Showing 135001 words to 138000 words out of 438336 words

Chapter 46 - Tsutsar Nama Book 1 Hausa Novel Complete

13 Dec 2024

2258

sai santsin Mable's ɗin ya dinga taimaka min har na kaisu balcony ɗin duka.
Ni kaina yanda falon ya dawo a hayyacinsa sai da nayi murmushi. Na baɗe ko ina da freshiners masu ƙamshin daɗi dana gani a wata drawer. Ac na kunna kaɗan dan falon ya sake samun nutsuwa. Ganin lokacin salla na neman ƙuremin na dawo falon farko nayi salla ganin akwai toilet a cikinsa shima. Duk da matuƙar gajiyar da nayi da buƙatar hutu da nake da shi haka na sake miƙewa na koma. Yanzu kam ina ƙara ƙarfin addu'a a bakina na tunkari ƙofofin ɗakunan nan biyu. Ta farko na murɗa amma sai na jita a kulle. Na koma kan ta biyu sai naji ta buɗe ita. Da sauri nayi baya saboda wani irin wari dake fitowa a cikinsa mai ban tashin hankali. Take zuciyata da cikina suka shiga yamutsawa, dole na fito a guje zuwa bayin dake a falon farko. Amai sosai na shiga yi kamar zan amayar da kayan cikina. Tun ina amaryar da ruwa dana sha kawai har na koma yunƙuri kawai babu komai, da ƙyar na samu nutsuwa na wanke bakina na fito ina hakki. Har na yanke shawarar fita na haƙura zuciyata ta zabureni akan muhimmancin aikin lada. Hawaye naji sun cika min ido dan zuciyata na ayyana min idan Umminmu ce a wannan halin kenan zanji ƙyanƙyamin kasa tsaftace mata wajen kwananta? Da sauri na shiga girgiza kaina tamkar mai magana da mutum. Bamma san lokacin dana zabura na koma ba. Sai dai ina zuwa ƙofar na zame vail ɗin kaina na nannaɗe fuskata gaba ɗaya har zuwa hancina sosai. Amma duk da haka ina ɗan jin warin kaɗan-kaɗan. Haka dai na dake ina karanto addu'a a bakina ga hawaye na ɓulɓulo min cikin idanu saboda tausayi da tashin hankali. Yanzu nan ɗan adam mai rai, mai gata ne a irin wannan ɗakin? Bily ban san yaya zan musalta miki ba. Amma duk yanda kike hasashe abin ya wuce nan, ƙazantace sosai a ɗakin mara daɗin misali. Amma haka na duƙa na fara tattarewa ina kuka. Dole naje na kwaso labulolin dana cire a falo da burin wankesu na dinga naɗe ƙazantar a ciki. Sai da na tattare komai tare da fito da katifar ɗakin da ƙyar dan itace kawai anan sai labuloli da wadrobe ta jikin bango. Ina jin mutanen gidan sun fara hayaniyar wari-wari, dan da gayya na kaita falon can na farko da zaka iya hanga ta dawn stairs. Juyawa nayi na koma ciki ina ayyana kowa yau dan ubansa sai ya shaƙa shima. Shine punishment ɗin ku. Sam ban kawo cewa tana a cikin ɗakin ba, dan ganin ban ganta ba a farko kuma har nayi kusan kashi ɗaya bisa ukun gyarashi yasa nai zaton tana ɗayan ɗakin ne ko can sama hawan ƙarshe. Toilet na nufa, cike da tsantseni na buɗesa. Bamma san na daka uban tsalle ba nayo baya cikin matuƙar razani jikina na karkarwa. Gurnani da nishin dake fitowa a toilet ɗin yasa hankalina ya sake tashi, a take hoton abinda na gani ya shiga dawo min da kansa. Mutum zaune sarƙa a ƙafa da hannayenta an saƙalo jikin fanfo. Gaba ɗaya hannunta da ƙafafun sunyi jina-jina alamar son ƙwace kanta ya kaita ga jin ciwon. Kanta a duƙe yake shiyyasa banga fuskarta ba, sai gashinta dake a wani irin cirkuɗe danƙare a kanta mahaukaciya dai cikakkiya. Tausayi da tashin hankali ya sakani durƙushewa a wajen ina kuka. Nafi minti uku sannan na miƙe na sake komawa toilet ɗin. Sosai idanuna sun gama rufewa, nama bar tunanin zata iya cutar dani kamar yanda Bahijja ta faɗa tana duka. A gabanta na zube zuciyata a dake na shiga kwance sarƙar ƙafafunta da suka kumbura suntum sukayi jina-jina. Har na kammala kwancewa bata ɗago ba, sai nishin nan dai mai ban tausayi da tashin hankali kamar wadda numfashi ke shirin barin gangar jikinta. Da ƙyar na iya kammala kwance sarƙar ƙafafun, na shiga shafa ƙafar hawaye na cigaba da zararo min. Wata irin ajiyar zuciya mai ƙarfin gaske ta sauke. Sai kuma ta ɗago a hankali. Wani irin bugawa da sauri-sauri zuciyata ta shiga yi saboda ganin yanda fuskarta tayi kaca-kaca da tabbunan raunuka, sai sabbin da har sun fara bushewa suma kusan uku. Gaba ɗaya baka iya shaida kamaninta saboda dauɗa data gama mamayeta. Dan kayan jikinta ma duk a yayyage suke fata-fata. Rawa jikina ya cigaba dayi, hawaye masu zafi na sake gudu a cikin idanuna. Bamma san lokacin da na kai hannuna saman fuskar tata ba ina shafawa. “Kiyi haƙuri Ummi, dan ALLAH kiyi haƙuri, ALLAH ya gaggauta saka miki, ALLAH ya baki lafiy.....” kuka ya sarƙeni na gagara ƙarasawa. Ƙara ta saki a hankali sai kuma ta shiga fisgar hannunta a galabaice. Zaram na miƙe cikin karkarwar jiki. “I'm sorry Ummu, I'm so sorry bari na cire miki. In sha ALLAHU koda fansar raina ne zan bada wajen taimakonki. Sai na ƙwato miki hakkinki, sai na san gaskiyar mafarin lalurarki. In har da saka hannun wani sai na tarwatsa masa tanadi”. Sambatu nake da kuka ina kwance mata hannayen suma. Suma dai sun kumbura sosai duk taji ciwo. Ga tabbuna nan da sayin sarƙar alamar ba yau ne aka fara ɗaureta hakan ba. Ina gama kwancewa ta saki ƙara mai ban tausayi da alama hannun ya mata nauyi, durƙushewa nayi a gabanta nai ƙoƙarin kamo hannuwan nata ra riƙe. Sosai kuka mai ƙarfi ya sake kuɓuce min harda shashsheka. Ɗago idanuna nayi ina kallonta, sai naga itama ni ta tsurama ido tana kallo kamar mai lafiya. Murmushi na saki mai haɗe da kuka. Sai kuma na buɗe baki da nufin bata haƙuri a bazata naji an damƙi wuyana. Sosai na waro ido waje dan azaba. Sai kuma na saki wahalalliyar ƙara jikina na rawa dan shaƙa ce bata wasa ba. Tamkar wulgawar walƙiya aka jehoni cikin ɗakin. Razanannen ihu na ƙwala na azabar buguwa da kaina yayi da bayana. Kafin na yunƙura na tashi domin ceton kaina har ta iso gareni, sake kai hannu tayi a wuyana ta shaƙoni......

💦💫💦💫💦

Sosai Musaddiq ke a cikin farin cikin da baki bazai iya musaltashi ba duk da bai samu tabbacin samuwar aikin ba. Sai dai yanda interview ta kasance ya matuƙar bashi ƙwarin gwiwa. Ga karramashi da akayi sosai a wajen har abin yaso bashi mamaki. Sai dai ganin harda wani da ya samu da nasa takardun shima ya cirema kansa shakku. An sallamesu akan kowa zaiga massage daga nan zuwa safiya.
Cike da ɗoki kuwa ya dawo gida, ga wani irin farin ciki daya gama mamaye masa rai, sai dai wani fanni na zuciyarsa na matuƙar jin kewar Kandalarsa, da yanzu ita zai fara sanarma albishir ɗin komai da bata labari. Amma ba komai ko yanzu ma bata ɓaci ba. Waya ya jawo ya shiga laluben layin mijin nata. Sai dai har ta tsinke ba'a ɗaga ba. Sake kira yay har sau uku nan ma shiru. Hankalinsa ya nema fara tashi sai ga shi an kirasa back da number ɗin. Cike da zumuɗi ya ɗaga. Suka gaida da mutunta juna. Mijin ya ɗora da bashi haƙuri akan ba'a kusa yake ba sanda yay kiran. Cikin mutuntawa Musaddiq yace babu komai. Sun ɗan yi shiru kowa da tunanin da yake yi, sai kuma suka yunƙuro kusan atare zasuyi magana. Dariya abin ya basu, dan haka Musaddiq ya dara, da ga can kuma mijin na Samraah ya murmusa har Musaddiq ɗin najin sautin murmushin nasa.
“Afuwan ina jinka”.
Da sauri Musaddiq ya ce, “Ni zan nema afuwa ai ina jinka”.
“Okay, dama zance ma bana gida ne, amma in sha ALLAHU dana koma zan haɗa ku. Sannan in babu damuwa tsoffin numbers nata ka ɗan turamin dan a mata welcome back ɗin su”.
Cikin jin daɗi Musaddiq yay masa godiya. Daga haka sukayi sallama. Dole ya haƙura yay kiran Hafizzullah dake makaranta yay masa albishir ɗin shi, murna suka dingayi, daga ƙarshe suka koma hirar Samraah ɗin dan da gaske kowa a cikinsu yayi kewarta sosai........✍️



_Humm, ni dai inada tambaya anan😂. Yayanmu Maash ne ko kuwa🥱🥱Bara dai bayi hiru to._


_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚 𝒇𝒐𝒖𝒓_


.......Zuwa yanzu labari ya gama shiga kunnen mutane da dama game da wannan aure na baƙo daga Kano da Halime. Ciki kuwa harda innarta da sauran matan gidansu kasancewar family house ne part-part. Dan har ƙannen mahaifinta da matansu duk a gidan suke suma. Koda su Abba suke isowa sun samu gida a matuƙar hargitse innarta nata tsiya da bori ana rirriƙeta. Abin nata zabban takaici. Dan suna shigowa ta dire tsalle ta shaƙe wuyan rigar Baba tana surutai da girgiza, ga zagi manya-manya. Da ƙyar ƙannensa da matansu suka ɓanbareta. ALLAH sarki Baba duk sai ya daburce. Fahimtar yanayin nasa yasa su Abba dakewa su. Tare da nuna masa cewar hakan ba komai bane daga halin banza irin na wasu mata kamar su Inna. Abba kuma ya sake ƙarfafawa Baba gwiwa akan in sha ALLAHU zai riƙe Halime da daraja ta yanda sai Inna ta yi kuka da idanunta. Baba yaji sanyi a ransa, hakan yasa yayma Abba alƙawarin nan da sati guda Halime zata tare kawai. Yanzu ɗin ma dan yana son sanarma dangin su Innar (dangin mahaifiyarta kenan) shiyyasa bazai basu ita ba. Sun gamsu da hakan, saboda suma suna buƙatar komawa su ɗan kimtsa. Gidan mai-anguwa suka koma aka kira musu Halime. Sai dai da ƙyar ta fito fiskarta a ƙunshe cikin Hijjab. Duk yanda Abba yaso ya ganta taƙi yarda ta buɗe fuskar. Aiko Alhaji Jafaru da Alhaji Sadisu nata ƙumshe dariya. Abba ko nata balla musu harara. Da ga ƙarshe ya korasu waje. Suna fita yay kan Halime yana lallashi, kamar almara yana kai hannu kan hijjab ɗin nata da nufin ɗagewa ta zungura da gudu cikin gida ta barsa da hannu a sage. Duk da yanda yaso dannewa ya gagara, tuni ya shiga ƙyalƙyala dariya yana mai jinjina wautar ta. Lallai akwai aiki gabansa tuƙuru kenan....

★•★•★•★

Duk yanda mama Balki taso samun nutsuwa ta gagara hakan. Sai faman kaiwa da komawa take yi hankalinta gaba ɗaya na akan Samraah. Tun tana irga sakanni har ta koma mintuna, amamakinta sai ga awa ta shuɗe. Awa ɗaya, biyu, uku itama ta shuɗe. Tsaye take akan kula da girkin rana dasu Kubrah keyi amma kaɗan-kaɗan sai ta fito daga kitchen ɗin, tun ma basu fahimtaba suma har suka fara tsarguwa. Cikin gulma suka dinga nunama junansu ita da ido da baki. Sam Mama Balki bata san ma sunayi ba, saboda hankalinta a rabe yake. Ƴar hayaniyar su Arwa dake falo da zagin da taji sunayi ya sata fitowa zumut daga kitchen ɗin. Hannu taga duk sun saka suna famar toshe hancina. Yayinda tuni Muhsin ya fara kakarin amai. Dai-dai nan itama mahaukacin warin ya daki hancinta, da sauri takai hannu ta toshe hanci, sai kuma ga jama'ar gidan suma sun fara fitowa daga sassansu kowa na tambayar warin minene haka?.
Rasa mai bama wani amsa akai sai nuni da sama saitin sashen Hajiya Babba kawai akeyi. A dai-dai nan katifar da Samraah ta jingina jikin ƙarfen da aka ƙawata adon wajen da shi da bata zauna dai-dai ba ta sulmiyo downstairs ɗin gaba ɗaya. Ihu yaran suka buga a tare suna tarwatsewa. Sai kuma yunƙurin amai dan gaba ɗaya falon ya ƙarasa gumamewa. Cike da fusata Hajiya Mammah ta koma upstairs ɗin tana ƙwala kiran Samraah da “K!! K!! K!!” dan ko sunanta bata sani na. Ihun nata yaja hankalin sauran iyayen dama su Azizat ɗin suma suka bita. Hakama su Falilah ba'a barsu a baya ba. Mama Balki ce ƙarshen bin bayansu.

Isowarsu ƙofar dai-dai da ƙwalla ƙarar azaba da Samraah tayi, a take kowa ya tsaya cak. Ƙarar da Samraah ta sake fasawa kuma duk sai suka ja da baya. Dan basa buƙatar ƙarin bayani ta ƙwaɓe ne tsakaninta da mai sashen. A matuƙar tashin hankali Mama Balki ta juya da gudu ta sauka downstairs ɗin jikinta na ɓari. Bama tasan sanda takai kanta sashen Maash ba. Kawai tsintar kanta tayi a gabansa durƙushe cikin kuka da roƙo ta kama ƙafafunsa....
“Alhaji ƙarami dan ALLAH ka taimake mu. Kandala. Kandala ce gata can a sashen Hajiya Babba...” numfashinta ya nema ɗaukewa gaba ɗaya saboda yanda take a kiɗime. Shiko Maash da tun shigowar tata a guje da tsawar da Hayatu yay mata na son ta dakata ya tsaya cak daga duba abinda Hayatun ke nuna masa a tab sai dai bai ɗago ba sai da ta ambaci Hajiya Babba dan shi bai ma san waye wani Kandala ba. Idan ka cire ita a gidan da mijinta sai wasu tsiraru a masu aikin da suka daɗe a tare da su kawai zai iya cewa ya sani har ma ya shaidasu koda a wajen gidan ya gansu. Amma daga basu ɗin ba babu wanda zai iya shaidawa a cikinsu.
Cak Hayatu shima ya dakata da ga yunƙurin maganar da yake, dan sai a lokacin yama fahimci wacece ɗin. Shine yay ƙarfin halin faɗin, “Mama waye Kandala? Mi kuma ya faru da Hajiya Babba?”.
So take tai magana amma ta kasa, sai nuna ƙofa kawai take ga hawaye na kwaranya mata. Ƙarasowa Hayatun yay da sauri inda take. Ya kama hannunta ya miƙar daga gaban Maash da take durƙushe. “Kinga relax. Calm down kiyi magana yanda za'a fahimta. Rufe idonki ki shaƙi iska ki fesar Mama”.
Kai mama Balki ta shiga jinjinawa tana haɗiyar kukan da sauri-sauri. Yanda duk Hayatun yace tayi tayi, ya miƙa mata ruwan gabansa ta sha maƙwarwa biyu sannan ta sauke nannauyan numfashi. Shi dai Maash kallonsu kawai yake amma ya gagara cewa komai. Cikin ƴar nutsuwar data samu ta sake faɗin, “Kan...kandala ce sabuwar mai aikin da Aunty Mama ta kawo. Ta..ta tafi sashen Hajiya Babba gata can tana ihu da alama....” sai kuma ta kasa ƙarasawa. Sosai Hayatu ya waro idanu a firgice. Yayinda Maash yayi wani masifar runtse nashi da ƙarfi, sai kuma ya ajiye tab ɗin hannun nasa ya miƙe. Baima tsaya ƙarasa jin zancen ba ya nufi ƙofar da kan sadashi da sashen mahaifiyar tasa kai tsaye daga sashensa. Sai dai kuma a kulle take. Jikinsa ya shiga shafawa neman key, amma da alama baya tare da shi, har ya kalla Hayatu zai yi magana sai kuma ya fasa. Komawa yay da baya ya fito, da sauri Hayatu da Mama Balki suka take masa baya. Ta babban falon gidan da ya gama gumamewa da warin katifar nan ya ratsa, da bibbiyu ya dinga haɗa stairs ɗin tsabar tashin hankalin da yake a ciki. Dan duk duniya bai haɗa al'amarin mahaifiyar tasa da komai ba. Cikin rufewar ido da ɗimuwa yake sa hannu ya ture duk wanda ya tare masa gaba. A haka har ya shige ciki gaba ɗaya dan su mutanen gidan suna a falon farko ne cirko-cirko sun gagara shiga ciki dan tsoro. Sai hayaniya da suka cika wajen da shi. Yana shiga securitys ɗin da sukai kira na cikin gidan na isowa. Suma takema Maash ɗin da Hayatu baya sukayi...

Sosai nake kakarin mutuwa. Idanuna kam sun gama firfitowa. A wannan gaɓar na sallama da rayuwa. Ta ALLAH kawai nake jira ta kasance. Wata irin bugawa da tama kaina a bango ya sani fasa wahalalliyar ƙara da ko sautin kirki babu yanzu saboda galabaita dana gama yi. Daga haka ban sake sanin mi kuma duniya ke'a ciki ba...

Shigowar Maash dai-dai da wancakalo Samraah da Hajiya Babba tayi kai kace irin an yadda magen nan. Baya yay taga-taga zai faɗi, sai da Hayatu ya riƙesa. Da sauri ya kai dubansa kan abinda ta wurgo ɗin, a kuma dai-dai nan itama ta sake wawuro abin morpping irin na wutar nan da Samraah ta ajiye tare da sauran kayan shara. Ji kake bummm!! Akan goshinsa. Kamar ƙyaftawar ido ta sake rarumo wani abun, jifan kan mai uwa da wabi ta shiga musu kamar yanda take yi a duk sanda take a irin wannan yanayin. Dole su Hayatu suka shiga fita a guje. Yayinda Maash ya kasa yin hakan shi. Dan shi damuwarsa ba ciwon data jimasan bane. Kar ita ta jima kanta ciwon. Ƙoƙarin nufarta yayi da son kwashe sauran kayan sharan. Amma ina jifa kawai take kai masa dasu tako ina...
Cikin wani irin karyewar murya ya shiga ƙoƙarin kai hannu gareta yana faɗin, “Please Ummie na kar kiji ciwo, dan ALLAH ki ajiye zai ji miki ciwo. Hannunki Ummie hannunki.”
Ina ita bama tasan yanayi ba. Jifan kawai take kai masa har sai da taga kayan sun ƙare, sai kuma ta koma kai masa duka da hannu. Cikin sa'a shima ta shaƙuro wuyarsa. Dai-dai nan masu kula da lafiyarta da akai kira a waya suka iso. Da ƙyar aka

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login