Showing 159001 words to 162000 words out of 429394 words

Chapter 54 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

1597

kawo dan ita haka take duk wani tsegumi na gidan zakajishi a bakinta.

"Zonan" Mama ta sake fada seta shiga tana rarraba ido Mama ta sake cewa ya akayi?"
"Daman, daman na kaiwa Yaya Umaimah ruwan wanka ne shine naga fuskarta ta kumbura sosai kamar ko faduwa tayi inaga ko Kuka tayi" ta fada tana satar kallon Salman se Mama ta daga mata hannu alamar taje ta kuwa fita da sauri kafin ta juya kan Salman tace

"Zaka fadamun inda kukaje ko se na hada dakai duka naci ubanku"
"Nidai Mama wallahi a waje muka hadu tace nazo na kaita Asibiti, seda muka dauki hanya tace Na'ibawa zamuje kuma koda mukaje a waje na tsaya ta shiga wani gida ban kuma san abinda tayi ba ta fito a yanda kuka ganta muka taho bata ce mun komai ba har muka zo gida" Salman ya fadi iya gaskiyar abinda ya sani. Mama dake kallonsa ta sauke ajiyar zuciya tace

"Shikenan tashi kaje Allah ya rufa asiri" ya miqe yana cewa
"Amma dan Allah Mama kar kice mata na gaya miki komai, kinsan Halin Yah Umaimah seta huce a kaina"
"Kaje abunka" Maman ta sake fada daga nan tayi shiru ta zubawa Tv ido dukda ba kallon abinda ake yi a ciki takeyi ba illah kogin tunani data tafi.

Umaimah ko ranar ko abincin dare bata fito taci ba kuma babu wanda yayi mata tayi haka ta kwanta seda cikin dare taji Yunwa na neman ranta kafin ta sanqami Burodi da ta kada madara da Milo a ruwan sanyi tasha, washe gari kuwa da wurwuri tun farar ta fita da kanta ta dora ruwan Wanka ta zuba wani a falask da zata sha shayi ta qule a daki. Batason a tuhumeta, kuma yanzu duk wanda yaga fuskarta seya tambayi meya faru.

Har goman safe tana daki, bata zata ba se ji tayi ana murnar dawowar Abbansu da ya tafi Umarar Mauludi, dafe kanta tayi dan yanzu kam bata da dama dole ta fita tayi masa sannu da zuwa amma ba zataje yanzu ba seda daddare. Wayarta ta dauka ta sake gwada kiran number Khausar amma har sannan a kashe ake gaya mata dan tun jiya bayan ta dawo daga gidan su Hadiza take kiran layin amma a kashe.
Kiran Rufaida ne ya shigo mata taja tsaki kafin ta latsa wayar ta shiga silent dan a yanzu haushin kowa takeji, idan ba ta rama abinda Yayan Hadiza ya mata ba kuma ta ci uban Hadizan bazata samu sauqin abinda takeji a zuciyarta ba kuma ba zata tunkari Khalil yanzu ba se bayan ta gama da qaramar yar iskar tukunna zata koma kansa shima taci masa uwa, qilan karuwar tasa ta gaya masa abinda ya faru shiyasa tun tsahon jiya zuwa yau be nemeta ba amma zasu hadu ne, seya gane ita ya ciwa Amana.

WhatsApp ta shiga tana budewa kuwa sega saqon Khausar harda sauke ajiyar zuciyavta bude ta tarar da Voice note data turo mata bata bata lokaci ba ta kunna ta fara ji
"Jiya naji labarin abinda ya faru, yanzu kika yarda ace ga mari ga tsinka jaka?
Ta bi miki miji kuma kinje bin ba'asi yayanta ya dokeki wallahi karki yarda idan ba haka ba kina nan zaune ganin idonki zata aure miki miji kuma daga nan sunanki sorry, dan haka idan kin shirya inada qarin hujjoji da idan kika same su ko a qafa aka daurawa Mijinki na tabbatar da seya kwance ta ya gudu. Kafin nan dai kiyi qoqari ki kwaci yancinki ki rama abinda akayi miki idan kuma kinyarda kin karbi faduwa shikenan".

Cikin sauri ta fara typing bayan da ta gama Jin voice din se kuma ta goge ta mayar mata itama da Voice tace
"Idan na gama da ita ina nan kan juyowa kanki tsohuwar Annamimiya dan na tabbata bakinku daya dake da ita tare kuka hada duk wata qulla qullar datake bin mijina Allah kadai yasan dalilin da ya saka yanzu kika zame kika dawo kina bani bayanai a kanta, toh ni ba mahaukaciya bace da kike zaton zan yarda dake, idan ma kin angizani ne saboda a cutar dani toh ta Allah ba taki ba gani nan garas babu abinda ya sameni kuma zan dawo da shirin cin kutumar ubanku gaba daya keda su, kin gama mun aiki tunda har kika kaini gidansu, ki jirayeni idan na gama da ita kanki zan juyo" tana turawa ta dannawa lambar block dan zuciyarta ta gama bata bakinsu daya da Hadizan, qila ma wani shiri ne sukeyi na su fitar da ita daga gidanta dan su samu damar samun Khalil ita kadai toh kuwa uban da ya haifi uwarsu ma yayi kadan kuma daidai take da qugun kowaccen su.

Wuraren uku na rana saqo ya shigo wayarta.
"Naji saqonki kuma naga kinyi blocking numberta, toh ki duba na tura miki saqo da wata sabuwar number. Ni me qaunarki kuma bana nufin cutar dake sema kareki daga cuta da ha'incin da ake miki a bayan idonki amam zaki gane ba yanzu ba".

Tsaki ta buga duk yanda bata so amma zuciyarta seda ta tilastata ta bude saqon da tace ta tura mata a waya ta kirata, kai tsaye tace idan zata samu dama zata tura mata,
Hoton Hadiza da Khalil ne idan batayi kuskurena Ranar da ya tafi SA ne, babban abinda ya daga mata hankali hoton a cikin jirgi akayi shi, a zuciyarta ta ayyana 'kenan tare suka tafi' kamar kuwa Khausar tasan tunanin da takeyi kenan ta turo mata da cewar
"Tare suka tafi, a cikin satin daya wuce ta dawo kuma tace zata sake komawa dan daqyar ya barta ta taho".

Wani abu taji ya danne zuciyarta yana neman katse mata numfashi se kawai ta sulale a qasa wasu hawaye masu zafin gask suka shiga kwararo mata. Kwakwalwarta tamkar an liqeta ta kasa kawo mata kowanne tunani illah na Khalil da Hadiza ya tafi, kenan shi yasa sam baya wani nuna kewarta lallai Khalil.

Anty da shirun Umaiman ya dameta ce ta ga Abba ya dawo har su Maman Asad sunzo tace bari dai ta leqa ko lafiya Mama dai ko a jikinta sabgarta takeyi. Yanda Antyn ta tarar da ita ya bata tsoro, ta dagota tana tambayarta lafiya meya samu fuskarta ta kasa cewa komai se kuka kawai. Qirjinta zafi yake zuciyarta kamar zata fashe wai Khalil ya raba musu kansa ita da wata Karuwa a waje wallahi ko duniya zata tashi bazata yarda ba, seta daidaita yarinyar nan idan ma bata halakata ba.

Kuka kashirban ta dasa sanda Anty ta yayibo mutanen gidan akan suzo su ga yanda take, Mama dai bata zo ba tunda taji kan zancen jiya ta barwa ranta duk ma inda taje da abinda tayi z fito ne a bakin su taji wai tace musu zamewa tayi a bandaki Hankulansu suka sake daguwa Maman Asad na ta tashi su tafi Asibiti tace babu komai lafiya lau take jinta dukda haka bata haqura ba seda ta kira wata qawarta ta hadata da Umaiman tayi mata tambayoyi kafin tace mata babu komai in taji wani abu ba daidai ba taje Asibiti sannan suka haqura. Mama dai dariya tayi daman tana dakin Abba daya kwanta baccin gajiya Anty take mata bayanin tace Allah ya rufa asiri daga haka bata tanka ba.

Umaimah bata samu fita zuwa inda Khausar ta kirata ba, kwana tayi idonta biyu tana saqa da warwarar matakin da zata dauka akan Hadiza da Khalil. Qarfe daya da rabi na dare ta gaji da juyi a gado ga shi ta rasa mafita akan abinda ya kamatu tayi bata daddara ba ta sake dannan kiran layin Khausar cikin Sa'a ya shiga ringing biyu ta daga muryarta da alamar bacci take tambayar wanene

"Umaimah ce, dan Allah kiyi haquri da maganar dana gaya miki dazu raina ne ya baci baki san irin halin dana tsinci kaina a ciki ba tunda kika bayyanamun abinda yake faruwa tsakanin Mijina da Qawarki, yanzu abinda yasa na kiraki akan taimakon da kika ce zaki yimun ne shi nake so naji wane shiri kike dashi akan ta da kika ce zai taimaka mun? Sannan ke din wacece, meye alaqarki da ita sannan me tayi miki da har kika zabi ki bayyanamun alaqarta da Mijina akan ki rufa mata Asiri a matsayinta na qawarki?" Umaimah ta fada murya a dashe saboda kukan da ta sha.

Shiru Khausar tayi dan har Umaimah ta cire tsammanin tana tareda ita sannan taji tace
"Tabbas qawatace Hadiza koma nace miki Aminiyatace amma tayi mun abinda har duniya ta nade bazan manta ba kuma na kasa yafe mata, kamar yanda take qoqarin shiga tsakaninki da Mijinki haka ta ringayi mun, duk saurayin dana hadu dashi a rayuwa baya zuwa biyu gurina in gar sun hadu ze koma yace ita yake so, ta rabani da duk wasu namemana kuma itama ba auransu takeyi ba, zata cucesu ne ta karbi abinda zata karba agurinsu kafin ta barsu kinga daga ni har ita munyi Asara kenan.

Sannan bayan wannan da akwai babban sirrinta wanda qalilan mutane ne suka sanshi, Hadiza mata take nema yan uwanta abinda har yasa nake sakewa ina nunawa Samarina ita kenan dukda tafini kyau da haduwa a zatona babu abinda zatayi dasu tunda ba layinta bane amma kuma sedaga baya na fuskanci ba haka bane, qazamar rayuwa takeyi tana hada mata da Maza duka tana mu'amala dasu abin mamaki kuma Mijinki ya sani a hakan kuma yake tareda ita dukda ina zargin abin nata harda Asiri a ciki, a cewarsa idan ya aureta yayi jihadi zata dena duk abinda takeyi

Wani dum Umaimah taji akanta, yanzu a ce duk matan duniya Khalil ya rasa wadda ze nema se yar Lesbian kuma har yana fadin wai Jihadi zaiyi, sam kwakwalwarta bata nemi hango gaskiya ko qaryar abinda Khausar ta gaya mata ba ta hau kai daram ta zauna,
"Kika ce Khalil ya sani?" Ta tambayeta cikin wani irin sauti, Khausar ta juya ta kalli Shema data rubuta mata duk abinda zata gayawa Umaiman ta bata hannu suka tafa kafinta jinjina kai kamar tana gabanta tace
"Na tabbata, na sanar Miki da cewar Aminiyata ce idan kinada tantama ki tambayi Mijinki wacece Khausar qawar Hadiza" duka Shema ta kai mata a baki ita kanta bata san sanda ta bige bakin nata ba ta zaro idanu, kallon bakida hankali Sheman tayi mata se tayi saurin gyaran murya tace
"Karima qawar Hadiza zaki ce masa idan kika fadi haka duk wata maganada ze ji a bakinki baze taba qaryata wa ba danyasan nasan komai akansa da ita Hadizan kuma yanzu zan tura miki da evidence din da nace dan ki sake tabbatarwa da kanki".

Umaimah bata iya magana ba, a maganganun kaf iya abinda ta gane yar Lesbian Khalil yake shirin dauko mata a matsayin kishiya se kuma sunan Khausar da ya samu guri a kwakwalwarta dan ita bata ma ji wani rudewa da tayi akan subul da bakan na balle canza sunan da tayi, Khausar din kawai ta riqe kuma tana katse kiran tayi saving number da sunan sannan ta koma WhatsApp tayi unblocking nata sega hotuna kuwa sun fara shigowa harda videos.

Dubasu ta farayi, a zahiri hotunane irin wadanda Yammatan yanzu harma da wasu matan auran suka daukesu a matsayin wayewa. Da yawansu ta fito daga Wanka tana daure da towel qarami daya bayyanar da irin kyan dirin da Allah yayi mata, wadansu rabin qirjinta a waje anyi wasu irin dauka dai da sam basu dace ba, wasu ita kadai wasu tareda mutane sun rungume juna ko suna kwance tare typucal hotuna dai irin na wadanda suka aro dabi'ar yahudawa suka dorawa kansu sam babu ganin rashin dacewa ko wani aibu kan abinda suke yi din sannan mafi yawancinsu a Hotel aka dauke su Wanda yake alamanta da yawa a lokutan tafiye tafiyensu na aiki take daukar su wannan a tunani irin na me hangen nesa da kyautata zato akan duk abinda ya gani kenan, banda Umaimah data rigada ta hau tayi daram akan zantukan Khausar din dan haka batareda ta bata lokaci ba ta ware wadanda take ganin sunfi muni da bayyanar da abinda take son isarwa ta aikawa da kafatanin yan gidan su Khalil din tun daga kan Hajiyarsa har zuwa kan Habiba autarsu, babu kodar a zuciyarta ta qara da saqon

"Ita ce matar da Khalil yake qoqarin aurowa a ta biyu, na kuma samu tabbacin cewar yar Lesbian ce ina kuam da shaida akan hakan".

Bayan ta gama turawa ta ajiye wayar, Agogo ta kalla qarfe biyu da minti sha biyar shi acan yanzu uku fa sha biyar kenan qila yana bacci, koda yake dole yayi bacci ya dauki farka ragowar Maza da Mata ya tafi da ita shiyasa har ya kwashi kwana biyu be kira ta ba balle yaji lafiyarta data cikindaya qaqaba mata.

Wayar ta sake dauka ta shiga WhatsApp, zuciyarta ta rigada ta bushe ba kuma ta tsoron ta mutu ko tayi rai balle abinda ze iya zuwa yazo babu tunanin komai Umaimah ta ringa aikawa da hotunan data turawa su Hajiyar Khalil zuwa duk wani WhatsApp group da take ciki tare da bayanin cewar gagarumar yar Lesbian ce sannan ta sake wucewa Tiktok ta dora hotunan da irin bayanin data tura a WhatsApp. Se bayan data gama aiwatarwa sannantaji hankalinta ya kwanta zuciyarta tayi sanyi, ko iya haka aka tsaya tasan ta gaka da rayuwarta ta tona mata Asiri a idon duniya babu me sake kallonta da idon rahama sannan ba Asiri ba ko tsafi tayiwa Khalil dan ya so ta tasan wannan magana ta rushe in dai yan uwansa suka gani.

Bacci ne ya kwasheta irin na wanda ya samu nutsuwar zuciya, ranta fes kamar an wanke shi da Hypo dan ta san ta gama da wannan maganar kuma sedai wata a gaba.
*KAFIN SAUKAR DA KO WACE IRIN CUTA, SAI DA ALLAH SWT YA SAUKAR DA MAGANINTA. DON KIN GWADA MAGUNGU?????
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
NA DA YAWA BAKI DACE BA BA SHI ZAI SA KI YANKE TSAMMANI BA. KI GWADA MAGANINMU ?AR'UWA, WATA-?ILA WARAKARKI NA TATTARE DA MAGANINMU.*
?ar'uwa mecece matsalarki? Muna ingantattun saiwoyi da sassa?e da garin magunguna na gargajiya, waWanda aka gwada kuma aka tabbatar da ingancinsu.
*Ina matan da basu taSa haihuwa ba?* Ko kuma sun taSa yi amma suka samu dogon jinkiri dalilin planning ko kuma haka kawai? Ko kuwa Sari kike yawan yi, da kin samu cikin sanadiyyar mafarki sai ya fita? ?ar'uwa albishirinki, da naira 2k kacal za mu baki ingantattun saiwoyin magunguna masu kyau, da za ki dama salala kina sha a jere har na tsawon kwanaki goma sha biyu, bayan gama sha ki zuba ido wata Waya, biyu, uku, in Allah ya yarda za ki dawo da kyakkyawan labari.

*Mijinki ne mai matsalar haihuwar?* Akwai magungunan da muke ba maza, shi ma dai da naira 2k kacal za mu haWa miki magungunan da za kiyi mishi amfani da shi. In Allah ya yarda za ki dawo mana da kyakkyawan labari.

*?ar'uwa matsanancin infection/sanyi ne damuwarki?* Ki kwantar da hankalinki. Da naira 3k kacal za mu haWa miki magunguna kala biyar, waWanda idan kika yi amfani da su duk yadda sanyi yayi miki illa kuma komai daWewarsa a jikinki za ki fatattake shi. Sunan wannan haWi *Bye bye infection.*

*Mijinki ne bai da kuzari a shimfiWa?* ?ar'uwa ko ki faWa ko kar ki faWa sanyi da basir sun gama yi ma mazajenmu illa, da naira dubu 5k kacal za mu baki dafaffen magani galan Waya wanda zai dinga shan ?aramin kofi safe da yamma. Wannan magani zai taimaka masa wajen fatattakar duk wani sanyi da basir da yake jikinsa, zai dawo da kuzarinsa sosai kamar matashin ingarman doki. Bazai ?ara neman maganin kuzari ba har'abada in Allah ya yarda.

*Ina mata, maza, yara, masu fama da lalurar Cancer/Daji?* Da naira 2k kacal za mu baku ingantattun magunguna kala huWu da za ku fatattaki daji daga jikinku.

*Ingantaccen haWin sabaya=?
?* HaWin sabayarmu duniya ne ?ar'uwa. Baza muyi miki ?aryar nonuwanki za su taso su tsaitsaya kamar na budurwa ba, amma fa za su cicciko, suyi kyau, su dinga she?i, sannan duk wata rama da take jikinki za ta cicciko, ni'ima bazai yanke miki ba saboda amfani da haWin sabayarmu.

*Muna da maganin wankin nono ga masu ciki da shayarwa.* Duk Wauri Waya 500.

*Sunana Fareeda Abdallah, a kaduna nake da zama. Amma muna aikawa da magungunanmu ko ina tsakanin Nigeria da Nijer, sai dai duk inda mai siyan magani take ita za ta biya kuWin mota ko na delivery zuwa gidanta. A tuntuSeni ta whatsapp ko a kira ni akan lambobin wayata 07039080978, 09077591726. Sai kun zo=?
?=?
?=?
?*

*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* =?L?
Page 42

Bata sake duba whatsapp din bama se wash gari da kusan qarfe tara bayan tayi wanka ta karya kuma se a sannan taje ta gaida Abba yayi mata yaya jiki da tambayarta Aboki kamar yanda yake kiran duka Jikokinsa Maza tace yana gidan Hajiya. Zam zama da dabinon Ajuwa ya bata yana cewa
"Gashinan musamman nayi dawafi dashi saboda ke, kisha ki shafe jikinki da niyyar Allah ya shirya ki ya shirya tunaninki ya kuma baki lafiya keda abinda yake cikinki ku rabu lafiya".
Seta tura baki gaba wai ita me takeyi da kullum ake faman cewa Allah ya shiryata koda yak shariyar Allah ai bata yawa Allah ya shiryeta din. Seda suka taba yar hira kafin ta fita Mama dai daga amsa gaisuwar da tayi mata bata ce komai ba ta bita da kallo a ranta tana mamakin walwala da annashuwar data gani a fuskar Umaiman, sannan har yanzu da dan sauran kumburi a fuskar tata ga jini daya kwanta cikin idonta bangaren da ta sha mari.

Seda taci dumamen Tuwo ta qoshi kafin ta ciro wayar daga chaji ta bude, Missed calls ta gani sunfi Ashirin, Anty Amina, Jamila duk sun kirata ga na Jalila da yafi na kowa yawa a ciki dan haka ita ta fara kira
"Umaimah saqon da kika turamun duk su Jamila sunce suma kin aika musu harda Hajiya me yasa, badan Allah yasa wayar ta na Hannun Khalifa ba shi ya gani ya goge me kike tunanin ze faru idan ta gani? Ai da kin bari mun fara magana dake kafin kowa

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login