Showing 321001 words to 324000 words out of 429394 words

Chapter 108 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

999

tsakanin kaida matarka na rasa wayafi wani cin kai. Dan Allah Malam kaje ka hado mata abubuwan da zata buqata tunda naga shirin zuwa dubiya kukayo sannan ka taho da wadda zata zauba da ita idan kuma kana buqata muna da Nurses da zasuyi maka aikin se kaje a baka Bill ka biya, ina da abinda zanyi idan shikenan maganar ka zaka iya tafiya" ya nuna masa qofa. A sabule ya fita koda yake hakan ma wani achievement ne ze sake ninka qoqari ta wata hanyar dan tabbatar da komai ya tafi kamar yanda yake fata.

Yana tare da ita har akayi Azahar kafin yace mata zeje yayi sallah daga nan ze biya ya gayawa Mama se ya koma gida ya debo mata kayayyakin amfani. Umaimah daketa mitar ita bata ga dalilin da za'a kwantar da ita tun safe ba, ina laifin ace su dawo da dare? Ita ya bari su tafi tare ta hado kayanta da kanta kawai dan be zama lallai ya dakko mata abubuwan da take buqata ba shidai Khalil ya lallabata ya tafi.

Ko minti goma beyi da barin Asibitin ba itama ta fita ba tareda ma ta bari Nurse din dake kula da ita ta sani ba bare ta hanata. Adaidaita ta tara ta tafi gidan, a hanya sukayi waya da Safina take gaya mata gobe za'ayi mata CS din yanzu ta gudo gida se dare zata koma idan ta hada kayanta. Da akwai wasu kayan Baby data siya gurin maqociyar Safinan bata karba ba ta roqeta ta kawo mata su gida yanzu dan akwai wanda zatayi amfani dasu sannan sukayi sallama.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* =?L?
Page 71


Tun daga compound take mamakin kwalayen data gani wanda take da tabbacin na kayan gado ne saboda gashi nan a rubuce seta tabe baki irin ina ruwanta din nan saboda tunanin daya zo mata Hajiya ake sakewa gado, ita fa can su gane yanda suka dena sakata a sabgar su ba bazata saka kanta ba, tasan dai duk wannan shirin baze wuce na auran Khalifa ba daman yaron ba mutunchi ne dashi ba shiyasa tun da ma ake zancen auran nasa bata taba saka baki ba kuma dalilin daya sa taqi fita taga lefen kenan sanann sisinta bazata bayar ba da sunan gudummawa tunda dai ba'a sakota a ciki ba
(A lissafin Umaimah kenan lefe na Khalifa ne saboda ta san da zancen yayi budurwa abinda bata sani ba babu wata kwakwkwarar magana ma tsakaninsu balle har aje ga batun kai lefe)

Kanta tsaye ta wuce cikin gida sedai mutanen data gani zaune a falonta sunyi daidai suna cin abinci yasa ta tsaya turus ta kasa gaba da kasa baya tana kallonsu kamar yanda suma suka zubo mata ido suna kallonta.
Cikin daga murya ta shiga kiran Ruqayya, ta fito daga kitchen da sauri jikinta na rawa dan tun zuwan Matan da batun da sukazo dashi daman ta firgice. A gaban Umaimah ta tsaya kanta a qasa tace
"Gani Hajiya"

Cikeda bala'i tace "Su waye wadannan da kika barsu suka shigo mun falo kamar nasu saboda tsabar rashin mutunchi ji yanda suka zubar mun da abinci akan carpet?"
Kafin Ruqayya ta bata amsa wata qatuwa daga cikinsu tace
"Aa karki ga laifinta mune mukayi kuskure mun dauka falon na masu gidan ne gaba daya ashe naki ne ke kadai da bamu zauna ba to Allah huci zuciyarki mu kam mun gama abinda ya kawo mu ma wucewa zamuyi".

Kallonta Umaimah tayi na wani lokaci tana qoqarin ta tuna a ina ta san fuskarta amma ta kasa
"Kinga Sumayya mun ma gama bari mu tattare mata gurin mu Alkhairin ne ya kawo mu ba tashin hankali ba" daya daga cikin masu cin abincin ta fada tana miqewa ragowar suka shiga tsince wanda ya zube a qasan, Umaimah data gama tunano inda ta san wadda aka kira da Sumayya qanwar Mansur ce to uban me ya kawo su gidan kuma koma mene duk fadin gurin Hajiyar be ishe su ha se an kawo mata mutane falo kuma ba'a gaya mata ba lallai mutanen nan sun raina mata wayo.
Gani tayi Sumayyan ta juya ta haye sama abunta yanda kasan dakinta ya saka Umaimah dakatar da ita da sauri tana cewa

"Ke ina zaki, kinyi hauka ne da zaki haye mun sama se kace gidanki?"
"Nan fa daya, falo dai da kikace naki ne mun bar miki amma baki da ikon hanamu hawa Sama tunda ba mallakinki ne ke kadai ba, da dakin yar uwarmu a gun kinga kuwa babu wnada ya isa ya bamu dokar sanda zamu shiga ko ya hanamu" Sumayya ta fada kafin ta juya taci gaba da hawa saman. Wata mulmulalliyar Ashar Umaimah ta kora kafin cikin Azama tabi bayanta. Rabon data hau saman harta manta amma yanzu saboda bala'i nacin ranta tsaf ta haye har suna bangazar juna da Sumayyan kai bakace da wani kaya a jikinta ba.

Qofar part din Khalil data gani a bude kuma nan Sumayyan ta shiga babu bata lokaci ta mara mata baya, sosai ta bude ido tana kallon Falon da aka qawata yayi kyau harya gaji da haduwa, daga kan Kujeru Zuwa labulale kayan kallo da sauran kayan kwalliyar falo babu abinda ba'a saka ba masu kyau da tsari. Wasu Samari biyu suka fito daga dakin da yake matsayin Master bedroom suka kalli Sumayya suna gaya mata sun gama. Daman suna shiga da Umaiman kitchen ta wuce abinta ta dakko kaskon da suka kunna garwashi dan haka tayi musu sannu tace su sauka qasa su karbi Abinci gasu nan fitowa yanzu zasu wuce.

Showglass din turaren wuta ta bude ta debi wanda zata zuba nan da nan qamshi ya fara tashi a gurin, bata ko nuna alamar tasan da tsayuwarta ba ta shige dakin da Samarin suka fito se Umaimah ta bita kamar Jani Talo, Sumayya ta ajiye Kasko ta wuce tana gyara zaman labule kafin ta kashe fitilar dakin ta dakko kaskonta ganin Umaimah tsaye a bakin qofa kamar wadda ta samu mantuwar tunani yasa cikin gatsali tace mata
"Malama ki fita zan kulle tunda nan ba dakinki bane"

"Ke da izinin ubanwa kuka shigo mun gida sannan wadannan kayan na wanene?" Umaimah data rasa tunanin da zatayi ta fada se Sumayya ta watsa mata wani banzan kallo kafin tace
"Da izinin uban wanda ya isa, kaya kuma ki tambayi Mijinki ze fiyi miki bayani kalar wanda qaramar qwaqwalwarki zata dauka ni da Allah Malama ki fita na kulle muna da abinda zamuyi inke baki dashi" ta janyo qofar garam ta rufe har tana buge Umaimah ba tayi wata wata ba kuwa ta finciko Sumayyan duk qibarta da yake a bazata abin yaje mata se gata wanwar a qasa Kaskon hannunta ya fadi qasa ya fashe wuta ta zube a qasan. Da sauri ta matsa tana dafe qugunta daya bugu, wata Qanwar Maman Humaira da ta bi bayansu saboda tsoron abinda ka iya faruwa tayi saurin kama Sumayya ta miqe tana mata sannu.

"Kan uban nan ni kika kayar wallahi sena nuna miki na fiki hauka a gidan nan" Sumayyan ta fada tana qoqarin fincike hannunta Umaimah ta kalleta cikin ido tace
"Tun kafin raina ya gama baci ku tattara tsiyarku ku fitar da ita daga gurin nan"
"Saboda gidan ki ne ko yaya? Ke ki qaddara ma gidanko ne tunda Mijinta yace nan ze ajiyeta baki isa ki hana ba kuma kaya sun shigo kenan kamar yanda me su take tafe gobe da yardar Allah gara ma ki Adana haukarki qila tayi miki amfani a gaba" Sumayya ta mayar mata se Umaimah ta sake zabura tayi kanta tana cewa
"Zan nuna miki hauka kuwa ganin idonki karku kwashe ku jira na dawo duk se kun gane kurenku" fuuuu ta fice daga falon ta sauka qasa, bangaren Hajiya ta nufa a fusace so takeyi taje taji da izin wa za'a ajiye wata a gidanta bama zata kira Khalil ba dan tasu daban seya gane kurensa wlh.

Hajiya na zaune da wasu Aminanta da suka zo mata Allah sanya Alkhairi ana ta maida zancen yanda abu ya faru Umaimah ta diro musu kamar Kirsimeti ta cake a tsakiyar falon tana haki qirjin Hajiya ya buga dum kafin kace me zufa ta fara keto mata a ranta fadi take ta faru ta qare wai anyiwa me dami daya sata.
"Hajiya bana buqatar sanin koma su waye wadancan kwanciyar hanka kowa na gidan nan su fitar mun daga gida da duk tsiyar da suka shiga da ita idanba haka ba na rantse da Allah se rankowa ya baci a gidan nan, saboda tsabar neman bala'i me ya hana ke ki sauko daga naki saman ki bashi ya saka matar seni ana mun hassada na sakata na wala a cikin gidana za'a kawo faccala a ajiye mun to wlh qaryane kuma har gaban abada na ci gida gara ma ku cire idonku daga kai".

Yanda kasan sakarkaru haka qawayen hajiya suka bude baki da hanci suna kallonta, Hajiya Uwani guda daga ciki tayi qarfin halin cewa
"Amma dai ke wannan yarinya duk inda kika fito ba yar arziqi bace ke, uwar data Haifi Mijinki kika iya tsayawa a gabanta kina gaya mata kausasan kalamai haka saboda baki da tarbiyya? Koda yake ma sakarya ce ke baki san abinda kike fada ba naga alamar Kishi ya taba miki kwakwalwa har baki gane abinda kikeyi to ki fita daga nan tun kafin na harzuqa nayi miki dukan tsiya a nan mara kunyar banza da wofi".

Tun kafin ta idar Umaimah taja uban Tsaki tana kallonta tace
"Idan ban kasa da mutum ba karya dauka" kafin ta sake kallon Hajiya da gaba daya ta muzanta tace
"Hajiya ki tashi ki fitar dasu tun kafin nayi abinda kowa ze zo yana nadama a cikin gidan nan"
"Kinga Umaimah ki nutsu, ni Babana ba yace kina Asibiti an kwantar dake ba?" Hajiya ta fada tana nufarta se Umaimah taja da baya tana cewa
"Saboda yasan munafuncin da kuka shirya ai shiyasa ya daukeni ya kaini Asibiti zanyi maganinku gaba daya yanzu" ta juya sukayi karo da Lubna wayar dake hannun Lubnan ta fadi qasa Umaimah ta bita da kallo saboda ganin wani hoto akai kamar na Khalil akan wayar Lubna ta tsugunna ta dauka har tayi gaba kuma ganin Umaiman ta tsaya ta dawo baya tana murmushi tace

"Aa ya na ganki haka baki shirya ba ko ke ba zakije ki taya Habibin naki murna ba bayan shi gashi can saboda zumudi ya kasa zama seda yabi Amarya gurin kwalliya, kalle su ki gani dan Allah basu dace ba" Lubnan ta qarasa tana nuna mata screen din wayarta. Video Khalil ne yake tafiya rungume da wannan yarinyar ta gidan su Mansur, dukda kwalliyar data sha irin ta Amare bata kasa ganeta ba saboda irin tsanar da tayi mata a zuciyarta, Khalil din ya riqeta a jikinsa yana dariya ita kuma tana boye fuskarta a jikinsa alamar Kunya bata san sanda ta fizge wayar daga hannun Lubna ba ta dawo da video daya qare farko, yanda ta kwale ido tana kallon wayar ka rantse kwalli tayi da Attaruhu take neman iska ta shiga ta fifita mata.

Ta maida video baya bayan ya qare yafi sau nawa duk a qoqarinta nason ganin abinda take ya canza daga Khalil dinta zuwa wani mutum amma hakan ta gagara, ta ko ina Video ya tabbatar da cewar Khalil ne dan video daukar kusa ne tar fuskokinsu suka fito kamar ma magana sukeyi cire sautin akayi ga kayan da suke jikinsa dasu ya barta a Asibiti yanzu wayasa da Key din mota dake riqe a hannunsa duk ta shaidasu se kuma meya rage da zata tabbatar da cewar Khalil ne?

"Kawo na nuna miki sauran naga kina ta maidashi baya" taji muryar Lubna a tsakiyar kanta, cikin Azama ta dago a abinda be wuci second daya ba ta rotsa wayar da qasa kafin ta saukewa Lubna kyakykyawan tukuicin Mari taci kwalarta cikin wata murya tace
"Idan kina so ki tsira da ranki da lafiyarki ki bani amsa kawai, Ina Khalil kuma wacece wannan dana gansu tare?"

Lubna kuwa Mari da shaqar da tayi mata a lokaci data sun shigeta, lokaci daya ta firgice da ganin yana yin Umaiman ba tareda bata lokaci ba kuwa ta bude baki dakyar saboda shaqar data sha tace
"Yana gurin Kwalliya yaje dauko Amaryarsa daga can ze kaita gurin da zasuyi Yinin biki"
"Amaryarsa? Yinin biki?" Ta shiga maimaitawa a fili abinda yasa ta sassauta riqon da tayiwa Lubna kenan har Qawayen Hajiya da suka kawo mata dauki suka samu nasarar karbarta daga hannun Umaimah nan ta durqushe kuwa ta shiga tari dan ta dandana mata qamshin mutuwa, matsa tayi mata bata wasa ba hakan ya tuna mata da dukan data taba lakada mata shekarun baya randa suka fara zuwa gidan da Yayart???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?a.

A sannu kuma cikin nutsuwa Umaimah taja qafafunta ta qarasa inda Hajiya take zaune kamar dutse tun shigowar Umaiman ta dauke wuta, ta bude baki yafi sau goma amma ta gagara furta abinda take so ta fada saboda yanda kalmar tayi mata nauyi a qirji, a hankali ta lumshe idonta ta hadiye wani abu kafin ta budr ta sake kallon Hajiyar cikin wani irin sauti tace
"Hajiya nasan kina jina mu me Lubna take nufi da maganarta?"

Dagowa Hajiya tayi a sanyaye ta kalleta tace
"Umaimah kiyi haquri ki koma Asibitin kinji"
"Hajiya tambayarki nayi kawai ki bani amsa babu ruwanki da dukma inda zani daga nan nidai kawai buqatata ki qara mun bayani akan abinda kunnuwana sukaji" ta sake fada tana dagawa Hajiyar hannu se daya daga cikin Qawayen Hajiyar ta yunqura da niyyar Magana Hajiya tayi saurin dakatar da ita tana miqewa tsaye ta nufi Umaimah tace
"Muje ciki nayi miki bayani toh"

"Babu inda zanje daga nan gurin harse kin gaya mun abinda nake son naji" Umaiman ta fada cikin daga murya tamkar me yi da yar cikinta daidai nan aka sake bude qofar falon Jalilah da Jamila suka shigo cikin shiga ta alfarma sunyi anko na Lace haka fuskokinsu sunsha make-up.
"Meye haka? Ke wace fitsarar kikeyiwa mutane da ake jiyo muryarki tundaga tsakar gida?" Jalila ta fada tana kallon Umaimah swta juya a fusace ta kalleta tace
"Bada ke nake ba da uwar data haifeki nake dan haka ki sararamun" ta sake jutawa kan Hajiya da jikinta ya dauki rawar tsoro saboda hango kamar Iskokan Rashin mutunchin Umaiman zasu tashi da tayi cikin rawar baki tun kafin ta sake yi mata magana tace
"Kinga Umaimah kiyiwa Allah mu shiga ciki bari na kira Khalil din duk inda yake yazo yanzu se kiji komai a bakinsa ma"

"Wai Hajiya menene haka saboda Allah wannan mara mutunchin yarinyar kike bawa haquri me aka mata ba dole ma ta sake rainaki ta ringa miki duk cin kashin data ga dama ba, dallah Malama zo ki fita daga nan bakiji kashedin da nayi miki ba kenan akan Hajiya to wlh ko kishiga hankalinki ko yanzu jikinki ya gaya miki" Jalila ta fada a fusace

"Idan baki dakeni ba Aisha da Usman shegenki sukayi Jalilah, ni zaku rainawa hankali ni zaku yaudara? Ashe daman abinda Mama da yan uwana suka fada mun gaskiya ne ni zaku yiwa rufa rufa a cikin gidan nan ku cuceni ku daurawa Mijina aure da wata ba tare da na sani ba?" Umaimah ta fada cikin wani sauti jikinta ya dauki rawa take idanunta suka rine zuwa Jaaa kamar jini ya kwanta, da hannu ta shiga nunasu tana jan nufashi maganar ma ta gagara fitowa daga bakinta se ta juya kawai ta fice daga falon Jamila tabi bayanta Ita kanta Jalilah da take a hasale nan take jikinta yayi sanyi saboda ganin yanayin Umaiman Hajiya kuwa hannu ta dora a kai tana kiran
"Shikenan kun gani ko Jalilah kinga abinda nake gudu Allah gamu gareka ka karemu daga sharrin zuciyar wannan yarinyar".

"Hajiya Aisha Allahya sanya Alkhairi ya kuma rufa asiri nidai bari naje" Hajiya Uwani ta dauki jakarta ta maqala gaba daya sauran suka mara mata baya sunayiwa Hajiya sallama ganin wannan tashin hankali dake shirin ballewa a gidan kowacce ta fita da tambayar daman Uwargidan Khalil din bata san yayi aure ba kenan?

Umaimah kuwa tana fita a compound din daya raba bangaren nasu taci burki tabi motar yan jere da kallo Sammani ya bude Musu Get suka fice. Gurin da Sammani yake zama ta kalla, wata ajiyar zuciya ta sauke saboda hango zungureriyar Kokarar da yake ajiyewa a kusa saboda barayi, bata kulashi ba da yake tambayar me take buqata ta zari qaton sandan tayi cikin gida, Jalilah data biyota taja da baya a zatonta ita zata lodawa Umaimah kuwa ko kallonta batayi ba ta shige falonta kai tsaye ta haye sama ta murda qofar falon Amarya cikin Sa'a ta jishi a bude ta tuta qofar ta shiga, bata tsaya bata lokaci ba ta shiga dukan duk abinda hannunta ya kai kansa.

Sedata rugurguza mata kayan kallo tas da su Centre table, Showglass, frames, flower vase da duk wani abu da ze iya fashewa kafib ta wuce da niyyar shiga bedroom din nan qofar a kulle bata haqura ba ta ringa dukan handle din qofar a qoqarinta nason ta lalata shi ta samu ta bude qofar daidai nan Su Jalilah suka hawo saman gaba daya saka saka salati ganin irin barnar da tayi cikin Tashin hankali Hajiya take cewa
"Haba Umaimah ba se kinyi haka ba kiyi haquri a warware komai cikin nutsuwa wallahi muma ba'a son ranmu ba Allah ne ya qaddara faruwar hakan amma..."

"Kiyi mun shiru tsohuwar munafuka har kina da bakin cemun wani abu bayan duk abunda kika shirya yanzu zakice mun ba'a son ranku ba a son ran kutumar ubanki ne kenan kika aura masa yar qawarki sannan kice mun ba'a son ranki ba to idan kin cika ki qaraso nan ki gani na rantse da Allah sena rotsa miki kai ki mutu kowa ya huta na rage mugub irin Azzalumai macuta"

"Ke Umaimah baki da hankali ne Hajiyar kike gayawa haka?" Jalilah ta harzuqo zata qarasa inda take Hajiya ta riqeta tana girgiza mata kai tace
"Aa Jalilah karkije ba a hayyacinta take ba maza ki kira Khalil, Jamila dakko wayata ki

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login