Showing 111001 words to 114000 words out of 429394 words

Chapter 38 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

991

katsewa kafin ta daga cikin muryar kuka ta amsa sallamar Hajiyan.

"Umaimah lafiya meya faru a gidan Zara'u? Ta kirana tana gaya mun wadansu maganganu da ban ganewa kansu ba sannan na tambayi Khalifa yace be san komai ba" Hajiyan ta fada cikij muryar damuwa musamman yanayin kukan da taji kamar Umaiman nayi.

Kuka Umaimah ta fashe dashi kamar yanda zuciyarta ta kitsa mata ta fara cewa
"Hajiya wacece wadda kika tura mu gidanta, haka kawai da farko baki ga yanda ta karbe mu ba faran faran muka gaisa amma tana ganin Khalifa ya fita ta canzamun fuska ta shiga zagina tana zagin iyayena, bata gaji ba Hajiya ta gayyato wata mata itama tazo suka hadu har tana cemun mayya wai na cinye muku zuciya keda Khalil ya zabeni ya bar yar uwarsa to wallahi ban isa ba se taga bayana, in saka ido in gani seta rabani da Khalil" ta qarasa tana fashewa da kuka.

Salati Hajiya ta ringayi kamar zatayi kukan itama ta ringa bawa Umaimah haquri amma kamar wadda take tunzurawa se qara rusa kuka take tana cewa
"Babban abinda ya fi mun ciwo hajiya har fa cewa takeyi Khalil ya gurbata muku zuri'a ya auro mayya gashi nan na haifi maye wai mu'ayyad ya zura mata ido yana kallonta duk abinda ya sameta bazata yarda ba" seta sake rushewa da kuka.

Ran Hajiya ya baci tace
"Ki kwantar da hankalinki in sha Allahu babu abinda ze faru se Alkhairi, maita kuma data dora miki seba bi miki kadinki ki barni da ita" haka ta ringa lallashinta ita kuwa se sake rura wutar take ta hanyar fadar maganganun qarya akan Goggon ta jefeta dasu da haka sukayi sallama.

Wasa wasa qaranar magana ta zama babba dan korar ne lalle Umaimah tayi tace bazatayi ba ta kuma rantse akan bazata koma gidan Khalil ba an tanbayeta meya faru tayi shiru se kuka takeyi da suka gaji suka qyaleta.

Washe gari Khalil ya dawo, kansa a qulle saboda maganganun da Hajiya ta gaya masa da wanda Badariyya da Mahaifiyarta suka kira suka gaya masa ya rasa wanene me gaskiya a ciki? Haka kawai zuciyarsa tafi gasgata zancen Badariyyah musamman da tun a daren yake neman layin Umaimah yana shiga amma bata dagawa.

Kai tsaye gidansa ya wuce dan duk tunaninsa ya bashi ta koma sedai yana zuwa ya tarar da qofa a rufe, da muqullin hannunsa yayi amfani ya bude qofar ya shiga, gidan tsaf an gyara ko ina dakinsa ya wuce ya ajiye kayan daya shigo dasu ya fada wanka dan ya kwaso gajiya a mota sukayi tafiyar kuma shi yayi tuqin. Seda ya shirya sannan ya wuce gidan Hajiyarsa, a can yaci abinci tana sake maida masa zancen abinda ya faru cikin bacin rai bece mata komai ba se haquri daya bata ya ci abinci ya wuce gidan su Umaimah.

Tana kwance akan gado Saufullahi ya shiga yace tazo inji Mama, doguwar rigar Atamfa ce a jikinta ta mayar da hular data zame daga kanta tabi bayansa, tun daga qofar palour take jiyo qamshin turarensa seta sake tamke fuskarta ta shiga sa sallama ciki ciki.
Yana zaune akan kujera da Mu'ayyad a hannunsa ta samu kujerar bakin qofar ta dofana tana masa sannu da zuwa, fuska babu yabo babu fallasa ya amsa mata hankalinsa na kan yaronsa, abin ya bata mata rai ta sake tunzura baki gaba, bece mata komai ba yana ci gaba da yiwa Mu'ayyad wasa Mama ta shigo tana kallonta tace

Kije ki nunawa su Nazifi kayan da zasu fitar miki dasu ku wuce dare yanayi"
"Nifa Mama na gaya miki babu inda zanje, yaje can ya auro yar uwar tasa su zauna tare" Umaimah ta fada tana tunzura baki se suka kalleta gaba daya, a zuciyaraa yana sake samun tabbacin abinda aka ce ta aikata dagaske tayi shine ta zagaye ta karantawa Hajiya qarya da gaskiya ta sakata ciwa Goggo Zara'u mutunchi har abin ya nemi ya zama rigima seda Baffansu ya tsawatar shine yanzu nan zata nemi ta caja masa kai ko.

"Banason iskanci Umaimah, ki wuce ki hada kayanki nace miki idan ba so kike ranki ya baci ba" Mamanta fada murya babu wasa se Umaimah ta miqe tana cewa
"Wallahi Mama dagaske nakeyi bazan koma gidansa ba, seyaje ya auro duk wadda yaga dama" tana gama fadan haka ta miqe ta bar dakin.
*SUMAYYAS_HERBAL_APHRODISIACS*

*Shin yar uwa kina da wata matsala ce data shafi zamantakewar aure da kika kasa gane kanta? Ko kuwa a bangaren megida ne Al'amura basa tafiyar miki daidai yanda kike so*

*Qaiqayin gaba, farin ruwa ko ruwa me qarni yana fitar miki kinje Asibiti kinsha magani har yanzu ba'a dace ba? Ko kuwa kin kasa gane kan mu'amalar auratayya bakyajin dadi ko kina jin zafi a lokacin saduwa*
*Aa damuwarki inda zaki samu ingantattun magungunan mata marasa illah wadanda masana ilimin suka hada ba yan taka haye to ki garzayo nan domin muna da maganin matsalolinki da yardar Allah*

*A Sumayyas_herbal_aprodiasics* *muna bada ingantattun magunguna wadanda masana sukayi bincike suka tabbatar da suna samar da waraka ga dukkan matsalolin da kuka zo dasu*
*Muna da maganin sanyi ko wanne iri da yardar Allah zamu baki bayan munyi miki tambayoyi domin sanin yanayin lakurarki*
*A bangaren kayan gyara muna da ingantattun tsumi, Gumba, Kaza/ciccibi, Sabaya na gyaran Nono, maganin qiba dana rage qiba ingantattu da babu kwaya a cikinsu*
*Sannan munada tsari na tattaunawa da mata domib musan matsalolinku mu kuma baku shawarar yanda zaku magance su da yardar Allah*
*Adreshin mu Zaria/Abuja muna kuma aika kaya ko ina a fadin qasarnan cikin Amincin Allah kutuntube mu akan*
*07031876677*
Ko a IG *sumayyas_herbal_aphrodisiacs*

*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* =?L?
PAGE 31

Juyawa Mama tayi da niyyar binta Khalil ya dakatar da ita da cewa
"Ki barta Mama yanzu tana cikin bacin rai idan ta sakko dan kanta seta dawo" ya miqe tareda kwantar da Mu'ayyad akan kujerar yayi mata sallama ya fita, dakin da Umaimah take ciki ya shiga tana tsaye a jikin window tana dakon ganin wucewarsa daman ta waiwayo da sauri tana cewa

"Na gaya maka bazan koma ba, harni za'a tura gidan su budurwarka su wukaqantani, daman kuna tare har yanzu qarya kayi mun da kace kun rabu toh Allah ya tona maka asiri na sani kuma zama dakai na gama sedai kaje ka aurota ragowar wasu can ka qarata da ita".

Cikin bacin rai ya kalleta yace
"Karki sake aibata ta dan jinina ce bazan iya canzata ba sabanin ke da zan iya rabuwa dake, sannan ita wadda kikaje kika yiwa rashin kunyar qanwar mahaifina ce uwa daya uba daya har kika iya tsayawa a gabanta kika zageta idan da kinsan darajar babba kome zatayi miki ai bazaki tanka ba taci albarkaci na amma shikenan kici gaba da duk abinda kikeyi akwai ranar da zaki kwashe kashinki a hannu. Zama kuma kiyi ta zama gaki ga gidan nan har sanda kika gaji" Yana gama fadar haka ya fice daga dakin cikin bacin rai ya bar gidan a ransa ya qudurce shekara dari daga yanzu baze sake waiwayarta ba, duk abinda ta yanke a wannan gabar akansa ze tafi. Saboda bacin rai be iya komawa gida ba gari ya shiga ya ringa yawo abinda be iya ba ga wutar sha'awarta dake damunsa sabida ya gama saka ran a ranar zata dawo, har wasu hadi Abokinsa ya bashi acan sokoton yasha danma bacin ran da yake ciki ya danne kaso hamsin na buqatar da yake ciki amma duk da haka yana cikin wani yanayi.

Gajiya yayi da yawo ya samu wani gurin shaqatawa ya zauna, daga gefe can yana hango yammata da yawa sunsha anko kamar dai wani shagalin biki suke gabatarwa a gurin dan yaga wata da tafi yin kwalliya kamar Amarya. Yana zaune a gurin har suka gama suka fara watsewa hankalinsa yayi nisa a tunani yaji sallama a kusa dashi. Firgigit yayi ya kalli masu sallamar, yammatane guda biyu suna sanye da kalar Ankon daya gani suka gaishe shi ya amsa yana kallonsu da rashin sani.

Wadda tafi kalar rawar kai a ciki tace
"Sannu Malam kayi haquri mun dameka ko dan Allah taimako muke nema"
"Toh, taimako kamar na me kenan?" Ya fada yana kallonsu a ransa yana tunanin me ze taimaka musu dashi.

"Biki mukazo kaga ni bamu sani ba har dare yayi ashe mun rasa motar tafiya gida duk wanda muka tsayar se yace mana ba hanyar zeyi ba ga lokaci yana ta sake tafiya dan Allah idan babu damuwa ka taimaka ka kaimu gida mana" Budurwar ta sake fada dayar tana zungurinta akan tayi shiru amma taqi.
Kallonsu yayi sama da qasa, a haka dai basuyi kalar watsatstsun yammata ba kuma ya ga dagaske bikin sukazo amma me yasa sun san unguwarsu ana wahalar samun mota zasu kai dare a gurin har qarfe sha daya na dare shi ya rasa ma wannan abu da zaace biki ba zaayi shi a cikin gida ba se an tafi yawon guraren shaqatawa kuma ita Amaryar ya za'ayi ta tafi bata tabbatar da duk jama'ar data tara kowa ya isa gidansu lafiya ba?

"Dan Allah ka taimaka mana idan kuma ba zaka iya ba mu nemi wani dare yanayi" yarinyar ta sake fada taba marairaicewa, se Khalil ya kalleta kamar yace bazashi ba se kuma tausayinsu ya kamashi, Mata ne idan be taimaka musu ba besan gurin wa zasuje ba shin zasu samu na gari ko kuma mugu a yanda rayuwar nan ta lalace haka, muqullinsa da wayarsa ya dauka yayi gaba ba tareda ya musu magana ba suka bi bayansa, har sun isa jikin motar suka waiwaya,

"Hadiza bazakizo mu tafi ba" suka hada baki gurin fada se ya waiwaya ya kalli wadda suka kira da Hadizan, tana sanye da irin kayansu sedai ita ta dora hijabi daya kai mata guiwa akai. Su ukun suka shiga ya dauki hanyar Na'ibawa kamar yanda suka gaya masa sunan unguwarsu, seda ya kaisu har qofar gida, a lungu suke cikin ransa kamar ya dake su ganin yanayin unguwar tasu sannan hat su iya kaiwa dare haka dole su rasa motar dawowa ai.

"Bazaki bari ya qarasa dake gida ba Hadiza?" Mw rawar kan cikinsu ta sake fada ganin itama Hadizan ta sauka bayan su biyun sun fita seta girgiza kai tace
"Aa nan ma yayi, na kira Musa nace ya jirani a nan mu qarasa gida kin ganshi can ma" ta fada tana nuna dan matashin saurayi da suke tsaye su biyu daga gefe, Khalil yabi shi da kallo kamar su daya da ita hakan ya nuna qaninta ne ya tabe baki ya tada motarsa sunayi masa godiya be ko bi ta kansu ba ya juya mota yana jin dayar na cewa
"Kunga be karbi lambar ko daya daga cikinmu ba babu wadda tayi masa ai shikenan".

Kafin ya kai gida sha biyu tayi, haka ya lallaba yasha ruwan lemon tsami ya kwanta, kafin bacci kuwa ya dauke shi yayi wanka yafi sau goma haka yayi bacci a wahale.

A can gida kuwa fada Mama ta rufe Umaimah dashi kamar zata daketa seda Anty ta shiga tsakani,
"idan kika kashe auranki Umaimah ki nemi gurin zama badai a gidan nan ba tunda ke shaidaniyar yarinya ce mara jin magana. Yanzu daman abinda kika je kikayi kenan sannan kika hada musu rigima a cikin family saboda bakya tsoron Allah kici gaba Umaimah idan daidai kikeyi zaki gani" Mamq ta fada muryarta na rawa kamar zatayi kuka Anty ta shiga bata haquri ta fice ta barsu.

Fada Antyn ta ringayi mata se kuma jikinta yayi sanyi, tun a daren ta fara neman Khalil amma bata samun wayarsa ita kanta bata iya bacci me dadi ba a ranar har washe gari kuwa yaqi amsa mata waya seda aka kwana biyu sannan ta same shi shima amsa daya ya bata bayan data gama surutunta yace ta zauna ta qara hutawa sosai karta dawo yanzu. Kuka wiwi ta dasa musu akan se su nemo shi su bashi haquri daman Abbansu baya gari lokacin da ta qulla tsiyarta, koda ya dawo aka mayar masa da yanda akayi be ce mata komai yace a rabu da ita ai Bari ba shegiya bace idan taji jiki da kanta zata maida kanta gidanta shiyasa koda tana tanbotsan haukanta babu wanda ya kulata, data ishesu da iface iface Mama tayi mata biji biji dole ta shiga hankalinta.

Binbini da kiran waya kuwa babu irin wanda bata yiwa Khalil amma kullum amsar daya ce ta zauna ta qara hutawa dukda dauriya ce kawai yakeyi dan ya fuskanci idan ba ya zama namiji akan Umaimah ba iskancinta kullum qara ta'azzara yakeyi.
Seda aka shafe sati uku a haka, ganin fa dagaske Khalil ya fita a sabgarta dan daga baya dena daga wayarta yayi ko idan ya daga yace mata yana aiki ze kira kiran da bazeyi ba kenan seta komawa fakewa da Mu'ayyad. Haka kawai zata kirashi tace suna son abu, ranar farko yazo har qofar gidan ya kaqo mata siyayya tuli abinda ta nema da wanda bataa nema ba be shiga ba ya bawa yara ya hada mata da kudi cikin envelop yace akai mata.
Ranar akan yan aiken ta huce ta ringa rashin mutunchi da tijara a cikin gidan kwana biyu a tsakani ta dorawa Mu'ayyad ciwon qarya nan ma bezo ba ya turo mata Khalifa dan bama ya gari a sannan yayi tafiya.

Kuka wiwi ta kirashi a ranar tanayi masa ta bashi haquri yace mata yanzu dagaske ze haqura amma da sharadi, sharadin kuwa shine se taje ta gayawa Hajiya da bakinta duk abinda ta fada mata qaryane saboda yanzu haka akan wannan dalili gaba me qarfi ta qullu tsakanin Hajiyar da Goggo Zara'u haka cikin dangi sun kasu biyu kowa da wanda yake goyon baya.

Hankalin Umaimah ya tashi da jin wannan sharadi nasa toh ta ina zata fara zuwa ta cewa Hajiya qarya takeyi yanzu? Amma da yake neman shiri takeyi tace masa ta yarda washe gari kuwa babu wanda ta gayawa inda zata da sassafe ta wanke qafa tayi gidan Hajiya, Mamakin da Hajiya ta nuna na ganinta da kuma tambayarta da takeyi na yaushe suka dawo ya sakata chanza plan ashe Hajiya batasan da cewar har sannan tana gidansu ba daga baya ne ma da taji shiru kwana biyu ta tambayi Khalil yace mata ta tafi Minna gurin Yaya Naziyya da suka koma can da Mijinta dan ko haihuwar Umaiman bata samu zuwa ba shine taje gaisheta.

A maimakon ta gyara abinda ya kaita seta zauna ta sake zuba sabon lalen gurmi, kuka ta fasa wa Hajiya akan Khalil yayi fushi da ita tun akan waccen maganar dan har yanzu tana gida yace ba zata koma ba seta je ta bawa su Badariyyah haquri, ran Hajiua ya baci ta dauki waya zata kirashi Umaimah ta hana

"Idan kika kirashi Hajiyavze qarayin wani fushin yace na hadaki dashi, nidai dan Allah karki gaya masa na fada miki wani abu, kawai ki nuna masa kinsan ina gida har yanzu ya barni na koma dakina dan yanzu wallahi Hajiya gidanmu kowa fushi yake dani babu meyi mun magana" Umaimah ta fada tana matsar hawaye, Se????? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? 
Hajiya taja kwafa tace

"Da kin barni na kirashi ai naci masa mutunci mutumin banza kawai yanzu shi har idan yana da zuciya ze saka daga ido ya kalli Zara'u da duk wani natane mutanen da suka qishi saboda abin duniya shine yanzu zasu dawo masoyansa, ze dawo ya sameni ita kuma Hajiya Malika da zata ringa biye masa itama zanje har gidan na sameta ai haba shikenan se abi a tsangwameki kuma akan gaskiyarki" haka ta ringa fada daga qarshe tace ta koma ta hada kayanta ta koma dakinta shi kuma Khalil din zata hadu dashi idan ya dawo suka rabu Umaimah na sake roqon karta gayawa Khalil komai, a daren ranar kuwa se gashi da kansa ya kirata yace ta shirya washe gari ta koma shi se jibi ze dawo, Roqonsa tayi akan ya bari ta koma jibin da safe dan gobe zatayi kitso da sauran shirye shirye haka kuwa akayi washe gari ita kadai ta ringa hidimarta daman Anty ce me tayata ita kuma bata nan Ankwantar da yayarta a Asibiti ita take jinyarta.

Bayan komawarsu tayi zaton zeyi mata fada ko ya tado da maganar sedai taji shru, tun tana dari dari harta sake suka ci gaba da rayuwarsu tamkar babu abinda ya faru. Sabon? babi suka bude na rayuwa me cike da qauna da tattalin junansu, Tsakanin Khalil da Umaimah kullum cikin rige rigen kyautatawa junansu suke tareda tattalin tilon dansu da suke ji dashi kamar tsoka daya a miya. Qarin hidimar Mu'ayyad da rashin sabo ya saka aiki ya kan kacamewa Umaiman musamman da Mu'ayyad din ya koyi rigima ya koda yaushe yafi son yaji shi jikin mutum dan haka idan dai ba yana hannun Khalil ba to sedai ta goyashi idan tanaso tayi ayyukan gida, saboda rashin sanin yanda zata tsara ayyukanta se ya zamana wani lokacin har Khalil ya dawo daga aiki bata samu ta kammala abinci seya jirata haka wankin yaron duk takarar da Mama tayi mata a gida akan karta ringa tara wanki tayi qoqari da tayi masa wankan safe ta wanke kayan daya bata amma bata iyawa gajiya takeyi dan lokacin hutun nata idan yayi bacci sannan take samu ta leqa social media dukda yanzu ta kiyayi duk wata da take shishshige mata dason yin qawance da ita qarqarinta hira a group shikenan.

Qarin abinda Yafi damunta a yanzu shine yawan tafiye tafiyen da Khalil yakeyi kuma yace dole da ita ze tafi dan idan har tafiya ta wuce ta kwana biyu tofa qafarsa qafarta wanda sam ita abin beyi mata ba bata so kullum cikin qorafi take da wuya kuma suyi tafiyar aje a dawo lafiya basu bata ba, ta ringa mita kenan da fadar maganganu da azatonta zasu saka yayi zuciya gaba ya qi tafiya da ita kamar yanda Rufaida ta bata shawara amma ko a jikinsa, yi yake kamar besab tanayi ba.

Wata shida da haihuwar Mu'ayyad idanka ganta seka dauka Yara biyar take raino yanda gaba daya ta hargitse shikansa gidan ya fita a kamanninsa duk inda ka duba kayane zube na sakawa da kayan wasan Mu'ayyad.

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login