Showing 408001 words to 411000 words out of 429394 words

Chapter 137 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

1055

baya cikin qaramin lokaci oho, a haka ta fara fita aiki wanda hakan ba qaramin taimakonta yayi ba dan a dan lokaci Walwalarta ta fara dawowa, yanayin aikin da mutanen da take mu'amala dasu suka taimaka mata matuqa gurin fuskantar gaba ta dena tuna bayanta.

Qarfe tara take fita ta taso hudu dan haka zatayi Breakfast, an cire mata shara da wanke wanke se kuna girkin dare idan ta dawo wata rana ma yin abinsu sukeyi basa jiranta musamman Anty takance ta gaji taje ta huta kawai tayi abinta. Albashin da ake bata ya matuqar taimaka mata, bata da matsalar suturu dan yanzu datake fita nema take saka kaya dan haka ta dinka dogayen Hijabai har qasa kaloli masu kyau dasu take zuwa aiki yanda ta kame kanta bata shiga sabgar komai da bata aiki haka magana ma ba kasafai takeyinta ba se abinda ya zama dole hakan yasa kowa a gurin yake mutuntata.

Da sallama ta shiga office din Hajiya Huda zata kai mata wasu takaddu data buqata, Cike da tsananin mamaki take kallon matar data kira sunanta tana zaune akankujera tana zabga mata murmushi. Umaiman ta gyara tsayuwarta tana sake kallon matar. A jikinta tana jin tabbas ta santa a wani guri amma ta kasa tuna ina ne. Hadiza ta qara fadada murmushinta tana cewa
"Baki gane ni ba ko Umaimah? Hadiza ce, shekarun da yawa kin ganni na zama qatuwa duk wanda ya dade be ganni ba se yayi da gaske yake ganeni"

Qirjin Umaimah ya buga da qarfin gaske da jin sunan matar, Numfashinta ya tsaya na wani lokaci har bata san sanda ta saki takaddun hannunta ba kafin ta shiga jansa da qarfi jin sunan Hadizan kadai ya haifar mata da wani yanayi tareda shigar da ita rudani na gaske, lura da hakan ya saka Hadiza miqewa ta kama hannunta tana cewa
"Lafiya dai ya naga kamar bakiyi murna da gani na ba?"

Idon Umaimah yayi rau hawaye suka shiga sakko mata, so take ta bude baki amma ta kasa cewa komai se kawai ta fashe da kuka, Hadiza ta sake kallon Umaiman cikin yanayin nuna rashin jin dadi tace
"Kiyi haquri, ban dauka ganina ze bata miki rai ba, tunda na shigo na ganki kafin nayi miki magana kika shiga wani office na bari se zan fita se mu gaisase kuma gaki anan amma kiyi haquri, da nasan bazakiji dadi ba da ban miki magana ba" ta sake hannun Umaimah tana yunqurin tashi se Umaiman ta damqe hannunta lokaci daya ta durqushe a gaban Hadizan cikin tsananin kuka tace
"Dan girman Allah ki yafe mun, nayi nadamar abinda na aikata miki a kullum cikin Addu" a nake Allah ya hadani dake ya bani ikon neman yafiyarki gashi yau ya amsa mun Addu'ata ki yafe mun" ta qarasa tana riqe qafar Hadizan dake qoqarin dagota amma ta kafe taqi tashi.

"Dan Allah ki tashi kar wani ya ganki haka, Anty Huda kiyi mata magana ni zumunchi kawai nazo muyi ba tayar miki da hankali ba ki tashi koma wace magana ce se muyi a zaune dan Allah" Hadizan ta sake fada, dakyar ta samu Umaima ta zauna a kan kujera har sannan hannunta riqe dana Hadiza tana kuka kamar me ta sake cewa
"Haqqinki ne yake bibiyata, na rasa aurena, uwa uba na rasa mutunchina Khalil din da nayi hauka akansa na rasashi ina Ji ina gani ya zama mallakin wata bani ba. Dan Allah ki yafemun Hadiza ko zan samu sauqin rayuwar da nake ciki".

Jikin Hadiza yayi sanyi da jin maganar Umaiman, sun rabu da Khalil kenan take nufi meya faru?"
"Ki yafe mun Hadiza" Umaiman ta sake fada cikin tsananin kuka. Hajiya Huda da tayi shiru tana kallon Dramar tasu ta sauke numfashi tace
"Ya isa Umaimah ki dena kukan haka, Hadiza meya hadaki da ita haka da take kuka tana neman gafararki?"
Se Umaimah ta sunkuyar da kai ba tareda ta dena kukan ba wata irin kunya da nauyi sukayi mata rubdugu. Idan Hajiya Huda taji labarinta tabbas duk wani girma da mutuntawa da ake mata a ma'aikatar ya qare daga yau zasu ringa mata kallon mara mutunchi da bata tsoron Allah amma hakan ya fiye mata idanhar Hadiza zata yafe mata a shirye take data sake yin Video ta roqi yafiyarta kamar na wancan karon.

Hadiza kuwa murmushi tayi tana kallon Yar uwar Mijin nata tace
"Babu komai Anty Huda, can an dade mun taba samun sabani da ita amma ya wuce a gurina kuma tun a lokacin mantawa tayi amma na fada mata na yafe har gaban Allah babu komai a raina" seta koma kan Umaimah tana cewa
"Wallahi na dade da yafe muku Umaimah tun a wancan lokacin banida wani abu dana riqe akanki amma naji kince kin rasa Khalil, kardai Rasuwa yayi ban sani ba?"

"Khalil be rasu ba Hadiza amma bama tare kusan shekara shida kenan ya sakeni" Umaimah ta bata amsa tana sunkuyar da kai qasa se office din yayi shiru na wani lokaci kafin Hadiza ta sauke numfashi tace
"Allah yasa hakan shine mafi Alkhairi a rayuwarku gaba daya".
Umaimah dake kuka har sannan ta daga kai ta kalleta tace
"Harda haqqinki da yake bibiyata ki yafe mun dan Allah"

"Umaimah, na gaya miki nifa ban riqeki da komai ba amma dai tunda so kike na sake fada kiji na Yafe miki Umaimah na yafe miki abinda kikayi mun Allah ya yafe mana gaba daya".

Ajiyar zuciya me qarfi ta sauke tana jin nauyin zuciyarta na raguwa. Hajiya Huda ta miqe da kanta ta dakko ruwa me sanyi ta miqa mata a sanyaye tana cewa
"Kisha seki shiga ki wanke fuskarki tunda tace ta yafe kukan ya isa haka".
Ta karbi ruwan tasha kamar yanda tace ta shiga bandakin dake cikin office din, Hajiya Huda ta kalli Hadiza data sunkuyar dakai, maganar rabuwar Umaimah da Khalil din ta tabata seta dafa kafadarta tana cewa
"Madallah da kyakykyawar zuciya irin taki Hadiza, Ubangiji yana son masu yafiya Allah ya yafe miki kurakurenki kema kamar yanda kika saka sharri da Alkhairi, ubangiji yaci gaba da dabaibayeki da Ahalinki da Albarka mara yankewa, dan uwana yayi sa'ar mata"

Hadiza tayi murmushi daidai nan Umaimah ta fito ta wanke fuskar amma har sannan bata dena hawayeba tana jan majina, Hajiya Huda ta nuna mata kujera tana cewa
"Zauna a nan har se kin dena kukan zaki fita, ba zaki ja a fara tuhumar me akayi miki ba ina tace ta yafe to kukan ai ya isa haka ko" kamar tace ta qara kuwa ta sake fashewa da wani kukan. Auna qirman laifin da tayiwa Hadizan takeyi a zuciyarta wai duk ina tunaninta yake tafiya a baya idan zata aikata mugun Abu? Khausar da Rufaida sun cuceta, su sukayi mata ingiza me kantu akan Hadizan, wannan be zamar mata darasi ba ta sake janyo Safina rayuwarta gashi yanzu ta tarwatsa komai ya lalace ta rasa komai da take taqama dashi. A ranar se Hajiya Hudace ta maidata gida dakanta saboda irin kukan data ringayi harya haifar mata da ciwon kai me tsanani. Seda ta kwana biyu tana jinya kafin ta koma aiki ta kuma yi maruqar qoqari gurin danne duk wata damuwa ta cigaba da walwalarta.

KHALIL

*HALIN KISHI*

*NA MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*

*FIKRA WRITERS ASSOCIATON*
*(DON CIGABAN ADABIN HAUSA)*

Page 87

BAYAN SHEKARA DAYA

A hankali kamar wadda akayiwa kiran yan zawarawa suka fara kawo mata caffa. Idan ta fita bata dawowa gida ba tareda wani ya taya ba saboda yanzun Alhamdulillahi ta murmure, jikinta ya fara dawowa dukda bata maida cikarta irin tada ba amma tayi kyau fatarta ta goge musamman da yanzu take daukar Albashi tana kula da kanta ta siyi mayuka masu kyau dan har Supplement Maman Asad ta sakata dole ta siya masu gyara fata bana qarin wata halitta ta jiki ba ya kuwa karbeta ya bude mata ciki ta ringa cin abinci sosai kuma me gina jiki nan da nan se gata ta dawo hayyacinta tayi tas shiyasa duk idan ta gifta Mazan basa iya dauke kai akanta amma a bangarenta ta shata musu layi, babu Wanda ta bawa dama duk irin yanda Yan uwanta suke mata magana akan bafa zata zauna haka ba, gara ta sako ranta ta bawa wani dama su daidaita dan mutunchin Mace gidan auranta.

Anty Hafsa ma da take zaune tayi aure tuni, daman ita tace saboda Yaranta Mata take zaune duk manemanta idan ta kawo musu zancen da yaranta zata zauna se su zame ita kuma tace ba zata barsu hannun dangin Mahaifinsu ba dan basu nuna musu zumunchi ba, tunda ya rasu aka rana gado suka karbi rabonsu kowa ya zame ya barta da wahalar Yayan nata hudu da suke duk Mata. Tashi daya Allah ya aurar mata da uku, babbar ta gama Jami'a, me binta tana level 3 se ta ukun ta shiga kenan duk suka samu Miji Mama tace babu abinda za'a jira haka aka hada da Sharifan Anty da itama ta gama makarantar tuntuni se sannan ta samu Mijin aka sha biki. Auran yaran da wata uku ita ma ta daura nata da wani tsohon Abokin Baban yaran shima matarsa ta mutu shikenan ta tare da sauran yarta data rage ta hada da nasa ta riqe masa.

Auran Anty Hafsa yasa suka taso Umaiman itama a gaba. Dole badan tana ra'ayi ba ta fara barin maneman nata suzo gida saboda Mitar Mama ma kadai ta isheta sedai kuma wata sabuwar jarabawa data bullo mata duk wanda yayi zuwa daya gidan baya dawowa sedai su shiga yi mata wasa da hankali a waya da son cewar su hadu a wani gurin, wasu ma daga haka se zancen banza ya shigo ciki duk wanda kuwa ya kawo mata zancen banza zagewa take tayi masa tijara dan ba wai tayi sanyi ne gaba daya ba daman rayuwa ce kawai ta bida ita.

Mama ta sakota a gaba da cewar ita take korarsu da baqin halinta. Sassauci da rahamar data samu a gurinta ta fara ja baya suka koma yar gidan jiya fada kyara da hantara kullum ta dira mata mitar taqi fitar da Miji tunda ba maneman ne bata dasu ba korarsu takeyi.
"Nasan me kikeyiwa qulafucin komawa gidan Khalil kikeyi to tun wuri Idan zaki cire ranki akan sa ma ki cire dan baze maidake ba, ke idan kina da kunya ma in aka ce ki koma se ki yarda? Ki kalli Hajiya Aisha da wane idon bayan dibar Albarkar da kikayi mata? To idan ma zaki fiddashi a ranki tun wuri dan rigada ya miki nisa, tazarar ku tamkar ta sama da qasa ne. Yana can yana rayuwarsa cikin jindadi da kwanciyar hankali tareda matarsa da take sonsa take girmama mahaifiyarsa shekara bakwai kenan kina zaune idan da ze waiwayeki da tuni ya nuna alamu dan haka gara tun wuri ki samu wani ya rufa miki asiri ya aureki dan ke kam a yanzu sedai kiyi auran rufin asiri" haka Maman take yaba mata magana duk kuwa sanda ta fada mata haka ranar wuni zatayi tana kuka.

Amma ta yarda da ita datace Khalil baze waiwayeta ba. Yaranta suna yawan kiranta da wayarsa musamman Bibi, sau da yawa suna tare dashi tana jin muryarsa yana hira cike da nishadi amma koda wasa be taba gaisawa da ita ba ita ma kuma tayi namijin qoqari gurin riqe kanta bata tambayar yaran shi haka indai ba su suka kira ba bata kiran layin nasa, daga bayane ma da zuciyarta ta gaza, tana ganin idanhar bata nemi yafiyarsa ba bazata qarasa samun cikakkiyar nutsuwa ba se ta ringa tura masa da Text message na ban haquri amma ko sau daya be taba maida mata da amsa ba haka ko ya kawo yara sun hadu be taba yi mata kallon wata halitta da zaman aure ya taba hadasu ba balle har tasa ran ganin soyayyarta a kwayar idonsa. Idan ta gwada kiran layinsa ma baya shiga sedai idan yaran ne suka kira da kansu tasan kuma shiya saka lambar tata a wani tsarin ta yanda bazata same shin ba, seta koma canza layuka dukda hakan batayi nasara ba dan baya dauka, daman tun Asali ta sani da wuya ya amsa baquwar number in dai ba me ita yayi masa saqo ya fadi wanene shi ba, dan haka kota kira baya dagawa. Daga baya ma har wayar Mama take dauka ta kirashi, tayi haka kusan sau uku duk be daga ba sedai daga baya ko da daddare zataji suna waya da Maman alamar se sannan ya samu sukunin kira kenan akan hakan Mama tayi mata tatas data gane ita ce take kiransa da wayar, ta ringa mata gori da Tijara kai ba zakace ita ta haifeta ba, irin wadannan abubuwan kadai sun isa su sanar mata da matsayinta a gurin Khalil yanzu dan haka dole taja jikinta ta kuma karbi qaddara a yanda tazo mata koma meya faru itace sila, ita ta siya da kudinta. Data haqura ta zauna dashi kamar yanda yasha fada mata ta sani babu wata Mace da zata zo ta zarce ta matsayi a gurinsa seta biyewa kururuwar shaidan ya kaita ya baro gashi ta qare a nadama da dana sani mara amfani.

Tun daga nan ta sake janye jikinta akan lamarin Khalil amma bata fasa tura masa da saqonnin ban haquri ba dan wannan ya zame mata dole, tana buqatar Afuwarsa data sauran Ahalinsa amma Khalil din ya shareta funfurus kamar baya ganin saqonnin Alhalin kullum ta turo seya duba ya karanta sannanya goge. A haka taci gaba da aikinta, Al'amarin zawarawa kuwa abin tun baya damunta har ya fara bata tsoro. A lissafe cikin qasa da wata biyu tayi Zawarawa sun kai Goma amma babu guda daya daya tsaya daga zuwa dayan nan basa dawowa. Dama duk wanda taga take taken ze zo mata da wata maganar blocking dinsa kawai takeyi ta dena biye musu tayi masifa tunda ta fahimci Al'amarin Mazan yanzu ya qazanta sedai kawai ace innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Fasadi yayi yawa a doron qasa, babu kunya babu tsoron Allah mutane sun maida zina Ado musamman ga Mazan aure da matan auran ma dan abin ya zarce yammata yanzu masifar ta girmama kuma babu tsoron Allahn daya halicci mutum qiri qiri suke zuwar mata da buqatarsu, ita dai batayi kalar yar iska ba haka nan bata shiga da take bayuynar da jikinta Hijabine kullum take bulalawa har qasa dan da yawan zawarawan seda suka mata qorafin shogar tata wai tana rage mata kyau sannan bata da sakin fuska ko sakin baki da ze saka suga lakwa lakwan da zasu zo mata da maganar banza amma a hakan dai bata tsira ba.

Da Hadiza kadai ta iya tattauna maganar wadda yanzu sun dinke sun zama Qawaye har gidansu take zuwa itace dai sau daya ta taka gidan Hadizan tana kuma bala'in jin dadin tarayyarsu saboda yanda take qaruwa da ita ta fuskoki da dama. Kasancewar Hadizan Lawyer gomnati Umaiman najin labarin kesa kesai a gurinta da suke qara sakata tsoron Allah ta kuma tsoraci duniya. Idan taji wani abun se taga ashe ita a iskancin ma ba abinda ta iya manyanta na gaba ta kuma godewa Allag daya bata ikon gano kuskurenta ta kuma gyara tun gabanin lokaci ne qure mata ba. Sanda take yiwa Hadiza zancen matsalarda take damunta game da rashin tsayawar Maneman nata sa kuma irin abubuwan da suke bijiro mata dasu dariya kawai tayi take ce mata

"Ki godewa Allah ki kuma cigaba da neman taimakonsa dan a dukkan al'amuranki, ba wayo bane ba dabara ba Umaimah muna cikin wani zamani da ubangiji ne kadai ze shige mana gaba. Karki sakawa ranki damuwa duk wanda kikaga yazo ya tafi ba mijinki bane babu kuma Alkhairi a tare dashi, in sha Allahu da sannu zaki rabauta da tanadin da ubangiji yayiwa bayinsa da sukayi kuskure kuma sukayi tuba na haqiqa karkiyi sauri a rayuwa labari na kadai ya isheki Misali, kina kallon abubuwan dana fuskanta a rayuwa qila badaban faruwarsu ba bazan dace da irin Mijin da kalar rayuwar dana samu a yanzu ba".
Jikin Umaimah yayi sanyi laqwas da kalaman Hadizan, koda ba da wata manufa ta fada ba amma maganar ta shafeta saboda duk idan za'a bada tarihin Hadiza da gwagwarmayar data sha tabbas seta fito a shafin mummunar qaddadararta.

Data sakeyiwa Rumasa'u Farar Aminiya maganar itama dai kamar Hadizan ce mata tayi ta share komai taci gaba da Addu'a in sha Allahu Alkhairi yana gaba da wannan tadan samu nutsuwa amma kwarzabar Mama tasa dan kumarin data farayi ya nemi guduwa, data dawo gidan zata kafa mata mitar wance ta haihu wance tayi kaza, tun ba da Hajiya ta kira Maman take gaya mata wai Bibi ta fara Al'ada ba ranar kam taga abu, Mama harda cewa seta jira su jera ita da Bibin suyi aure rana daya tunda taqi tsayar da Miji to ga yarta nan ta girma ko yanzu za'a iya kaita daki. Akayi katari ranar wani ya aiko sallama da ita ta fatattaki Yasir dayazo fada mata saqon Mama ta qara samun nayi seda Abba ya saka baki kafin ta barta ta shaqi iska me dadi a gidan. Kodan abinda Mama take mata da zata samu Miji ko wanene zatayi aure amma ta rasa, abinda bata sani ba duk wanda yazo da yan Majalisar qofar gidansu sun qyalla ido sun ganshi zasu bi baya su lalata komai ta hanyar bashi labarin qarya da gaskiya daya faru su kuwa daga nan su gudu se su zagayo mata da zancen iskanci.

Ire iren wadannan abubuwan suke qara jefata cikin damuwa idan ta tuna zamanta da Khalil a lokutan data ringa wukaqantashi da gayya tana hankadawa Matan waje shi. Me yasa bata taba yin wannan dogon tsinkayen ba, mata na waje suna farautar Maza wasu ma basuji ba basu gani ba matan ke jansu tana kallo irin haka na faruwa a gurin aikinsu ballantana irinsa a lokacin da yake cikin buqata badan tsarewar ubangiji ba ai da tuni Khalil yayi tambari a neman Mata amma ya kame kansa duk saboda ita magana me tsaho bayayi da mata hatta wanda suke ciki daya a gaban idonta se yayi mata wannan Alkunyar dan kar ranta ya baci duk irin halaccin nan da yayi mata amma ta kasa yi masa uzuri akan abinda ba haramci ba to da

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login