Showing 252001 words to 255000 words out of 429394 words

Chapter 85 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

948

kuje kawai, ni kallon kwallo ma zamu tafi yanzu" Habibun ya bashi amsa yana shirin juyawa. Hannu ya saka a Aljihu ya zaro kudin da besan adadinsu ba ya miqawa habibu daidai nan ta iso gurin taja ta tsaya kanta a qasa kamar me qirga duwatsun gurin.

"Se an ce ki shiga motar ko? To ki kwana a tsaye. A haka zakije kinawa mutane wanan salo salon wallahi Yah Khalil inta bara maka lokaci ka barota a can kawai kayi tafiyarka" Habibu ya fada yana harararta ita dai bata tanka masa ba ta kama murfin gidanbaya zata bude ya sake katseta da cewa
"Wato ga Driver kin samu, kefa yarinyar nan kin samu guri da yawa wallahi"

"Nifa na dauka da kai za'aje" ta fada kamar zatayi kuka, Khalil dake zaune ya kalli Habibu yace
"Ka rabu da ita haka mana, shiga mu tafi".
Gaban motar Habibu ya bude mata saboda cin zali harda ranqwashinta.

Tafiyar kurame sukayi, ita dai ta riqe Takaddunta a hannu ta sunkuyar da kai ga uban Ac daya qure da qamshin turarensa sun dameta. A bangaren Khalil kuwa yanda kasan an bame masa baki da kwado haka yaji duk tarin tambayoyin da warning din daya shirya kora mata akan ta qyale kurwarsa ta huta ji yayi sun shafe se ma wata nutsuwa da yaji ta daukar masa sanadiyyar zamanta a kusa dashi. Lokaci lokaci yake waiwayawa ya kalleta har suka Isa wani babban Cafe yayi parking motar kafin ya fita Humaira ta bishi a baya tamkar kazar da kwai ya fashewa a ciki dan ita wannan hade fuskar tasa tsoro yake bata.

Basu bata lokaci a gurin ba akayi mata duk abinda ya dace dan suna shiga ya hadata da ma'aikatan gurin ya koma gefe ya tsaya har aka gama kafin suka gaya masa kudin ya biya. Wanda yayi mata aikin ya kawo masa takaddar da aka fitar mata ya karba yana gaya masa ranar da zata dawo dan ta san rana da lokacin da zata rubuta Jarabawar. Seda suka ci rabin hanyar komawa gida kafin ya kalleta yace
"Wane course kika cike?"

Daga kai tayi ta kalle shi ganin shima itan yake kallo yasa tayi saurin sada kanta qasa tana juya zoben hannunta muryar ta na dan rawa tace
"Fine art"
"Fine art" ya maimaita be qara ce mata komai ba yaci gaba da tuqinsa har suka kusa shiga layinsu kafin sake kallonta yace
"Ina wayarki?"
"Banida waya" ta bashi amsa. Se ya kalli hannunta itama hannun ta kalla kafin yayi magana tace
"Wayar Mama ce ni Yah Mansur yace ba yanzu za'a siya mun waya ba".

"Da layinta kikayi rijistar kenan" ya fada ba tareda ya kalleta ba seta daga masa kai kafin da sauri ganin baya kallonta tace
"Eh, shiyasa ta bani wayar ai".

Gani tayi ya dauke hanya daga komawa gida yayi wani gurin daban, ko motsi batayi ba har suka isa qofar wani shago ya kashe motar yaceata yana zuwa. Be dade a ciki ba ya fito da Leda fara qarama ya shiga motar suka juya zuwa gida. Suna isa ana kiran Sallar Magriba dan haka be shiga ba ya miqa mata Ledar daya fito da ita daga shagon dazu tareda kudi dubu goma yace ta kaiwa Mama. Ko saurar godiyar data tsaya yi masa beyi ba ya juya kan motarsa. A kan hanya ya samu masallaci yayi sallah, se a sannan ya duba wayarsa da tunda ya fito daga Office be sake dubata ba. Tarin Missed calls ya gani s sannan ya tuna da ya sakata A Silent da zeyi sallar Azahar kuma ya manta be cire ba.

Kiran Umaimah ya fara bi, tambayarsa tayi yaushe ze dawo gida dan ta fita amma tana hanyar dawowa. Sabon salon data tsiro dashi kenan se ta fita inda zata sannan zata sanar masa kuma yasan baze wuce gidan wannan qawar tata da sam yaqi Jini ba shi ya rasa ma tsakanin ita da Rufaida wacce yafi tsana a cikinsu. Gaba daya matar kalar munafukai ne da ita ga Ladabi da kana gani kasan bana Allah da Annabi bane, ya rigata komawa gidan, ta shigo da tarkacen kayan Jarirai ta baje masa su wai a gidan Safina ta siyo maqociyarta ce ta kawo shine ta diba.

Har ya kwanta saqo ya shigo wayarsa dake hannunsa. Baquwar number ce. Bude saqon yayi ya karanta abinda yake ciki
"Nagode kwarai Yaya Khalil, Allah ya saka da Alkhairi ya qara arziqi. Mama tace ayi maka godiya Allah ya raya su Mu'ayyad".
Ya maimaita karanta saqon yafi sau Goma kafin ya gane daga inda yake.
Inda ta samu number sa yake mamaki koda yake baze wuce a wayar Maman ba. Maida wayar yayi ya ajiye kamar wanda aka tsikara kuma ya janyota ya sake bude saqon. Number da ta turo yayi saving da 'Fine Art' kafinya goge text din dai dai nan Umaimah ta shigo cikin shirin kwanciya. Yana jinta tana mitar qafarta na ciwo kafin ta koma kan maganar kudin kayan data dauko. Be ko tanka taba yaja bargo ya rufe jikinsa alamar bacci zeyi. Tun bayan da sauka dawo shiri take neman yanda zata samu kudi a hannunsa shi kama ya tsuke bakin Aljihunsa tsaf ya qudurce a ransa kudi indai ba akan abinda ya zama dole ba ya dena bata. A da da yake bata dinma bega abinda ta tsinana dasu ba balle yanzu da shida kunnensa yaji tana shirya yanda zata samun kudin da besab abinda zatayi dasu ba.

Da safe yana zaune kan Dining yana jiran Umaimah da take soya masa kwai ta gama dan Ruqayya bata nan, anyi mata rasuwa ta tafi garinsu kwana uku kenan. WhatsApp ya shiga, abinda be fiya dubawa ba Status haka nan yau yaji sha'awar dubawar yana shiga kuwa da status din 'Fine Art' ya fara cin karo. Waqoqin hausa ne na soyayya ta dora a jere guda uku, se hoton wani da aka rufe fuskarsa da Emojin Zuciya ta rubuta 'Haskena' a qasan hoton. Haka kawai yaji ya qware da ruwan Tea daya kurba ya shiga tari har seda Umaimah dake kitchen ta fito ta bashi ruwa tana masa sannu. Seda tarin ya lafa masa kafin ya miqr tsaye idonsa yayi jajir saboda kwarewar da yayi ya sabi jakarsa dake kan kujerar kusa dashi Umaimah ta kalleshi da mamaki tana cewa
"Naga ka miqe, ina kuma zakaje baka karya ba?"
"Ki barshi kawai na qoshi, da akwai kudi na ajiye miki akan Dressing Mirror na zuwa Asibitin" ya bata amsa kafin ma ta sake magana ya kusa kaiwa qofa se kawai ta bishi da Adawo lafiya a ranta tana mamakin abinda ya harzuqashi haka dan fuskarsa da Muryar sa sun nuna fushin da zuciyarsa take ciki.

Khalil kuwa seda ya fita daga layinsu kafin ya samu guri ya tsayar da mota. Wayarsa ya dakko ya sake komawa WhatsApp din ya bude status dinta. Hoton ya tsurawa ido kamar wanda yake son goge Emoji din ya samu damar ganin fuskar wanda aka boye din har wani huci yakeyi saboda yanda zuciyarsa take tafasa kai kace Umaimah ce ta dora hoton wani Namiji bashi ba ta kirashi da haskenta. Kiran wayar Anwar ne ya katse masa kallon status din, suna gama magana ya tada motar yaci gaba da tafiya ita kanta motar tasan yau ran me ita a bace yake saboda yanda yake fizgarta kamar ze tashi sama.

Sama sama ya ringa amsawa masu gaishe shi, a office dinsa ya tarar da Anwar dake jiransa zasu fita ya jefar da jakarsa kan kujera Anwar ya bishi da kallo ganin yanda yake abubuwa kamar wanda yake fada da kayan office din.
"Khalil lafiya kuwa?" Anwar ya tambayeshi ganin yayi wurgi da Chajar wayarsa da yake qoqarin jonawa amma taqi hawa alhalin ba laifinta bane shine be kunna socket din ba yake ta danna chaji.

Tsaki yayi ya zauna akan kujera ba tareda ya amsa shi ba. Anwar yaja daya daga cikin kujerun gaban Table din shima ya zauna yana fuskantar sa, yasan matsalar sa daya ce bazata wuce Umaimah ba amma ya zata sunyi magana tun kwanaki kuma Khalil din da bakinsa yace baze sake bari lamarinta ya dameshi ba ballantana har ya shafi aikinsa yanzu kuma me tayi masa haka da ya zuciya yake qoqarin yiwa abubuwa rotse.

Gyaran murya Anwar yayi yana kallon Khalil da shi kuma yake kallon wayarsa, status din yake sake kallo dan ta qara wasu hotunan guda biyu, daya dai Hasken nata ne se na qarshe ita da Mama da Nusaiba matar Mansur a Harami da alama Umarar da Mama take da Mauludi tare suka tafi kenan.
"Khalil" ya kira sunansa, se ya dago daga kallon wayar ya dubi Anwar,
"Meya faru?"

Tsaki Khalil yayi kamar bazece komai ba se kuma cikin qufula yace
"Wata yarinya na siyawa waya saboda ta raina mun hankali yanzu kawai naga ta saka hoton wani gaja da caption wai Haskenta" ya fada muryarsa na nuna zallar takaicin da status din Humairan ya qunsa masa shi dai Anwar kasa riqe kansa yayi seda ya fashe da dariya harda kyakyatawa yana kwanciya akan Table dan maganar ba qaramin shiharsa tayi ba. Yanzu wannan fushin duk akan mace yakeyinsa lallai Khalil yayi nisa sedai fatan Allah ya taro shi.

Kallonsa Khalil ya ringayi har yayi dariyarsa ya gaji takaici kamar ya shaqoshi ganin irin kallon da yake binsa dashi ya saka Anwar dakatawa da dariyar yana cewa
"Allah ya baka haquri, maganar taka ce ai dole ta sakani dariya. Wai ka siyawa yarinya waya ta dora hoton wani a Status, kai dole ma na kai labarin nan NH yau gayu suji su dauki darasi" ya sake sheqewa da wata dariyar da tafi ta da abin haushi.

Tashi Khalil yayi ya shiga hada abubuwan da zasu fita dasu din ransa a bala'in bace kamar ya rufe Anwar da duka.
"To amma tsaya, Ina Umaimah da har aka siyawa wata waya kuma kake fushi dan ta saka wani a status? Kai bama wannan ba da alama mayyar data kama ka ta sakar maka kurwa kenan har ka iya yin budurwa ka siya mata waya lallai Khalil ka shahara wuyanka ya riqa ko ince Alqadarin Umaimah ya karye tunda gashi ka dena tsoronta kai tsaye kake abinka yanzu" Anwar daya tsaida dariyarsa dakyar ya sake fada. Shidai Khalil be kulashi ba ya gama tattara abinda yake da buqata ya fita Anwar dinya rufa masa baya. A mota ma haka ya tasashi da magana shidai yayi masa shiru dan abinda ke cin ransa ya ishe shi haka suka gama zagayen duba ayyukan da zasuyi ransa a dagule babu dadi.

A wani restaurant suka tsaya cin Abinci bayan sunyi Sallar Azahar. Anwar ya sake kallonsa ganin gaba daya ranar bashida walwala gashi bini bini ya dauki waya ya duba ya riga Khalil din cinye abincinsa dan haka ya jirashi ya gama, ganin sauran da suke tare basu qarasa ba ya saka shi amfani da damar ya kalli Khalil yace
"Mutumina kasan abu na farko da zan fara ce maka shine duk abinda zaka yi a rayuwa kayishi tsaka tsaki. Idan zaka so abu ka so shi daidai Misali haka idan zaka qi abu ka qishi saisa saisa saboda wata rana duka abu biyun nan suna iya rikida su koma akasin Asalinsu.

Kaga kai babbar Matsalar ka a rayuwa ita ce zurfafa Soyayya. A duk sanda kaso abu kana daukarsa ka bashi muhimmanci sama da kowa da komai a rayuwarka bana buqatar tunatar da kai Matarka kadai ta isheka isha idan haka ne zamantakewarku kadai ta isheka karatu akan duk wata mace da zaka sake mu'amalanta anan gaba. Duk abinda ya faru dakai Soyayyar ka tayi amfani da ita ta yaqe ka, nayi zaton ka koyi darasi se gashi yanzun ma kana qoqarin sake afkawa a ramin da yafi wanda ka baro Zurfi da duhu.

Ni nasan Wannan Mayyar da ka ringa iqirarin ta kamaka babu wata mayya se Maitar Soyayya, ka sake fadawa tarkon Love at first site din daka saba ne shine kazo kana mana wata Drama wai Wata Mayya ta kamaka ashe ban sani bama har abu yayi nisa kun daidaita harta kai ga ka siya mata waya. To nidai abunda zan iya gaya maka daya ne zuqa biyu, yanzu dai gashi da Idonka ka gani cewar ba kai kadai take kulawa ba kamar ma shi wancan yafika fawa a gurinta tunda da wayar daka siya akeyin status dashi ana kiransa da Haske kai ko Arziqin duhu baka samu ba. Ita Mace daka ganta a sanda kake nacinta kana nuna mata So da kulawa ba takai take ba,se kaga zuciyarta tana ga wanda be kaika ba, sedai ka qare a wahalta mata ita kuma tana Wahalta masa tunda shi take so".

Yanda kasan me daukar karatu haka yasa kunnuwa yana sauraron Anwar, fashin baqin da yayi masa yasa ya shiga tunanin kenan da gaske Son yarinyar yakeyi? Saurin qaryata hakan zuciyarsa tayi se kuma daya bangaren ya jefo masa tambayar
"Idan ba sonta kakeyi ba ina ruwanka da sabgarta har kake kishin ta saka hoton wani a status?"
"Tab da kuwa an fadi babu nauyi ace ina son wannan yar yarinyar da bata wuce na haifi Sa'arta ba" ya fada. Be ankara da cewar a fili yayi maganar ba seda yaji Anwar yace

"Ai babu wani aibu idan kaso qaramar yarinya abu daya ne dai A yanzu idan aure zakayi Khalil kamata yayi ka nemo matar da take sonka ba wacce kai kafi so ba, bani da buqatar gaya maka dalilin haka dan ka fini sani. Bance karka so koma wacece ka samo ba amma ka zauna kayiwa kanka Hisabi shin ta dace dakai? Zata share maka hawayen da kake fata ko kuwa? Idan ta gaza cin wadannan Test din ka haqura da ita ka nemi wata cikin manyan yammata da suka gogu da rayuwa kuma su suke sonka ba wai kai kake sonsu ba na tabbata se sunfi binka sun baka nutsuwar da kake nema sannan ka sani duk macen da zaka aura a yanzu dole ya zaman cewar tayiwa matarka zarra ta kowanne fanni shi kadai ne ze samar maka da zaman lafiya a cikin gidanka dan ka fini sanin da wadda kake zaune, amma idan da ita wannan din zuciyarka ta aminta, ka nemi zabin Allah ka bar masa komai a hannunsa duk kuma hukuncin daya yanke maka kar kayi Jayayya da hakan ka karbeshi da kyakykyawan Yaqini".

"Bafa tasan ina sonta ba, ni dakaina ban yarda cewa Sonta nakeyi ba. Haka kawai tun daga randa na fara ganinta na rasa nutsuwata. Yarinya cefa Qarama Anwar, she is just 18 me zan tsinta a jikinta kawai Shaidan ne yake nema yayi mun wasa da hankali amma ni ba wani abu game da ita a raina" Khalil ya fadawa Anwar din iyakar gaskiyarsa. Murmushi Anwar yayi yace
"Lokacin daka fara Son Badar haka kace soyayyar yan uwantaka ce, se gaka harda kwanciya a gadon Asibiti da tace ba zata aureka ba. Umaimah kuma Friendship ita kuma wannan Tausayinta kake ji halan tunda kace yarinya ce?"

"Exactly, tausayinta naji. I learnt that she is an orphan babu uwa babu uba, shine ma har yasa na siya mata wayan saboda tace bata dashi. Cousin din Mansur ce, a gidansu take. amma ni ba wani sonta nakeyi ba kawai haushin da naji akan me daga na siya mata waya zata ringa saka hoton wani saurayi bayan ni purposely saboda tayi karatu na siya mata" Khalil ya sake fada, se Anwar ya miqe yana murmushi yace
"Abokina ka nemi zabin Allah kawai kaji idan kaji ta kwanta maka daga nan ka nemi yardarta ka dage kuma da Addu'a Allah yasa qarshen wahalarka ne yazo".

Har ya koma gida maganganun Anwar nayi masa yawo a kai, sam baya so ya yarda da cewar wai Son Humaira yakeyi to ta Yaya ma? Amma kuma duk wasu Shika shikan soyayya sun gama bayyana a tare dashi. Wannan faduwar gaban da yawan tunaninta da yakeyi harya dora mata Maita ashe duk na kamuwa da Soyayya ne be sani ba amma kuwa idan haka ne So be kyauta masa ba daya rasa inda ze sauka se akan wannan yar tatsitsiyar yarinyar da Yasan kwakwkwarar tsawa idan Umaimah tayi mata zata iya suma. Kai bama wannan ba ya tabbatar babu yanda za'ayi Mansur ya yarda ya barshi ya aureta dan yace matarsa bata da hankali dukda shine babban zagin da kullum yake Addu'ar Allah yasa ayi mata kishiya to dai dara taci gida Addu'a ta karbu kuma akan Qanwarsa sedai fatan Allah ya taqiata dan idan har ze qara aure dagaske to babu wata Mace da ze aura idan ba Humairan ba, ita kadaice tayi masa irin shigar da Umaimah tayiwa zuciyarsa.

Raba dare yayi yana kallon Umaimah dake baccinta hankali kwance saboda duniyar tana gara mata yanda take so, ta samu kan Mijinta bata da wata damuwa. Tunanin irin yanda zasu kwasota kawai yakeyi idan har maganar nan ta tabbata amma a wannan karon baya jin zeji bari, ko shi ko Umaimah.

HUMAIRAH




*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* =?L?
Page 59

HUMAIRAH

Bayan da Khalil ya sauketa tana shiga gida ta ajiye ledar daya bata da saqon Mama ta faa bandaki saboda fitsarin daya matseta tunda suka fita take jinsa. Habibu ta tarar ya bude ledar data ajiye ya zaro kwalin Waya Iphone bata dai san ko wacce ce ba dan ita ba sanin waya tayi ba.
"Ke waya siya miki IPhone?" Ya fada ganin ta fito daga bandakin, Mama dake juya kwalin ta kalle ta tace
"Humaira wadannan fa daga ina haka?"

"Yaya Khalil ne ya bani, mun taho a hanya ya tambayeni inada waya nace masa Aa ta hannuna takice shine ya tsaya a wani shago ya siyo wannan ga kudi nan kuma yace na kawo miki ya wuce yana sauri" ta bawa Maman Amsa cikin nutsuwa, kafin ma Mama tayi magana Habibu ya amshe yana cewa
"Kan bala'i kuma shine ze siya miki IPhone? Lallai Yah Khalil qaiqayi kudi suke masa besan ko Keypad baki gama sanin yanda ake dannata ba ballantana wata IPhone ai kawai ni ya siya wallahi, alfarma daya zan miki na jefeki da Infinix dita ki qarasata" ya

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login