Showing 123001 words to 126000 words out of 438336 words
da asha ruwan tsuntsayen nan nawa na yanzu🙏_
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒔𝒆𝒗𝒆𝒏𝒕𝒆𝒆𝒏_
......Akan takalman ƙafarsa na fara sauke idanuna, yanda suke sheƙi da ɗaukar idon mai kallo ya isa tabbatar maka almubazzaracin da akai da kuɗi wajen sayensu. Coffee brown suit ne a jikinsa, sai rigar ciki milk color. Kamar kullum botiran farko a buɗe har ana iya hango jikinsa kaɗan. Luf-luff gashin kumatunsa ke kwance a saman fuskarsa tamkar masu barci, sai wani irin sheƙi suke suma. Hannunsa ɗaya a cikin aljihun wandonsa ɗayan riƙe da wayar dake manne a kunnensa yana wani motsa ƙananun pinkish lips ɗinsa a hankali kamar wanda akaima tilas. Kamar kullum kunnensa ɗaya manne da ɗan kunne, daga tacan saman kansa zane da kitso ƙwara biyu zane ata gefe da gefe, tsakkiya wiving kusan biyar, cikkune dan haka ɗaure yake a tsakkiya ƙarshen kitson kuma gashin a warware ba'a kitseba dan haka ya sakesa kawai a baya yana lilo. Wani irin takaici da haushi ya sakani kallon fuskarsa duk da nasan tabbas yayi ƙyau. Karaf kuwa idanuna a cikin nasa. Bamma san lokacin dana balla masa harara da murguɗa nawa bakin ba. A mamakina sai kawai naga ya lumshe nasa idanun tare da buɗesu a lokaci guda yana cije gefen lips ɗinsa ya ɗauke kansa. nima ɗauke nawan nayi kamar zan fasa kuka, ji nake tamkar naje gareshi yanzu na zazzage masa abinda ke a raina. Amma dai na dake, sai harara dana sake jefama jelar PA ɗinsa dana fahimci tunda idonsa ya sauka a kaina yay suman tsaye. Niko na ɗauke kaina tamkar ban san da zamansa a wajen ba. Tunda nasan dai duk abinda mugun ogansa ya ƙulla tare da shine makirin shima.
Addu'ar da aka fara gabatarwa ya saka kowa a wajen sake nutsuwa. Mu dai marasa gata duk muna a tsaye kan ƙafafunmu, yayinda suko ke zaune a kujerun da aka ƙawata wajen. Sosai yanda akai addu'ar wa kowa harda iyayenmu ya sake saka min nutsuwa har idanuna na tara ƙwalla. (ALLAH sarki rayuwa, da ace muma namu iyayen na raye babu yanda za'ai mu tsinta kammu a cikin wannan gararin rayuwar. Amma ko yanzu ma alhmdllh, koba komai mun rayu cikin aminci tunda gallazawar rayuwa batasa mun lalace ba). Kewar su Yaya Musaddiq ce ta sake taso min sabuwa har na zurfafa a tunani batare dana farga ba. Taɓanin da Bahijja tayi ne ya maidoni a hayyacina. A hankali na sauke ajiyar zuciya da nannauyan numfashi. Cikin raɗa-raɗa a saitin kunnena ta ce, “Aunty Kandala muje zamu fara bada drinks”. Kaina kawai na iya jinjina mata, dan gaba ɗaya babu wani ƙarfi a tattare da ni. Ta wajen babban table ɗin da aka shirya nau'ikan abinci dana lemuka da ruwa muka nufa. Bahijja ta zari handglob guda biyu ta miƙamin tare da mun nunin na saka. Itama ta zara ta saka a nata hannun sannan ta buɗe ƙatuwar kular da kayan ruwan ke ciki ta ɗiba lemunan da ruwa duk ta loda a babban tray data jawo guda biyu. Sai da ta gama zuba nata da nawa sannan ta ce, “Yauwa to muje. Kowa a gabansa zaki fara ajiye ruwa sannan ni kuma na ajiye lemon da suka buƙata”.
“Kamar ya?”.
Na tambaya cikin rashin fahimta. Ƴar dariya tayi. Kafin ta ce, “Na zuba miki ruwa ne dan kar su baki wahala. Shi ruwa zaka ajiye ne kawai. Amma lemo dole sai mutum ya zaɓa sannan”.
Kaina na jinjina mata alamar gamsuwa, sannan na kama tray ɗin na ɗaga ina ɗan taɓe baki. Ai da sauri na maida na ajiye ina waro idanu. Ai wlhy bazan iya ɗauka ba yamun nauyi. Ragewa na fara yi, hakan ya sata zaro idanu waje alamar nuna mamaki. “Lafiya kike ragewa?”.
“Yamun nauyi wlhy Bahijja bazan iya ɗauka ba”.
Sake waro idanu tayi, niko ban sake kulata ba na rage fin rabi sannan na ɗauka. Kallo take mun na tama rasa abin faɗa. Ni ko na sake ɗauke kaina gefe kamar ban ganta ba. Dole itama ta barni muka bar wajen tana gaba ina biye da ita. Suma sauran kowa ya fara aikinsa dan komai a tsare yake. Mun fara da table ɗin farko. Mai ɗauke da mutane huɗu kamar ko ina. Maza biyu masu tsananin kammani, a fisge kuma suna kama da mutumin can Maash. Sai dai kawai su baƙaƙe ne. Tabbas nasan mai irin fuskar nan amma na manta a ina. Sai mata guda biyu ƙyawawa suma, ɗaya fara tas ɗaya black beauty. Su duka sunci ado sosai mai tsananin ƙawa. Ganin kallon da suke min na rashin sani yasa naji kamar duk na daburce. Amma sai na dake kaina a ƙasa na shiga haishesu ƙirjina na bugawa da sauri-sauri. Mazan ne kawai suka amsa min, yayinda baƙar matar ta dubi Bahijja a gadarance ta furta, “Wannan fa?”.
Jikin Bahijja har ɓari yake. Cikin in-ina ta amsa da, “Au...aun..Aunty Mama ce tazo da ita randa ta iso”.
Su dukansu ɗan kafeni sukai da kallo, sai kuma duk suka janye cike da basarwa. Jiki a sanyaye na bar wajen, batare da ina kallon gabana ba saboda zancen zuci na iso table na gaba. Ganin nayi tsaye kawai Bahijja ta ɗan zungureni, firgigit na kawo numfashi, ɗagowar da zanyi na sauke idanuna a kansa. Zaunensa yake a harɗe fuskar nan kicin-kicin tamkar ba wanda ya tara jama'a ba. Gaba ɗaya hankalinsa na akan tab dake a hannunsa ne. Yanda yay serious a kanta zai baka tabbacin abinda yake yi mai muhimmanci ne. Ga uban ƙamshin turarensa da ya mamaye wajen gaba ɗaya. Fuska na yamutse tare da ɗauke kaina. Harara na ballama ɗan koren PA ɗinsa dake table ɗin bayansu. Ƙasa naga yayi da kansa yana murmushi. Jinai zuciyata ta ƙulu da murmushin nasa, amma sai na danne tare da cije lips ɗina kawai....
“Woow! fine girl ko ana mana rowan ruwan ne?”.
Ɗaya daga cikin waɗan da ke zaune a table ɗin tare da shi ya dawo dani a hayyacina. Ni sai ma yanzu na lura da sauran dake zaunen a tare da shi. Su duka su nasan fuskokinsu a wajen taron buɗe Companyn sa na Kano. Dan ALLAH ya bani baiwar da dawahala nai maka gani ko ɗaya ne na manta fuskarka koda ace ban riƙe suna ba ko a inda na sanka ba. A hankali na ɗan yamutse fuska ta. Batare da nace komai ba na fara ajiye musu ruwan. Uku na ajiye abina batare da nashi ba, dan kowa a gabansa na ajiye amma shi banda shi. Na ɗaga tray ɗin zan bar wajen wannan dai da yay maganar ya ɗan waro idanunsa yana nuna min shi. “Beauty baki ajiyema boss ba fa”. Yi nai tamkar ban jisa ba sai da Bahijja tasa hannu ta ɗauka ruwan ta ajiye masa jikinta har yana ɗan rawa. Harararta nayi batare dana san dalili ba. Itako ta waro idanunta na nuna mamakina. Tray ɗin na sake ɗagawa da nufin barin wajen ina dallamasa harara ta gefen ido dan tunda mukazo wajen ko sau ɗaya bai motsa ba balle kai tunanin yama san da zuwan namu, batare da nasan yanda akai ba, ta yaya kawai tray ɗin ya suɓuce min na tafi gaba ɗaya na. Idanu kawai na runtse tare da sallamawa, amma sai na jini zaune jikin mutum, yayinda shi kuma tray ɗin ya suɓuce a ƙasa sauran ruwan suka tarwatse. Wani irin zuƙa da nayima mayataccen ƙamshin turarensa ya saka gabana faɗuwa. Da sauri na buɗe idanuna dake a rufe. Sai kawai na waro su tare da yunƙurawa da sauri zan miƙe amma hakan ya gagara. Dan sake zamewa nayi na koma jikin nasa gaba ɗayana har ma fiye da farko.
“Sai kice son hawa kike ba sai kinyi pretending ba”.
Naji saukar muryarsa a cikin kunnena. A wani irin zafafe na sake yunƙurawa gaba ɗaya na na miƙe jikina har tsuma yake, sai da Bahijja data gama firgita ta riƙoni. Jinai bazan iya daurewa ba, idanuna na tara ƙwalla na watsa masa harara, sai dai ina motsa lips ɗin na nufin juye masa abinda ke raina naji na gagara hakan. Sakamakon wani shegen kallo daya tsatstsareni da shi tare motsa lips ɗinsa a hankali, “Kina cewa tak sai kowa yasan ke MATAR MAASH ce”.
Da masifar ƙarfi na cije lips ɗina hawaye na sake ciko min idanu. Badan na samu horo akan aikina game da salon da yay maganar ba da bazan fahimta ba. Amma gamu ƴan jarida yaren magana da ido ma an karantar da mu balle na motsa lips. Da wani irin salon rainin hankali ya kai yatsarsa manunuya saman goshinsa tamkar zai gyara silin gashi yay salute tare da sakin wani matsiyacin murmushi gefen baki ya kanne ido ɗaya.
“Sai na tarwatsa rayuwarka”.
Na faɗa nima a saman lips ɗin ina haɗiye hawayen da suka ciko min idanu. Sanin zasu iya zubowa na kai durƙushe nima ina taya Bahijja tsinci ruwan daya tarwatse. Sai faman haɗiyar zuciya kawai nakeyi dan ni kaɗai nasan abinda nake ji a cikinta, nu mutumin nan zai cema ina son hawa masa jiki ne dama. Ƙasa-ƙasa Bahijja ta furta, “Aunty Kandala kice masa yayi haƙur....” ruff ta rufe bakinta tare da haɗiye sauran abinda ke bakin nata saboda hararar dana balla mata. A fusace na miƙe tare da sunkutar tray ɗin nabar wajen. Mama Balki ce tai min nuni da nazo inda take. Dole na nufi inda muka ɗebo ruwan. Amsar tray ɗin tayi tana faɗin, “Badai kiji ciwo ba ko ɗiyata? Alhamdullah ma Alhaji ƙarami na kusa ya taimaka miki da kinyi muguwar faɗuwa ai. Sai naci ƙaniyar Bahijja kuwa, tunda bance harda ke za'ayi aikin nan ba amma ta jaki”.
Sosai naji raina ya ƙara zafafa. Wato su abinda suka fahimta kenan nazo zan faɗi ya taimakeni, alhalin ina zargin taɗeni akayi da ƙafa, tunda karo naci da abu a bazata, kuma babu wani dutsi ko ƙarfe balle ace shine. Ko rantsu nayi ba'a bina bashin kaffara mutumin nan shine silar faruwar komai, dan shine ya taɗeni da ƙafarsa........✍️
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒆𝒊𝒈𝒉𝒕𝒆𝒆𝒏
_*_Assalamu alaikum. Gaisuwa a gareku da fatan alkairi bayin ALLAH. Dan ALLAH kuyi haƙuri! kuyi haƙuri! kuyi haƙuri!!. Ba haka naso al'amarin ya kasance ba. Sai dai kana naka ne ALLAH na nashi. Nashi kuma shine gaskiya. Saboda ku na tsara kwanaki biyar, amma suka koma kwana tara. Amma in sha ALLAHU gamu mun dawo filin daga. Zakumin haƙuri na dinga baku ko 2pages ne dan na samu na rage nawa aikin nima daga nan ko zuwa kwana uku ne. Ngd Ngd sosai da haƙurinku gareni da uzirin da kukayi min. Wanda suka kirani kuma, kuma nagode, wanda sukai ma amarya da mai rasuwa addu'a a group duk na gode ALLAH ya bada ladan zuminci😘😘🙏._
........“Kinga maza jeki ki zauna dan baƙya cikin wannan aikin”. Mama Balki ta katse min tunani. Kaina kawoi na iya ɗaga mata da faɗin, “Nagode” a taƙaice na wuce ina haɗiyar zuciya. Inda muke tsaye da da Bahijja na koma na tsaya, sai dai duk bayan sakan sai na harari inda yake. Haka dai taron ya cigaba da gudana. An ƙara gabatar da addu'a musamman akan wadda aka tara taron da fatan ALLAH ya bata lafiya, na fahimci ba kowa yasan ainahin ciwon da take tare da shi ba, dan ina jin wasu mata biyu na gulma ƙasa-ƙasa game da hakan. Wai shekara da shekaru anata ciwo-ciwo amma anƙi sanarma duniya wane kalar ciwo ne. Sosai suka bani mamaki, a raina nace duniya kenan, mutum na jikinka amma baya maka so dan ALLAH.
Natsuwar fara addu'ar na samu damar fara bin kowa dake a wajen da kallo daki-daki. A hankali Bahijja da duk hankalinta ke a kaina dan tuni sun kammala raba lemon da ruwa sun dawo inda muke ta furta, “Aunty Kandala kinga waɗanda ke a table ɗin kusa da nasu Uncle Boss ta hannun dama da muka fara bama ruwa da drinks mai milk shadda shine mahaifinsa. *_El-mu'azz Mashi_ kenan. Sosai na tsurama wanda ta faɗa ɗin ido ta gefe dan ɗazun ban iya musu wani kallon kirki ba. Eh tabbas da gani babu tambaya, dan ya ɗebo wasu a cikin kamanninsa. Kamar tsaho, dogon hanci da makamantansu. Sai dai shi baƙine sannan alamun girma ya bayyana kaɗan a tare da shi. Musamman akan gashinsa akwai furfuta tsilli-tsilli. Haka kawai nake sake jin tabbas nasan fuskar, sai dai a ina? Na manta sam dan na kasa tunawa. Cikin katse min tunani Bahijja ta cigaba da faɗin, “Sai matar dake kusa da shi. Hajiya ƙarama kenan. Itace matarsa ta biyu kuma amaryarsa. Itace mahaifiyar Arwa. Ance ta taɓa haihuwa da shi sau ɗaya tagwaye duk maza a shekarar farkon aurensu amma duk sun rasu, ba kuma ta sake ba. Arwa dai da ita tazo. Matar bata da damuwa sosai, sai dai akwai miskilanci da mulki tamkar itace ma uwar Maash ɗin. Sai dai abubuwa nata da yawa na matuƙar birgeni, duk da dai wasu na bani haushi musamman yanda Hajiya Mammah ke takata yanda take so amma bata iya cewa komai ko nuna ikon ta na matsayin matar gida, wani lokacin ma sai ka ɗauka itace matar gidan ba Hajiya ƙarama ɗin ba”.
Sosai na tsurama matar idanu itama. Ƙyaƙyƙyawar mace kam ga suffar kamala black beauty da ita. Amma da gani kasan miskilar ce dan sam babu fara'a a fuskarta kamar dai ɗazun da tai tambayar ni wacece a daƙile.
Bahijja ta cigaba da faɗin, “Na kusa da shi kuma Alhaji Abdullahi Mashi, ƙani wajen Alhaji El-Mu'azz kenan. Uwa ɗaya uba ɗaya. Ta kusa da shi Hajiya Mubeena matarsa uwar ƴaƴansa uku. Itama dai tana da ƙarancin damuwa, sai dai ta hannun damar Hajiya Mammah ce dan ƙiri-ƙiri take nuna banbanci tsakaninta da Ummi ɗin (Hajiya ƙarama) na taɓa jin su Aunty Falila suna gulma wai ai dama ƙawarta ce acan ƙasar Niger da tayi aure, kin san mahaifin su Azizat buzu ne, shiyyasa kike ganinsu da shegen gadarar nan da masifa duk da dai shima wannan family ɗin masifa kamar a jininsu take, fitinannun mutane ne na bugawa a jarida, Uncle Boss ne kawai nake gani ma shiru-shiru a cikinsa ko magana da wahala kaji yana yinta, in ma yayi ɗin ba lallai kaji sautin muryarsa ba, sai ko Aunty Mama itama tana da sauƙi sosai, idan kinga tana faɗa an ɓata bata rai ne matuƙa. Daga table ɗin gefensu akwai Azizat ita kam kin haddaceta” tai maganar da shaƙiyanci, sai kuma ta cigaba da faɗin, “Sai Mabrukah autar Hajiya Mubeena, sai....”
Da sauri tayi shiru saboda yafito ta da Azizat ɗin tayi, jikinta har rawa yake ta nufeta. Wani takaici ne naji ya ƙwaƙume min zuciya. Bamma san na saki sirrin tsaki ba da taɓe bakina na ɗauke kaina daga sashensu ma gaba ɗaya. A bazata suka sauka akan Hajiya data ɗakkoni daga Abuja. A mamakina sai naga ta sakar min murmushi harda kashe ido ɗaya. Ɗan tsira mata idanu nayi cikin nazartar yanayin nata dan haka kawai komai daya faru a tsakaninmu tun daga Abuja ya shiga dawo min. Yanda take wani bina da kallon ƙurilla ya sani balla mata harara na bar wajen gaba ɗaya dan muna facing juna. Dai-dai nan mc yay kiran sunan uban taro cike da girmamawa. A tunani na Alhaji El-Mu'azz ɗin ne zai tashi, amma sai naga makirin nan ne ya miƙe cike da ƙasaita bayan ya gama shan ƙamshi da busar iska da fesarwa. Taku yake tamkar mai tafiya a kan gilashi, dan sai ka ɗauka ma bazai ƙarasa inda mc ɗin yake ba dan jiji da kai. Mic ɗin ya amsa, sai kuma yay ɗan shiru kamar wanda ya rasa abin faɗa. Baki na taɓe tare da watsa masa harara sai idona a cikin nashi. Da sauri na ɗauke ina mai murguɗa bakina kawai....
“Hummm!!” ya faɗa cikin mic ɗin ta yanda kowa dake a wajen sai da ya ji sa. Amma a mamakin kowa ya sake ɗinke fuska kamar bashi ne yace hummm ɗin ba. Sai ma cigaba da maganarsa da yay cikin harshen turanci mai haɗe da faransanci, yau dai ALLAH ya taimake mu ba'ai Hausa ba balle a ɓaga mana