Showing 36001 words to 39000 words out of 438336 words
“Samraah kin san mi kikayi kuwa? Kin san wanene wannan mutumin kuwa? Kin san ƙyautar mi ya baki kuwa? Amma kika watsa masa ƙasa a ido ta hanyar maida masa bayan ya fifitaki sama da kowa. Kuɗi duk ya bama sauran 50-50k, amma ke makullin mota ya baki batare da ko dubawa kinyi ba kika ɗauka kika maida masa...”
“Mata fa dai?”.
Na tambaya da iya gaskiya ta. Shima cike da ƙwarin gwiwa ya amsa min da “Yes Mota Samraah. Shiyyasa a kullum nake faɗa miki ke ɗin mai sa'a ce dear”.
Kaina na ɗan girgiza da murmushin basarwa, na ce, “Humm to amma Sir mi zanyi da shi idan na riƙe? Sannan wace amsa zan bama iyayena idan sun tambayen a ina na samu mota? A shi karan kansa mi ma zaisa ya mana irin wannan ƙyautar haka dan kawai munyi hira da shi?”.
“Tab ɗin, wlhy yarinyar nan baki da hankali...” ya faɗa cikin ƙunar rai, a take na sake tamke fuskata dan kalmar tasa ta mun matuƙar zafi a zuciya. Duk yanda naso na shanye na gagara hakan, kai tsaye nace masa, “Sir minene abin rashin hankali anan? Bayan kuma na faɗa maka hujjata. Wannan fa rayuwata ce”
Wani irin tsayawa yay duka hannayensa riƙe da ƙugunsa kawai yana kallona tamkar ya samu television. Ni kam na sake fuskewa kamar ban san yanayi ba. Na fahimci takaicina ne ya maƙureshi ya hana shi cigaba da magana. Dan a fusace ya sa ƙafa ya tunkuɓar da flower base ɗin da akai ado da ita a office ɗin, sannan ya ce, “Samraah out. Get out of my office now..”
Ko kallonsa banyi ba na juya nai ficewata. In ma ca yay na bar Company ɗin gaba ɗaya daga yau banda matsala da hakan. Ko takan Mansoor banbi ba nai ficewata gaba ɗaya daga gidan. Napep na tare zuwa garejin su Yaya Musaddiq. Na samu suna shirin shiga sallar azhar, sai dai shi Yaya bai kai ga tafiya ba yana ƙoƙarin ɗaura alwala ne. Tun kafin na ƙarasa inda yake na fahimci ya zuba min ido.
“Lafiya kike?”.
Ya faɗa dai-dai ina isowa gabansa shi kuma yana wanke ƙafarsa. Mai makon amsa sai na tura masa baki. Kansa ya girgiza kawai yana sake faɗin, “Je can ki zauna muyi salla to, idan na dawo sai kiyi taɓarar”. Daga haka ya wuce ya barni a wajen dan ya kammala alwalar...
💫´⊙ω⊙💫⊙ω⊙💫⊙ω⊙`💫
Zaune yake a falo tare da Hayatu da Juliet, tab.. ce a hannunsa, ƙafafunsa miƙe saman Centre table da aka turo gabansa sosai. Hankalinsa gaba ɗaya nakan screen ɗin tab ɗin, hannunsa ɗaya rike da haɗaɗɗiyar chocolate yana ci a hankali tamkar baya so. Yayinda Juliet ke bayani akan abinda ya zaunar da su ɗin, dan itama dai laptop ce a hannunta, sai Hayatu dake riƙe da takardu ta gefenta. Abinda juliet ɗin ta faɗa na ƙarshe ne ya sakashi ɗagowa cikin rashin sakewar nan tasa ya zuba mata ido. Da sauri ta risinar da nata dan Maash nada wani kwarjini dakan hana mai kallonsa iya masa kallon ido cikin ido na tsawon lokaci, koda kayi jarumtar yin hakan da zaran shi ya zuba nasa cikin naka zaka ji ka takura. A ɗan daƙile ya ce, “Ina son magana da Mustapha. Sannan ai cancel ɗin Thailand a cikin schedule namu a maida Finland”.
Atare su duka biyun suka amsa masa dan zancensa ya shafi kowannensu. Babu ɓata lokaci kowanne ya shiga yin abinda aka saka shi. Juliet ce ta fara ɗagowa cikin harshen turanci tana tambayarsa, “Sir komai zai zama ne de same date?”.
Kamar baima jita ba aikinsa yake, sai da ya mula dan kansa sannan ya bata amsa da “Uhm”. Cikin girmamawa ta jinjina kanta da amsa masa ta cigaba da aikinta. Dai-dai nan shima Hayatu ya taso daga inda yake da waya a hannunsa. Ta gefensa ya ɗan tsaya cikin risinawa ya miƙa masa. Batare daya ɗago ba a hankali ya furta, “Sa a hans free”. Da sauri Hayatu ya maidata hans free, sai ga muryar wancan da ya kira da Mustapha rangaɗam. Duk da a cikin waya yake cikin girmamawa ya gaishesa, zaka tabbatar da hakanne ta yanda yake magana cikin ƙanƙan da kai. Shikam kamar yanda ya saba ya amsa a taƙaice. Sannan suka tsunduma maganarsu, duk dai akan harkar business ne, mafi yawan maganar kuma Mustaphan keyinta.. ba wata doguwar magana sukai ba ya barsa suka cigaba da magana da Hayatu. Dai-dai Hayatun na ajiye wayar shima alamar sunyi sallama ɗaya daga cikin securitys ɗin gate yay sallama tare da yin knocking. Hayatu ne yaje garesa yana amsa masa sallamar. Jin abinda security ɗin yace ya sashi ɗan wara ido waje. Sai kuma ya juya cikin falon da sauri. Cikin ɗan yanayin rawar harshen wanda ya shiga ruɗani ya ce, “Sir Baba prof.. ne a gate”.
Cak Maash ya dakata da abinda yake, sai kuma ya lumshe idanunsa tare da buɗesu luuu gaba ɗaya akan Hayatun. Bashi da alamar cewa wani abu, Hayatu kam duk ya ƙagu yace ɗin. Idanun nasa ya maida ga tab ɗin abinsa batare da yace komai ba. Sake birkicewa Hayatu yayi, sai dai baida tacewa.
“A buɗe masa”.
Zabura Hayatu yay yana sauke nannauyar ajiyar zuciyar da sai da ta saka Juliet danne dariya. Dan haka ya harareta ya nufi hanyar fita da sauri. Shiko Maash aikin gabansa ya cigaba dayi hankali kwance. Mintina huɗu ba'a cikaba sai gasu kuwa. Baba prof.. ne a gaba. Tun a taku biyu ya tsaya yana bin falon da kallo, kafin ya sauke ƙyawawan idanunsa na tsufa akan santalelen jikan nashi mai ji da lokacisa. Murmushi ya saki a hankali, sai kuma ya cigaba da shigowa cikin falon guards ɗinsa guda biyu biye da shi. Sai Hayatu a gefe. Juliet ma tuni ta miƙe tsaye. Cikin girmamawa ta shiga gaishesa, ya amsa mata da kulawa, har lokacin kuma Maash bai motsa ba balle ya kalla kakan nasa. Hayatu ne yayma guards ɗin Baba prof... da Juliet magana dan haka suka fice suka barsu su biyu.
A karo na babu adadi Baba prof.. ya sake sakin murmushi. Idanunsa akan Maash ya ce, “Fushinne har yanzu? Common sweetheart ya kamata ka huce mana. Kaifa yanzu babban mutum ne ba little Awwab ɗin nan ba mai hawa saman wuyan grandpa ɗinsa yay doki saboda fitinarsa. Be a man mana my baby boy”.
Fuska Maash ya sake tsukewa. Batare da yayi magana ba ya dangwarar da tab.. ɗin hannunsa yana miƙewa kamar a fusace zai wuce. Caraf Baba prof.. ya damƙo hannunsa, jawosa yay kawai ya faɗa jikinsa ya rungumesa tsam-tsam yana dariya. Sun jima a haka Maash nata faman sauke ajiyar zuciya, yayinda Baba prof.. keta murmushinsa shi dai. Sai da ya tabbatar ya gama haɗiyar zuciyar kafin ya ɗagosa. Hannu yasa saman kansa ya birkita gyararriyar sumarsa da yau bai ɗaure ba. Babu shiri Maash ya saki murmushi daya sake ƙawata ƙyawunsa. Baba prof.. kuma ya ƙyalƙyale da dariya tare da jamasa dogon hancinsa sannan ya sake maida hannunsa kan sumar tasa ya shiga kwantar da ita yanda take.
“Dibeka so cute idan kana murmushi. Amma ka dinga ɗaurema mutane fuska har ni ɗin ma Kakanka ban tsira ba. Kai nidai naga takaina da kai balaraben Nigeria”.
Murmushin Maash ya sake yi, batare da yace komai ba ya girgiza kansa kawai yana nufar kujera ya zauna kamar yanda Baba prof.. yayi. Cikin girmamawa ya gaida kakan nasa, shiko ya amsa masa cike da kulawa, sai kuma yabi falon da kallo yana cigaba da faɗin, “Mutumina alƙawarin ALLAH dai ya cika ka dawo mafari. Hakan nada ƙyau kuma naji daɗi kwarai da gaske. Ina fata kuma za'amin afuwa da rashin cika alkawarin dawowa da nai jiya. Gangar jikin nawane kawai acan, amma zuciyar na nan. Shiyyasa ma ina sauka a Lagos ko gida banje ba na sake biyo jirgi zuwa nan ɗin.”
“Ba komai ya wuce ai, ina fatan ka dawo cikin ƙoshin lafiya”. Maash ya faɗa cikin tausasa harshe duk da dai maganar da ƙyar take fita. Baba prof.. bai damu ba, dan yafi kowa sanin wanene jikan nasa. Wannan yanayin nashi kuwa halittarsa ce, tun yana ƙaraminsa baida sakewa da mutane. Sannan haka yake dai babu yawan magana. Wasu abubuwa da suka faffaru kuma suka sake maidashi dunɗun dukum ya zama miskilin gasken gaske. Gashi nan dai babu yabo babu fallasa a ɓangaren kirki. Dan babu wanda ke ɗaga masa yatsa bai karya ba. Ya iya rikici da rigima ƴar gaske. Dan tabbas Maash akwai rikici, tsagerane na bugawa a jarida, sai dai yanayinsa na shiru-shiru yasa sai ya zuba maka tsiya yay kamar bashine yayi ba, in kuma za'a tambayi mutum dubu su shedesa suma akan bashi ɗin ne yay ba. Sai dai su da sukai masa sanin ciki da bai na rayuwa, musamman ma shi kakansa da mahaifinsa da mahaifiyarsa sun san shine ya yin......✍️
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚 - 𝒕𝒘𝒐_
.......“Da kika gudo kika barni yanzu ban kawo kaina ba?”. Mansoor ya faɗa dai-dai suna ƙarasowa inda nake shi da Yaya Musaddiq. Baki na ɗan murguɗa ta cikin mask ɗina, a zahiri kam nai ƙasa da kaina sai dai bance komai ba. Sai Yaya Musaddiq ne ke dariya. Ni dai bance komai ba, sai da Mansoor ya sake faɗin, “Bazaki ban haƙuri ba?”.
Bakin na sake turawa. Sannan na ce, “To kayi haƙuri”.
Murmushi Mansoor yay yana kaiwa zaune. “Ai dole ma na haƙura dan bana iya dogon fushi da ke. Ga yaya Musaddiq nan ma shaida ne”.
Murmushi Yaya Musaddiq ya sake saki, ni kuma na ɗan harari Mansoor ɗin. Shima murmushin yay a lokacin, tare da ɗan taɓe bakinsa ya ɗauke kansa gefe. Sai kuma ya sake juyowa gareni. “Mi MD yace dake?”.
Mask ɗin na cire ina kumbura fuska kamar MD ɗinne har yanzu a gabana. Labarin komai na basu, shi kuma ya faɗama Yaya Musaddiq komai tun daga farko. Sosai naga farin cikin abinda nai ɗin a fuskar Yaya Musaddiq, har takai ya kasa haƙuri ya dafa kaina da faɗin, “ALLAH yay miki albarka Kandalata. Abinda kikayi shine dai-dai, dan nima anan banga wani dalilin da za'a baki ƙyauta harta mota ba ki amsa. Ki cigaba da haka, dan gaskiya itace RUHIN dukan MUSULMI na ƙwarai. Sannan ita mace tana bine ta kowacce hanya domin kare mutuncinta da kimarta a al'adance da kuma addinance.”
“Nagode Yaya”.
Na faɗa cikin zumuɗi da jin daɗi. Dan kalamansa sun ƙaramin ƙwarin gwiwa ƙwarai da gaske. Ganin Mansoor bai tanka ba na ɗan juyo na kallesa. Murmushi ya sakar min, nima sai na mayar masa da murtani. Kaina tsaye na ce, “Amma kaima zaka maida musu?”.
“In sha ALLAHU”.
Ya bani amsa cikin tabbatarwa. Nan ma nayi farin ciki, daga haka na mance da dukkan damuwata muka koma hira mai daɗi. Harga ALLAH ina matuƙar son waɗan nan mazajen biyu, dan sunada matuƙar muhimmanci a rayuwata. Sun kuma taka rawa mai ƙarfin gaske da in har zan nuna kaina sai na haɗa da koda inuwarsu ce. Ko kaɗan bamuyi maganar videon nan a wajen ba saboda tsaro, sai da muka koma motar Mansoor sannan muka ƙarasa. Yaya ya bada shawarar mu binciki ɗan sanda mai gaskiya da zamu iya damƙama video ɗin kawai batare da sunanmu ba, kokuma mu haƙura a gogeshi mubar zancen, ko bajima ko ba daɗe idan har halin mutumin nan ne hakkin rai bazai barsa ba. Amma maganar yin fito-na-fito da shi bama ta taso ba a garemu.
Harga ALLAH maganar Yaya Musaddiq bata mun daɗi ba, taya kawai dan mutum nada kuɗi a dinga nuna tsoronsa haka bayan akwai hujja mai ƙarfi a tare da mu. Amma sai na danne yanayina nace mu sakesa a media kawai, dan a wannan zamanin banga wani ɗan sandan da suke hasashen samu ba. Su duka basu goya da bayana ba. Shima Mansoor yana bayan shawarar Yaya Musaddiq ɗin ne. Dole nima nabi ra'ayinsu, duk da tun farko dama ni na fara kawo shawarar kaiwa ƴan sandan, banbancin shawarar tasu da tawa ƙalilance. Bayan mun kammala tattaunawar munbar Yaya anan ni kuma Mansoor ya wuce kaini gida. Muna tafiya muna hirarmu mai daɗi, duk da yaso mu tsaya muci abinci naƙi yarda da hakan. Koda mukaje gidan ma sai da muka ɗan ƙara taɓa hira, duk da dai hirar tamu ma dai akan bikinmu ne, dan iyayensa zasu sake zuwa a satin sama domin saka rana. Ya kuma tabbatar min da bawani lokaci mai tsayi za'a saka ba. Dan shi ya gama kammala komai amarya kawai yake jira. Naji kunyar furucin nashi sosai, dan haka na ɓalle murfin motar na fita abina. Ina jiyo sautin dariyarsa ban kulashi ba, sai da zan shige gida gaba ɗaya ne na juyo. Ido ɗaya ya kashe min, aiko nai wuff na afka ciki..
A falo na samu duka mutanen gidan tsaye carko-carko har Abbas yau yana gida. Ga kayana a barbaje an musu filla-filla. “Yauwa ga ɓarau-ɓarau ɗin nan ta dawo”. Furucin Bibaa ya dawo da hankalina kansu. Kafin nai wata magana kawai naji saukar mari. Duk da azabarsa ta matuƙar ratsani banyi ko gezau ba. Sai wanda ya marenin na zubama ido kawai, ba kuma kowa bane face Abbas. Nunani yay da ɗan yatsa tamkar zai tsokale min ido ya ce, “K dan uwarki kawo sarƙar Mom da kika sata, shegiya ɓarauniya mai kama da aljanun daren salla”.
Cikin dakiya irin tawa na ce, “Karka sake zagar min uwa. Sata kuma kanku ya kamata ku bincika, tunda kune ke shiga ɗakin Mom ɗin ai. Ni ba ɓarauniya bace, kuma in sha ALLAHU babu wani tsananin rayuwa da zaisa na aikata ta”.
Daga haka na duƙa domin tattare kayana. Amma sai ji nai an shaƙoni ta baya. Har hijjab ɗina na matsemin maƙoshi. Da sauri nasa hannu naja hijjab ɗin sama. Sannan na miƙe. Baby ce mai riƙon nawa yanzu, itama hannu ta ɗaga zata maran, sai dai kafin ta sauke min ni na sauke mata nawa yatsun biyar akan farar fuskarta. Saurin janye nata hannun tai tare da sakina ta haɗa duka hannuwanta biyu ta riƙe kuncinta. “Karki soma fara wannan wasar dani a gidan nan, shima daya maran ɗin ba ƙyalesa nai ba balle ke shashasha”.
“Toni bari na marekin sai ki haɗa ki rama” Mom ta faɗa tana wani zaburowa kaina. Banyi ko motsi ba harta ƙaraso ta maran ɗin a haggu da dama. Sannan ta shaƙoni. Kakari na fara, amma ko gezau bata da alamar sakina. Sai ma faɗi take, “Dan ubanki ina sarƙata? Ina kikaje kika saida ta? Dan nasan fitar da kukai ke da annamimin mai saki yin komai a gidan nan abinda kuka je saidawa kenan. Kuma wlhy bazan yarda ba, sarƙata ko kuɗinta”.
Zuwa yanzu kwata-kwata bana iya numfashi da ƙyau, hakan yasa Abba da tun ɗazun baice komai ba ya ƙaraso da sassarfa yana ƙoƙarin cire hannun Mom ɗin daga wuyana. “Kinga Jalilah saketa Please. Sakarta ta faɗa inda take kada ki kasheta mana”. Sam bata da alamar sakin nawa kuwa. Dan haka ya tureta da ƙarfinsa har sai da tai taga-taga zata faɗi, ni ma dai zubewa nai a wajen ina sauke wahalallen numfashi a gwagwgwame. Ga tari dake neman sarƙeni. Da sauri auta yazo gabana ya duƙa yana miƙamin ruwa. Banyi musu ba na amsa, dan ina buƙatarsa. Sauri-sauri na fara sha, sai ji nai an kaɓe ruwan ya zube jikina gaba ɗaya. Yayinda Auta ya fasa wani kukan azaba. Da sauri na tashi zaune, dan bata ruwan da aka zubarmin nake ba ta shi nake. Yaron na sona sosai a gidan, kawai dai dan baida yawan magana ne sai idan shi yaso, dan miskili ne na bugawa a jarida. Ba komai akai masa ba, Baby ce data figesa daga kusa dani kawai yake ma ihun kuka, Bibaa kuma na huci alamar itace ta kaɓar da ruwan da ya bani......
✨(☯෴☯)(☯☯)(☯෴☯)✨
Badan Maash yaso ba dole ya shirya suka fita da Baba prof.. zuwa Company, daga can suka tsaya sukaci abinci a wani haɗaɗɗen restaurant. Daga haka suka wuce airport domin masa rakkiya, dan ya rasa jirgin sha biyu sai ya sake bucking na yamma. A hanyarsu ta zuwa airport ɗin