Showing 102001 words to 105000 words out of 438336 words
Abinda Janny ta faɗa kenan tana mai riƙo hannuna. Ban amsa mata ba, sai ma ƙoƙarin turjewa da nayi alamar bazanje ba. Hajiya dake kallonmu ta sake sakin murmushi. “Kinga ɗiyata nasan mike a ranki, karki damu shi komai na rayuwa mataki-mataki ne tamkar ajin makaranta. Ki kwantar da hankalinki zamuje gaɓar da kike buƙata. Bani nai miki alƙawari ba”.
“Amma Hajiya.....”
“Shiiii!! Kar kice komai bita kawai”. Hajiya ta faɗa cikin katseni tana tsuke fuska a karo na farko. Canjawar fuskar Hajiyar ya ɗan firgitani, dan haka nabi Janny kamar yanda aka bata umarni tun farko....
Cikin dauriya da danne duk abinda ke mun kai-kawo a cikin rai nayi wanka na fito fes dani cikin doguwar riga mara nauyi ƴar kanti da Hajiya ta bani na saka. Ga wani ƙamshi mai daɗi na tashi a jikina. Hatta da dunƙulallen gashina da zaman asibiti yasa baya samun gyara sai da na wanke na busar da hair dryer dana gani a toilet ɗin. Yanda na fito da shi ne a buɗe yasa Janny sakin baki tana kallona. Fuska na ɗan tsuke amma sai hakan bai sata yin shiru ba sai da tayi magana. Da ga ƙarshe ta laƙemin wai zata tayani gyarawa. Mai sosai Janny ta saka min masu daɗin ƙamshi da ma wasu abubuwan da suka sake miƙar da tsahon gashin nawa daya fara dankwafewa tsaff, sannan ta fake min shi a ribbons. Ni a karan kaina sai da naji daɗin kan nawa dama a kwanakin nan ya isheni da ƙaiƙayi. Shiru nayi kawai zaune ina ƙarema kaina kallo, a take naji tausayin kaina ya kamani. Wasu hawaye masu zafi da ɗaci suka shiga sakko min. Hannu nakai na sharesu da sauri, saboda tuna nayi alƙawarin bazan sake kuka ba akan halin da nake ciki. Plate ɗin da aka kawo min na abinci na ɗan tsurama ido, sai kuma na tureshi gefe dan bana buƙatarsa a yanzu duk da uban ƙamshin dake tashi mai tabbatar da abincin zaiyi daɗi koda banga minene ba. Zamewa nai kwance a saman lallausan carpet ɗin da shima ke ta tashin wani irin ƙamshi mai daɗi, gashi tsaf babu datti. Gajiya da wahalar dana sha ya sa barci yin awon gaba da ni cikin ƙanƙanin lokaci..........✍️
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒔𝒆𝒗𝒆𝒏_
......“Madam bafa taci abincin nan ba, ko buɗe plate ɗin ma batai ba kuma tayi barci.” Janny ta faɗa cikin nuna damuwa.
Ƙaramar dariya Hajiya ta sauke tana wani lumshe idanu, sai kuma ta buɗesu akan Janny cike da salon irin na wayayyun mata da suka gogu da sanin duniya. “Barta yunwar ai ba ƴar gidansu bace, dan kanta ma zata ɗauka taci”.
Dariya tayi itama Jannyn da jinjina kanta. “Hakane Madam. Amma yarinyar yana da ƙyau fa sosai, ina ka samo shi haka? Ko dashi zamuje Lagos ne?”.
“Tsintacciyar mage ce, dan haka ma na dawo da tafiyarmu gobe kafin ta canja shawara. Saboda na kula babbar kaddarace wannan, kwalliya da sutura kawai take buƙata”.
Sosai Janny ta washe haƙwara, dan duk hausar da Hajiya tai tsaff ta gane kasancewar taji hausa sosai. Hajiya ma murmushin taketa faman yi, dan ita kanta tasan zata ƙaru da yarinyar sosai...
★Washe gari kamar yanda Hajiya ta faɗa suka tashi da shirin wucewa Lagos, harda Samraah nan dako sunanta basu sani ba har yanzu. Tunda suka tambayeta sau ɗaya tayi shiru basu sake tambayar ba. Tun jiyan kuma tana ɗaki kwance sai dai akai mata abinci a ɗakko kwano.. Janny ce mai ƙoƙarin kai-kawon, Hajiya dai nata bada umarni kawai, bakuma ta sake neman ganin Samraah ba tun shigowarsu gidan sai a yanzu da suka kwana suka yini dan tafiyar yamma zasuyi.
Ita dai Samraah bata san ina zasu je ba. Koda ta tambayi Hajiya kuma sai cewa tai ta jira zata gani. Badai tace ita ƴar Kano bace, zata bata mamaki ne. Al'amarin kamar asiri Samraah ta gagara cewa da Hajiya komai. Hasalima jinta take jikinta duk ya gama mutuwa ga bakinta ya mata nauyi. Sannan bata jin zata iya tsallake umarnin Hajiya sam koda cewa tai ta shiga wuta ta ƙone ko ruwan teku.
Tunda suka fito Janny taga Samraah na faman laɓe-laɓe a bayanta, Idanu Hajiya ta zuba musu kawai. Sosai ƙyawun yarinyar ya ɗauki hankalinta, sai taga tama ɗara yanda Jannyn keta kurantawa tun jiya. Baki ta buɗe zatai magana Samraah tai saurin faɗin, “Ina yini” cikin risinawa. Murmushi Hajiya ta ɗan yi tare da ɗauke kai, sai kuma ta sake maidawa ga Janny. “Wai nikam ashe amarya na kawo gidan nan ban sani ba. Irin wannan ɓoyo haka”.
Dariya Janny takeyi sosai itama idonta akan Samraah dake ta faman sinne kanta, da alama dai itama taji kunya, tunda koba komai ya kamata ta fito ta gaida Hajiyar da safe amma taƙi yin hakan. Duk sun fahimci taji kunyar ne suma, dan haka Hajiya ta kamo hanunta tana murmushi. “Daughter ai ko gaisuwa a fito muyi tunda dai naga baki son musan sunanki. Da alama dai yana da tsadar gaske, ko sai mun saya ne?”.
Karan farko na ɗago dara-daran idanuna masu shegen haske na sauke akan Hajiyar ina mai girgiza kaina da sauri, idanuna cike da ƙwalla alamar ina gab da shirin sakin kuka, dan haka kawai naji wani irin tsoro da shakkar matar ya shigeni mai tsananin gaske..
“A'a da alama dai ɗiyar tawa shagwaɓaɓɓiya ce, to mun haƙura tunda dai ba'a son mu sani. Mu sai mu saka miki namu sunan ai kawai kinga an huta canki canka ko”. Hajiya ta sake faɗa cike da salo tana murza hannuna a hankali.
Janny dai dariya take, yayinda ni kuma na duƙar da kai kawai, sai dai abinda Hajiyar ke min a hannu sam bana so, amma tsoron janye hannuna nakeyi..
“Baby zata shiga gaba koni Hajiya?”. Janny ta faɗa dai-dai muna isowa gaban hamshaƙiyar motar Hajiya data sha wanki take ta ƙyalli. Kallon Janny Hajiya tayi, yayinda ni kuma na ɗan ɓata fuska, a raina ina ayyana (baby kamar wata ƴar tsanar wasan yara) a fili kam sai na girgiza kaina a hankali na ce, “Sunana *_Samraah_*”.
A kusan tare Hajiya da Janny suka kalleni, Hajiya ta saki murmushi, Janny ta ce, “Woow nice name dear. Dole ki mana yanga irin wannan golden name haka”. Ta ƙare maganar tana ɗan rungumoni. Jikina na ɗan jaye daga nata batare dana sake cewa komai ba. Hakan yasa Hajiya ɗan harararta akaikaice alamar ta sakeni. Jayewa Janny tai tana faɗin, “I'm sorry maa”. Bata tanka mata ba ta kama hannuna muka shiga baya, dan tuni driver ya buɗe mana. Gaba Janny ta shiga, daga haka driver ya harba mota zuwa gate. Mun ɗan tsaya a bakin gate Hajiya tai magana da maigadinta, tare da bashi kuɗi masu yawa da suka bani mamaki. Shiko sai faman godiya yake bakinsa a washe har motar tai nisa da gate ɗin bai bar ɗaga mana hannu ba....
★ A cikin tafiyar ƙanƙanin lokaci muka iso airport, hakan sai yay matuƙar bani mamaki. Dan na fahimci airport ne muka zo, sai dai na gagara iya cewa komai dan ji nake tamkar an ɗaureni ne da sarƙa, bakina kamar an saka masa padlock. Wani irin sarawa naji kaina namin da tunani barkatai akan inda zasu kaini, a wane rami kuma na sake jefa rayuwata ni Samraah, kamar fa batun Lagos naji mutanen nan nayi, sai kuma zancen Hajiya ya sake tabbatar min da hakan. Dan bayan fitarmu a motar take sanarma drivern ta yay ƙoƙarin wucewa Lagos da sassafe gobe, bata son ya kwana a hanya bai iso ba. Shiko yana tabbatar mata da in sha ALLAHU cikin girmamawa. Daga haka Janny ta gungura akwatinansu ita kuma Hajiya taja hannuna muka shige ciki. Mun ɗan yi zaman mintuna goma a wasu kujeru kafin mu miƙe lokacin da ake sanar da parssinges ɗin Lagos suyi himma. Cikin kasa haƙuri da suɓutar baki saboda sunayen ALLAH da naketa ambato a ƙasan zuciyata na ce, “Muma wai jirgin zamu hau Hajiya?”. Kusan lokaci guda Janny da Hajiya suka saki ƙaramar dariya, kafin Hajiya ta kamo hannuna cike da kulawa. “Eh Samraah muma jirgin zamu hau zuwa Lagos, dan yafi sauƙin tafiya sai kiga nanda wani ƙanƙanin lokaci mun isa. Idan kuma baƙya son zuwa ne bazamu takuraki ba, tunkan driver yay nisa sai na dakatar da shi ya koma da ke, amma fa ba can gidan zaki koma ba, dole garinku zaki faɗa ya maidaki gidanku”.
A take batare da nasan dalili ba na ruɗe, na shiga girgiza kai idanuna na cika da ƙwalla. Cikin rawar murya na ce, “Hajiya kiyimun rai. Wlhy dana koma gida gara ma ki kasheni kawai. Sannan kuma shima ya tabbatar min zai iya salwantar da dangi.....” sai kuma nai shiru tamkar wadda aka tsawatarwa har ina kai hannu saman bakina na dafe. Ganin kallon tuhumar da Hajiya ke bina da shi da Janny ya sani sakin hawayen suka zubo. “Na yarda Hajiya ki kaini koma inane, amma banda maidani gida, zaki sameni a mai yi miki biyayya ɗari bisa ɗari...”
“Miya samu dangin naki?”.
Hajiya ta katseni tana mai tsatstsareni da idanu. Ruɗewa nayi jikina ya fara rawa da lips ɗina. Saina fara ƙoƙarin jan jikinna baya daga kusa da su. Dai-dai nan aka sake shelanta neman passinges na flight Lagos. Hajiya ta ɗan ja numfashi ta fesar, sai kuma ta sauke ajiyar zuciya da kamo hannuna. “Ok ok kiyi haƙuri ba sai naji ba. Muje kawai kar jirgin ya wuce ya barmu”. Ƙoƙarin tirjewa nayi Hajiya ta sake damƙoni da ƙyau tana min magana a hankali mai nuna alamar lallashi, sai dai nauyinta ya wuce duk yanda mai karatu ke hasashe....
Sosai jikina ke maƙyarƙyata a cikin jirgi saboda zantukan Hajiya. Sai faman maƙurewa nake a waje ɗaya alamar dai a firgice nake. Hajiya kam na riƙe da hannuna katamau tamkar zan tsere mata ne. Janny dake daga can ɗayan gefenmu kam kallonmu kawai take tana danne dariya. Dan duk wanda ya kalleni zai ɗauka ƙauyanci ne cike taf a kaina ba wai tsoro ba. A haka dai jirgi ya lula sama harda yunƙurin amai na amma na danne, bayan ya gama dai-daita dole sai da Hajiya ta rakani restroom nayi sa. Cikin ƙanƙanin lokaci sai ga zazzaɓi ya rufeni ruff abinka da wadda bata gama murmurewa ba dama. Koda muka sauka a Lagos kaina a juye yake ma gaba ɗaya. Dan bana iya gane komai yanda ya kamata har muka shiga mota zuwa anguwar da Hajiya take....
Babbar anguwace mara yawan cinkoson jama'a kamar ba'a cikin Lagos da nake jin ana faɗa ba. Duk da kuwa kafin mu iso cikinta mun shiga cinkoson matuƙa wani gurin ma da ƙyar muka fita, dan tafiyarmu daga filin jirgi zuwa gida yafi tafiyarmu daga Kano zuwa Katsina nisa, duk da dai shi wancan gari da gari ne, wannan kuma cikin gari dole akwai banbanci. Iya ƙagara na ƙagu a zo gida, dan a yanzu ma amai ne keta faman taso min tunda muka shiga motar. Da alama Hajiya ta fahimci halin da nake ciki ne ya sata siya min lemon zaƙi a hanya tace na dinga shanshana ɓawon, sai goro da shi kuma na dinga ɗan ci kaɗan-kaɗan. Wannan ne ya riƙeni zuwa gidan Hajiya.
Anan ɗin ma dai maigadi ya buɗe mana gate, sai faman washe baki yake da jerama Hajiya sannu da zuwa. Da taimakonsa mai taxi ɗin daya ɗakkomu ya fidda mana akwatinansu biyu madaidaita. Janny ta tsaya biyan mai taxi ɗin, yayinda ita kuma Hajiya ta kama hannuna muka nufi wata ƙyaƙyƙywar ƙofa fara da adon golden. Wannan gidan yafi gidan Abuja girma, lokacin da muke shiga falon kuma ya sake tabbatar min da yafi wancan ɗin kayan alatun more rayuwa ma. Dan falon ƙato ne na gaske, ga wasu manya-manyan hotunan Hajiya da wani mutum a jiki tamkar zasuyi magana dan girma. Sai ƴammata biyu masu tsananin kama da juna sannan suna kama da mutumin. Fitowar wasu ƴammata biyu da dattijuwa ya katse min kalle-kallen hotunan da nakeyi. Nai tsai ina kallon dattijuwar da ƴammatan da suka zube gwiwa bibbiyu suna gaida Hajiya da jera mata sannu da zuwa. Itako amsawa take cike da nuna isa da gadara tamkar ba Hajiyar dana sani daga jiya zuwa yau ba. Dan bayan ta gama amsa su a taƙaice tai musu nuni da ni. “Kuje da ita sashenku kafin na nemeta, duk kuma wanda ya mata wata any magana sai na wulaƙantasa ta yanda sai yayi dana sanin sani na a gidan nan. Ina sauran suke?”.
Da sauri dattijuwar ta amsa mata da “Madam Oyinka ta ɗauki Surayya da Umayyah, dan tare sukazo da wata baƙuwa tun jiya da yamma kamar yanda na sanar miki a waya”.
Kaɗan Hajiya ta yamutse fuska tana kallon agogo, kamar zatayi magana sai kuma ta fasa, dai-dai nan Janny ta shigo maigadi biye da ita jaye da akwatuna. Hannu kawai Hajiya ta ɗagama Dattijuwar alamar suje. Miƙewa duk sukayi suna min nuni da ƙofa.........✍️
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒆𝒊𝒈𝒉𝒕_
_______________
Toh Nazo maku
Da kayan arziki
Kudai kunsan mata sai da gyara
Macen da Bata da gyara ta zama yar kallo a gidan ta
A katafaren kamfanin mu na BEENAD HERBAL MEDICINE
Mun shahara wajen kawo maku ingattatun magunguna mata da na gyaran jiki,kayan mu guarantee ne
Muna da
Shedaniyar gumba
Gumba mai saying
Garin mai kabbara
Mai dalalan miyau
Wayyo dadi
Mai bunsuru
Dan jarida
Soyayya dole
Bakin kyalle
Tadire ta girke
Gumba mai likkafani
Maza taye
Zumar kwakwa
Zumar ridi
Zumar dabino
Zuma mai ma'ul ijaba
Farin jini
Mallakoki
Gumba kalla kalla da dai sauran su
A BEENAD HERBAL muna da turarukan wuta da humrah kalla daban daban sai Wanda kika zabba
Ga kuma maganin slimming
Gyaran nono
Maganin hips
Maganin Kara kiba
Da dai sauran su
Kayan mu tested and trusted ne
Muna maraba da masu siyan Daya ko sari
Muna Nan cikin garin kaduna
Kuma muna tura Kaya duk inda kike da yardan Allah
Ni ce taku har kullum
AMINA GACHI
07034404975
CEO BEENAD HERBAL MEDICINE &INCENCE
KADUNA
Phone no 07034404975
____________
......Wani irin yamutsawa kaina ya shiga yi, dan gaba ɗaya suffar ƴammatan nan da dattijuwar batai kama data mutanen kirki ba, sai irin gogaggun matan barikin nan da idanunsu ya gama gogewa. Juyowa nai a karan farko na dubi Hajiya, itako ta ɗauke kanta gefe fuskarta babu alamar wasa a yanzu. Kamar ba itace keta faman min murmushi ba a Abuja da lallaɓani. Kallona na maida ga Janny da itama take kallon Hajiyar, a karo na farko na ce, “Dan ALLAH Hajiya ku barni a wajenku”.
Wata irin tsawar data gigitani Hajiya ta daka min. “Ka jimin shegiyar yarinya, su ɗin sama suka ce miki suna da gida bayan wannan da suke ciki?!! Zaki wuce ko sai na banbance miki tsakanin aya da tsakkuwa ku gammin yarinya da tsurku. Kin fini sanin abinda ya dace ne!”.
Rawa jikina ya cigaba dayi har ina neman kifewa ƙasa. Bamma san sanda nabi wanda akace nabin ba. Da harara Hajiya ta raka bayansu, sai dai suna ficewa taja tsaki da fincike gyalen abayar data naɗe kanta da shi. Tuni gashin dokin kanta ya bayyana, ta jefar da ɗan vail ɗin tana magana cikin yare, sai kuma ta miƙe ta fincike abayar ma. Anan ɗin ma wani wandon bomshot ne na jeans ya bayyana a jikinta da riga best....
“Hajiya ya haka?”.
Cewar Janny tana dariyar shaƙiyanci. Da sauri ta harari Jannyn da zagaya hannunta saman kai ta ce, “God for bed yoo, sunana Jannifer Can hajiyansu su ƙarata da shi bani ba Mtsowww!!. Yanzu ma zanyi shirin Church pastor yay min addu'a akan hakan. I beg, give me wine na ɗan sha ma ko zandawo hankalina da ƙyau”. Tai maganar tana komawa saman kujerar ta zube. Wucewa Janny tai hanyar kitchen, babu jimawa ta dawo da kwalban giya mai tsadar gaske da cups guda biyu. Ita ta ɓalle ta zuba musu tare da miƙamata itama ta ɗauki ɗaya,