa.
Razana matuƙa muka gani a fuskar Hajiya Rubayya. Ta zabura cikin masifa tana faɗin bataga ubanda zai kamata ba kawai securitys ɗin gidan suka shigo. Abinda ya ɗaure kan kowa da bada mamaki babu wanda ya musu bayani suka nuna Kubrah, Falilah, Afrah sai yarinyar da ake