Showing 231001 words to 234000 words out of 438336 words
min.
“Karna fito na sameki a wajen”.
Ya sake faɗa dai-dai yana shigewa cikin cikin closet ɗinsa. Hannuna na dunƙule kamar zan kaima bango naushi sai kuma na tausayama kaina dai. Dan nasan nice zan sha wahalar a ƙarshe hannunna ya rugurguje a banza. Hararar inda ya shige ɗin nayi ina cizar lips ɗina da ƙarfi, ga hawaye share-share a fuskata. Jin motsin kamar zai fito ya sani zabura na nufi bathroom ɗin. Dole ina ji ina gani na haɗa ruwan wankan nai ƙoƙarin fara yi. Wankan nake ina hawaye da hango irin bala'in da zai iya biyo baya. Dan wlhy abin bazai zama mai sauƙin ba a gareni. Gara sashen Ummie da nake zama shi wannan suna ganin ai kamar ina cutuwane shiyyasa aka ɗagamin ƙafa. Amma nan fa? Ni kaina idan an titsiyeni ban san mizan ce ba. Dan nayi alƙawarin in har bada kansa ya fito ya bayyana musu wacece ni ba wlhy ko za'a kasheni bazan faɗa ba. Sai da na kammala wankan sannan hankalina ya tashi, dan ban san yaya zanyi da kayan sakawa ba kuma. Bathrobe ɗin sa na ɗauka na saka. Sallar walha da nake son zuwa nayi dan lokacinta yayi ya sani haƙura na fito, amma sai da na leƙa cikin ɗakin sannan. Shiru babu motsin komai, sannan a iya hangena ban hango alamar akwai mutun ba. Ɗan ajiyar zuciya na sauke na fito a ɗan ɗarare. Nannauyar ajiyar zuciya na sauke ganin tabbacin baya ɗakin, tunanin sauri na shafa mai yazo min, dan haka na nufi gaban mirror ɗin nashi. Zama nayi tare da bin kayan dake akai da kallo, cikin ɗan taɓe baki na furta, “Sai kace mace”. Da ƙyar na iya gane man shafawa, ina son na fara dubashi ina tsoron yin jinkirin da har zai dawo ya saman a wajen. Da sauri-sauri na shafa man da duk abinda zan iya amfani da shi a wajen. Na miƙe raina fal tashin hankalin kayan daya kamata ace na saka ya shigo. Daburcewa nayi dan abin yazo min a bazata. Rasa makamar riƙewa ta sani komawa kan stool ɗin kujerar na zauna tare da duƙar da kaina. Baiyi magana ba, sai madaidaicin akwati da yazo ya ajiye gab dani. Juyawa yay yayi ficewarsa yana faɗin, “Zanje wajensu, da munyi salla zasu shigo. Zaki iya zuwa duba Ummien kafin”. Daga haka yay ficewarsa. Da kallo na bisa duk kaina duk a ɗaure. Sai dai furta zan iya zuwa duba Ummie ne yay matuƙar wanke min zuciya. Mikewa nai cike da zumuɗi harda daka tsalle dan farin ciki, tuni na nema damuwata da tunanin wasu baƙi da ya ishi mutane da zancensu na ɗauki akwatin daya ajiye ɗin. Saman gado na kaisa na buɗe.........✍️
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒏𝒊𝒏𝒆𝒕𝒆𝒆𝒏_
.......Kayane ɗinkakku har kala biyar, sai kayan ciki b&p 12-12. Sosai naji kunya ta kamani. Wani gefe na zuciyata kuma na mamakin inda yasan seize ɗina. Hatta da ɗinkunan dai-dai jikina cif. Zumuɗin tafiya wajen Ummie ya sani ajiye komai gefe na shirya cikin doguwar rigar lass pink mai ƙyau mara nauyi kuma. Komawa nayi gaban mirror ɗin ina kallon kaina fuskata cike da murmushi. Na dawo Samraah ta ƴar jarida ƴar gayu. A take yaya Musaddiq yazo min a rai. Hawaye naji sun cika min ido na kewarsu. Tunda abin nan ya faru bamuyi waya ba. Dolene idan na dawo wajen Ummie na roƙesa aron waya nayi kiransu har su aunty Zakiyya ma. Da wannan tunanin na ɗauki turarensa na fesa tare da ɗaukar ɗankwalin nai simple ɗauri. Mayafin cikin akwatin guda uku na ɗauka ɗaya nayi salla dan babu hujjab. Ina idarwa na miƙe cike da zumuɗi na tattare duk kayayyakin dana baza na maida bathrobe ɗin danai amfani da ita da towels ɗin daya cire na maida bayin. Sake ɗan gyara fuskata nayi da faran fauda ɗin dana gani sannan na fice.
Nayi mamakin ganin falon ƙal yanzu yana zuba ƙamshi ga sanyin ac duk da dai ɗazun ma ba wani datti bane. Amma daga gani yanzu kasan an sake gyarashi. Kaina tsaye na fito batare da jin damuwar idan na haɗu da wani yaya zanyi ba. Koda na shiga sai da na sauke ajiyar zuciyar jin daɗin ganin babu kowa a falon. Dama ba lallai na samu masu aiki ba, dan yanzu lokacin hutu ne an gama na safe sai kuma azhar tayi. Kaina tsaye na haye sama harda ɗan guduna.
Naji matuƙar farin cikin samun sashen Ummie fes da shi, ga ƙamshi na tashi tako ina. Da alama aikin Mama Balki ne kuwa. Ilai kuwa a ciki na sameta tana bama Ummie abinci. Da gudu na naje na faɗa jikin Ummie ina mai sakin kuka. Dariya Mama Balki ta sanya min, niko ko'a jikina murnar ganin Ummie kawai nakeyi. Sai da na gama murnata na ɗago ina kallonta. Itama kallona kawai takeyi kamar ta samu television. Murmushi na sakar mata idanuna cike da ƙwalla na ce, “Ummie na i miss you”.
A bazatar da ta bamu matuƙar mamaki mukaga ta saki murmushi tare da kai hannu ta shafa kaina. Sai kuma ta saki kuka. Ruɗewa mukai mu duka. Ƙoƙarin miƙewa nake a jikinta amma sai ta riƙeni da ƙyau, sai kawai na sake rungumeta nima ina kukan. Mun jima a haka kafin na ɗago jin kamar jikinta ya saki. Mama na kalla, ta sakar min murmushi itama tana share ƙwallar idonta. A raunane ta ce, “Tayi barci. Dan tasha maganinta bayan na gama bata abinci. Gani nayi ga sake jawo kwanon sai nayi zaton bata ƙoshi ba shine na sake zaman bata kika shigo.”
Nawa hawayen nima na share. Sai kuma na tashi a jikinta muka taimaka mata ta kwanta. Zama nayi a kusa da ita hannunta cikin nawa ina jin matuƙar farin ciki da ganinta. Sai matuƙar tausayinta dake cimun rai da zuciya dan duk ta rame min a ido alamar ciwon ya bugeta sosai wannan karon...
🩸🩸🩸🩸
“Kamar ya an sallamesu? Waye ya sallame sun?”. Ta faɗa cikin daka tsawa. Ƙanƙame jiki nurse ɗin tayi jikinta na rawa. Cike da tsorata da birkicewar Hajiya ƙaramar ta ce, “Am sorry Maa. Wlhy ni ban san wanda ya sallamesu ba, naga kawai sun fito ne amma Dr Larai ce ta musu rakiya har mota. Muma ganin haka yasa muka rakasu”.
Wani irin tashi sama jijiyoyin Hajiya ƙarama sukayi, a fusace ta sake dakama Nurse ɗin tsawa. “Get out of my side!!”.
Ai da gudu Nurse ɗin ta fice kuwa. Har neman faɗuwa take, ALLAH dai ya taimaketa ta dafe bango. Tana fita itama Hajiya Ƙarama ta fice a fusace. Sai da taje ƙofar office ɗin Dr Larai sai kuma ta gyara yanayinta cikin jan numfashi da saukewa. Knocking ƙofar tayi, aka bata iznin shiga. Dr Larai na zaune da waya a hannunta da alama akwai abinda take yi. Shigowar Hajiya ƙaramar ya sata ajiye wayar tana murmushi. Da girmamawa matsayin Hajiya ƙarama na shugaba a asibitin ta ce, “Welcome Doctor ashe kin shigo? Yanzu nake tunanin zuwa na duba kafin na wuce gida ai dama”.
Murmushin yaƙe Hajiya ƙarama tayi, tare da jan kujera ta zauna. Hakan yasa itama Dr Larai komawa ta zauna. Gaisuwa sukai a mutunce. Kafin Hajiya ƙarama ta tambayi bataga petient ɗinta ba. Kota canja musu ɗaki ne?. Da ɗan mamaki Dr Larai ta ce, “Kunyi saɓani kenan? Dan sun wuce gida. Yaron nan naku rigimamme ne na bugawa a jarida. Dan har office ɗin nan yazo ta tirkeni sai na bama yarinyar nan sallama. Babu irin son fahimtar da shi ɗin da banyi ba dan ya barta ta ƙara samun sauƙi sosai amma fir yaƙi. Wai a dinga zuwa gida ana dubata. Ko kuma ya kawota asibitin kullum. Rikitaccen mutum ne na lura mai ra'ayin riƙau gaskiya.”
Da ƙyar Hajiya ƙarama ta ƙaƙaro murmushi. Sai kuma ta miƙe tana faɗin, “Ai in dai Awwab ne ƙyaga da yawa wlhy. Shike nan bari zanje gidan mu haɗu ai.”
Murmushi itama Dr Larai tayi da faɗin, “To shike nan hakan ma yayi, amma ina tausayama matarsa dan zata sha fama. Stubborn namiji irin wannan idan baka karancesa ba wahalar zamane da su. Dan su abinda suke so kawai za'ayi tilas.”
Murmushi kawai Hajiya ƙarama tayi dan ita abinda ya dameta shi ya dameta. Cikin wayancewa dai tace bara taje taga petient sun taru. Miƙewa itama Dr Larai tayi tana tattara kayanta. “Okay nima ai wucewa zanyi. Nasan Alhaji bazai wuce ba sai na koma.”
💦🩸💦🩸💦
Tuni ganin Ummie yasa na manta da dokarsa ta kar na daɗe. Na shagala sosai da kwance mata gashinta bayan nayi sallar azhar, kanta na a saman cinyata ƙamshin turarensa ya cika ɗakin. Da farko ban maida hankali ba saboda nasan na saka wani a jikina. Sai da naji alamun mutum na nufoni sannan na farga. Shi ɗinne dai sanye cikin brown wando da ash ɗin riga mai gajeren hannu. Gashin nan a ɗaure ta can ƙasa sosai dan har yana taɓa bayansa. Saukar iska a cikin idanuna ya sani jan numfashi da ƙarfi na lumshe idanun, sai kuma duk kunya ta kamani irin wannan abin kunya haka na kure bawan ALLAH da ido. A zatona zaiyi maganar kallon sai naji baice komai ba. Sai ma hannunsa da ya ɗaura saman nawa dake tsefe kan Ummie. A hankali na ɗan ɗago na kallesa. Shima ni ɗin yake kallo. Ƙure juna mukai da ido ga hannayenmu akan Ummie.
“Kinga mamanki kin manta da umarni na ko?”.
Ya faɗa a hankali kamar mai raɗa. Fuska na ɗan marairaice masa da karyar da kaina gefe a shagwaɓe na ce, “Kanta ne fa ya tsufa”.
Idanunsa ya ɗan ja luuu kamar zai lumshe sai kuma ya buɗesu tar akan nawa. Bazan iya jurar salon kallon nasa ba a yanzu dan haka na janye nawa a hankali na duƙar da kan. Shima sai bai sake cewa komai ba ya ɗan janye hannun nawa ya ƙarasa tsefema Ummien. Dama ɗayan da nake yinne ya rage. Dan bana mata kitson da yawa. Koda ya kammala cumb dake saman cinyata ya ɗauka ya taje mata kamar yanda naima sauran. Sannan ya tattare gashin cikin hannunsa. Kallona yay a hankali ya furta, “Cire band ɗin kaina, idan kin dawo kwayi kitson”.
Kai kawai na jinjina masa. Kafin a kunyace na kai hannuna saman gashinsa dake kwance luff yana ƙyalli kona wata macen albarka na zame sililin baƙin band ɗin daya haɗe da gashin sai ma ka ƙura ido kake ganewa. Koda yaushe kuma zakaga da irinsa yake ɗaure gashinsa. Ina gama zarewa gashin nasa ya tarwatse a baya. Sai kawai na shagala da kallonsa har sai da naji saukar hannunsa cikin nawa zai zare band ɗin sannan na dawo hankalina. Duƙar da kaina nayi kunya duk ta isan. Yau dai na kula kamar ina sakin layi da yawa. Sai dai yanda ya basar yasa na ɗan ji nutsuwa. Yana gama ɗaure mata ya gyara mata kwanciya shima ya miƙe yana faɗin, “Lets go”.
Dole na mike a hankali ina gyara mayafin jikina. Wani kallo ya dinga bina da shi daga sama zuwa ƙasa. Sai kawai nai gaba da sauri. A falo muka samu mama Balki ashe bata fita ba. Tana ganinmu ta saki murmushi da faɗin, “Har kun fito.” a kunyace na jinjina mata kaina. Shi kuma ya sanar mata akwai baƙi a gidan zuwa anjima zai kira wayarta tazo su gaisa. Ya kuma roƙeta ta rufe ƙofar falon ko Paah ne yazo karta barsa ya shigo. Maganar tasa ta ɗan ban mamaki, har na kasa haƙuri sai da na kallesa. Amma sai ya ɗauke kansa kamar ma bashi ne yay maganar ba...
A falon ƙasa muka ci karo da su Azizat. Tunda muka fara sakkowa duk suka miƙe tsaye tamkar waɗan da ke cikin shock. Dan su duka bakunansu a buɗe suke kallonmu idan ka cire wata farar budurwa da ban sani ba a gidan dake zaune ita bata tashi ba. Sai dai itama ta zuba masa ido kamar zata cinyesa. Kallo ɗaya na musu na ɗauke kaina. Kamar yanda shima naga baima nuna yasan da zamansu ba ya wucewarsa. Ina jiyo Malika na yin ashar a hankali. Ban san miya basu mamakin ba. Ganina a gidan? Ko kuwa ganina tare da shi?. Oho dai can ta matse musu. Dan ni su duka ukun a yanzu na shirya duk wadda tace zata shigo sabgata wlhy sai na mata zanen yarabawa a fuska.
Koda muka iso ƙofar shiga sashen nasa sai da na tsaya na ɗan gyara mayafina sannan na bisa dan shi har ya riga ya shiga. Da Hayatu na fara cin karo tsaye a ƙofa yana waya, muna haɗa ido ya wani rissinar da kai. Harara na balla masa na wuce ciki abuna. Bana ganin fuskar waɗanda ke a zaune, sai dai haka kawai zuciyata ke wani irin sanyi da jikina. Gani nike kuma kamar na sansu. Tamkar wadda ƙwai ya fashema a ciki na ƙarasa sosai cikin tsakkiyar kujerun ina sake yin sallama ƙasa-ƙasa batare dana kallesu ba. Turus na tsaya zuciyata na bugawa da ƙarfi sakamakon jin muryoyin da ko'a cikin barci bazasu taɓa iya su ɓace min ba. Jikina har rawa yake na ɗago dan tabbatarwa. Sai kawai naci karo da fuskar Yaya Musaddiq da ke faman min murmushi da ta Hafizzullah. Yanzu kam sosai rawar jikina sake bayyana tayi, ga lips ɗina na rawa kamar yanda hannuna ke rawa ina son nunasu amma na kasa........✍️
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚_
*_BILYN-ABDULL ONLINE SHOPPING_* _Duniyar cancaɗa ado da kwalliyar birgewa. Kar ku bari ayi babu ku😘😘😘._
*_My account on TikTok_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram_*
I'm on Instagram as @balkissaibrahimmusa. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_WhatsApp_*
https://chat.whatsapp.com/LkRMFFQZakP55c7xK0QaMG
https://chat.whatsapp.com/D1Ki9jt2lNkKVetOWNuFN5
........
......Cikin rawar jiki na nufesu da wata irin sassarfa na faɗa jikin Yaya Musaddiq na saki wani irin kuka da ni kaina bamma san na minene ba, sai kuma na jawo hannun Hafizzullah shima na haɗasu na rungume. “Oh oh Kandala na ashe bata canja hali ba har yanzu jama'ar ALLAH”. Yaya Musaddiq ya faɗa cike da tsokana yana ɗagoni a jikinsu. Cikin dariya da sharar hawaye Hafizzullah ya ce, “ALLAH Yaya bata canja ba sai ma abinda ya ƙaru.” hannu nasa a kansa na dungure nima ina sharar hawayen na ce, “Magulmaci kana nan da hali”.
Dariya muka sanya mu duka ukun. Kafin na sake kamo hannayensu cikin nawa su dukan. Cikin shagwaɓa na sake fashe musu da kuka ina faɗin, “Ya akai kuka zo nan? Waye ya kawoku? Yaya wlhy nayi kewarku, kullum da dare sai nayi kukan rashinku. Yaya dan ALLAH kuce kun dawo nan zaku zauna tare dani?”.
Murmushi kawai yaya Musaddiq keyi, sai Hafizzullah ne cikin dariya ƙasa-ƙasa ya ce, “Sai dai idan zaki bimu mu koma Kano. Dan ni ban wani yarda kinyi kewarmu ba Addah. Jibeki kinyi wata fresh kamar ɗanyan nama sabon yanka. Ga ƙiba kin haɗa kamar ke kaɗai ake ma tirka a gidan. Kai gaskiya ba wani kewarmu ke dai gidan miji daɗi kinma manta da mu”.
“Yaya ka ganshi yana tsokalana ko?”. Na faɗa a shagwaɓe batare dama nasan mi nake ba. Dan wlhy duk jina nake a ruɗe kamar a cikin mafarkin dana saba. Dana farka zan nemesu na rasa ne. A hankali Yaya Musaddiq dake murmushi har yanzu yana kallona kawai ya kai hannu ya share min hawayen yana faɗin, “Manta da shi, har kin manta da halin auta ne ma. Bayan da yaji zanzo badashi ba ya zauna ya dinga rusa kuka harda birgima a tsakar gida wai shi idan baizo yaga Addarsa ba zai faɗa rijiyan gidan su Mama Sadiq maƙotanmu”.
Dariya na ƙyalƙyale da shi, tare da kai hannu kan fuskar Hafizzullah daya kwaɓe ta cike da shagwaɓa naja kumatun, sai kuma na dunguresa da faɗin, “Ashe dai yaron nan na sona har yanzu”...
Duk abin nan dake faruwa yana zaune a