Showing 402001 words to 405000 words out of 429394 words

Chapter 135 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

1003

kafin suka masa barka suka tafi.

A mota Mama ta yiwa Hajiya zancen Bibi daya tsaya mata a rai danma suna makaranta shiyasa zancenya kwanta mata tun suna zaune se a motar ta tuna.
"Wlh Hajiya muna iyakar qoqarinmu, tabarar takwarata ai da ba'a kwabarta da abin seyafi haka dukda laifin Ubanne kuma shima ina tsawatar masa akan abinda yakeyi sam be kamata ba dan har yan uwan sun fara nuna rashin jin dadinsu dan idan abu ya hadosu tofa ko itace mara gaskiya ze shigar mata seda naci mutumchinsa akan haka na kuma gaya masa ze raba kan yayansa ne sa kansa. Ga wata yar banzar qawa da take da ita a makaranta da take qara dora mata karatun iyashege duk wani abun rashin kirki da kika ga tayi zakiji a gurinta ta koyo ga magana kamar Goyon tsohuwa, nidai na gayawa Uban ya canza mata makaranta tunda daman Idan sun gama Jarabawar zangon nan yace Sakandire zata shiga to ya kaita wata makarantar dan barin yaranka da irin qawar nan tata hadarine, kana tarbiyya suna warware maka kullum cikin tura mata mugayen aqidun qin matar ubanta da Yan dan uwanta takeyi, karkiso kiga yanda take hantarar yaron nan Auwalu da duka tun uwar tana kawaici har takai ta fara magana to yanzu dai abin yayi sauqi tunda Hasanar uban ta zaneta kwanaki da cewa ma tayi zata dauketa yaqi to nima ban matsa ba dan Azabar Jalilah tayi yawa, nata yayanma suka samu suka ballo bason koma mata suke ba dan ta fiya jaraba amma iya qoqari munayi Hajiya sedai mu qara".

Haka sukayi ta jajanta maganar har suka isa gidan Mama Hauwa ita dinma kamar ta goya Mama da Anty, yanda kasan akwai wata sanayya ta sosai tsakaninsu haka ta tarbesu basu jima sosai ba anan suka sube musu kayan barkar da Hajiya tace a tafi dasu can, Mama ta ringa godiya kamar me, a gidansuka bar Hajiya dan Salman ne ya kaisu ita zata jira Driver ya maidata gida suka tafi da santin kirkin Maman harda yayanta da suka tarar a gidan.

Da suka koma gidama wuni sukayi hirar fitar tasu, Umaimah nata zirga zirgarta tsakanin daki da tsakar gidan tana aiki duk abinda suke fada a kunnuwanta, idan tace batajin zafi duk sanda aka ambaci Matar Khalil tayi qarya amma babu yanda ta iya, Khalil ya zama tarihi a rayuwarta wanda ita tayiwa kanta silar rasashi ta sani kuma zata qare rayuqarta cikin nadamar abinda ta aikata ma kanta.

Wata uku da suka biyo baya yayi dadai da cikar Umaimah shekara biyar cif a cikin gidan ba tareda ta leqa koda qofar gidansu ba. Ita badan taji suna fada bama ta manta ba kuma ta damu data fitan ba to ina ma zataje? Wa take dashi da zata gurinsa yan uwanta ne kuma suna haduwa a gida a kaf qawayen nata data daukaka sama da komai babu wadda ta waiwayeta, har gara kwanaki Nuratu take ce mata ta hadu da Rufaida taje dubiya Asibinsu harta tambayeta, a lokacin murmushi kawai tayi duniya tayi mata karatu da yawa shiyasa sam bata damu ba da watsar da itan da sukayi ba, daman Mu'amalar da ba'a qullata domin Allah ai ba zata dore ba.

Tana kwance a dakinta sakamakon ciwon Mara data tashi dashi ranar saboda shirin zuwan baqonta aikin gidan ma Abin kari kadai ta iya hadawa Abba dakansa yace ta bari saboda yanda fuskarta ta nuna bata jin dadin. Tana kwancen ta jiyo sallamar Anty Hafsa da Maman Asad, bata iya tashi ba saboda yanda mararta ta daure mata tana jiyo hirarrakinsu a tsakar gida kafin suka shiga bangaren Abba dan yana gida. Sun jima acan dan har bacci ya fara daukarta taji muryar Maman Asad akanta bayan ta dana mata dukan daya farkar da ita tana cewa

"Yau halin ya motsa kenan, kina jinmu kika lafe a daki to se ki tashi dan wake nake sha'awa yau ga gari nazo dashi ki jefamun idan nayi da kaina bazan iya ci ba". Ta tashi tana yatsina fuska saboda yanda Cikinta yake karta mata Anty Hafsa kuwa cari ta shigayiwa Hajiyayyen tana cewa
"Ni ba cewa kikayi kinyi auta ba Hajiyayye? Asad fa Ya shiga Jami'a ki rufa masa asiri haka karku zo kuna jera Jego da matarsa"
Hajiyayye ta zauna gefen katifar Umaimah tana cewa
"Kai Yaya toh nawa ma Asad din yake Ashirin da daya fa, kuma wlh ni nayi niyya daga Afifa nayi auta Babansu yace ban isa ba tunda na hanashi qara aure sena haifo wanda yayi niyyar samun qari, ai shi yanzu hudu yake jira na qaro su zama goma nace wannan dinma Astagfirullah tsautsayine ina haifeshi ca zanyi su juya mahaifar Allah sa musu Albarka" suka saka dariya ita da Anty Hafsan Umaimah dai tana ta faman yatsina da gyara zama Anty Hafsa ta kalleta tace

"Qalau kiketa yatsina ke kadai, seta yunqura saboda jin kamar abu na zubo mata tace
"Marara ke ciwo"
"Aiko gashi nan kin bata jikinki, dan iskanci da a haka kike zaune kina period babu pad?" Maman Asad ta fada ita dai ta tattare rigarta ta wuce gaban Sif ta dauki Zani da panta kafin ta janyo qaramar Jakar da take zuba Yankunan da take amfani dasu saboda gudun datti ko qura ya tabasu ta dauki wanda zatayi amfani ta mayar ta rufe ta shige bandaki duk akan idon Maman Asad da Anty Hafsa. Jikinsu yayi sanyi qalau, Anty Hafsa ta tashi ta dauko jakar ta bude taga Tsummokaran da yawa ta kalli Hajiyayye tana cewa
"Yanzu da tsumma take amfani saboda Allah a gidan nan?"

Maman Asad ta sauke ajiyar zuciya ta miqe ta fice daga dakin itama ta maida mata da jakar tabi bayanta, a falo suka tarar da Mama na duba wasu Atamfofi da zata fitar duk suka zauna a sanyaye ta kallesu tana cewa
"Lafiya dai?"
"Babu komai" Maman Asa tayi saurin fada seta miqe ta dauki jakarta tana cewa
"Ina zuwa bari na karbo abu a bakin titi" ta fice.
Bata jima ba ta dawo da Babbar Leda ta shiga dakin Umaiman lokaci har tayi wanka ta shirya tana shan ruwan zafi, ta ajiye mata ledar tana cewa
"Gashi nan".
Umaimah ta kalli ledar ta kalli Maman Asad din seta ajiye kofin hannunta ta karba tana cewa
"Nagode, Allah saka da Alkhairi ya bar zumunchi"
"Amin" ta amsa mata kafin ta juya tavar dakin tausayin qanwar tata yana kamata.

Akan gado ta zazzage kayan, saitin man shafawa da sabulu ta gani Wanda ko ba'a fada ba masu tsada ne sanann zasu gyara fata, ga turaruka bodyspray, bodysplas da perfume harda oil Shampoo da condioner, Sabulan wanki da Omo Powder lip gloss, Harda su Eyeliner da Mascara ga Pad ta Virony me 32 guda hudu. Hawaye taji ya zubo mata data rasa na menene, ta sharesu kafin ta tattara kayan ta mayar cikin ledar ta zari Pad daya ta wuce bandaki, sedata gyara jikinta kafin ta dan fesa turare ta dauki ledar ta fita dakin Mama. A gabanta ta ajiye mata ledar tana cewa
"Maman Asad ce ta siyo mun"
"Allah ya saka mata da Alkhairi ya qara muku zumunchi" Maman ta fada ba tareda ta bude ledar ba, Anty Hafsa ta bude jakarta ta zaro dubu uku ta miqa mata tana cewa
"Wata yayi nisa idan munyi Albashi zan miki aike" ta karba tana godiya kafin ta miqe ta mayar da kayan.

Danwaken ta dora mata dan taji dama dama tayishi da dan yawa ko wani zeyi sha'awa aiko har Abba da ze fita sallar La'asar yaga tanayi yace zeci dan haka ta zuba masa ta kai masa bayan ya dawo. Se Magriba su Hajiyayye suka bar gidan, suna zaune da Mama bayan sallar isha suna kallo take ce mata
"Baki gaji da zaman gidan nan ba haka Umaimah? Ya kamata ki ringa fita kina ganin gari zaki rage wannan damuwar datake tsomareki ai".
Shiru tayi dan bata san me zata cewa Maman ba, ta fita kuma da izinin wa? Kuma ma ina zataje ita gaba daya ma bata sha'awar fitar, haka nan jikinta yake bata zamanta a gidan ya fiye mata Alkhairi yanzu tasan da yawa sun manta da ita duk ranar data fita aka fara ganinta kuwa labari ne ze dawo sabo, wanda bema san anyi ba yanzun ze sani.

Ganin tayi shiru yasa itama Maman bata sake ce mata komai ba, seda aka yi sati biyu a tsakani ranar Asabar bayan sun taso daga Islamiyyar da suke zuwa ita da Anty Umaimah na girki take ce mata
"An fara siyar da form na daukar sababbin dalibai, kiyiwa Abbanku magana a karbo miki ki ringa zuwa tunda wannan baqin ya fara washewa zaman ya isa haka"
Kallon kanta tayi, dagaskiyar Maman tunda ta fara wanka da Sabulu me kyau ta shafa mai me kyau ta washe, wannan uban baqin da tayi fatarta ta bushe har waskane tayi duk ya goge dukda bata koma Asalin kalarta na amma ta fara dawowa hayyacinta. Cikin In ina take cewa Maman
"Mama nayi masa magana kuma? Kin manta yace karna fita idan na gaya masa ze barni?"

"Ki tambaye shi mana idan ya hana srki haqura ki zauna kici gaba da girka tukunya" Maman ta bata amsa. Ta ringa juya maganar a ranta, ita kanta zata so ta koma Islamiyyar to amma bata so ta lalata shirin da suka fara da Abban in so samu ne zata cigaba da zama harse randa shi da kansa yace ta fita tunda ai yana sane bawai ya manta bane. Se washe gari Lahadi da Mama ta sake mata maganar cikin fushi tana cewa
"Dama ba karatun Addinin kikie so ba bayan harda rashin ratsa miki jiki da beyi ha yasa kika ringa tambele kina hauka a baya to se ki zauna ki qare rayuwarki babu wan babu qanin, keba aure ba keba neman ilimi ba bazan sake miki magana ba tunda baji kikeyi ba, dama na manta ne ai hali zanen dutse".

A daren ta samu Abba da zancen son shiga Islamiyyar, jikinta na rawa ga maganganun Mama ga tsoron yanda ze karbi maganar tata, ta sauke ajiyar zuciya ganin ya zaro dubu uku ya bata yana cewa
"Gashi nan ki bawa Antyn ku kamar haka tace mun kudin Hijabi da suka dinka kwanaki, idan na fita anjima zan karbo miki form din a Masallacin gurin Malam Babba, sauran Litattafai kuma seki duba anan duk ina dasu suna a nan suka samu". Ta ringa jera masa godiya kamar zatayi kuka kafin ta tashi har takai bakin qofa ya tsayar da ita, dakinsa ya fito ya miqa mata Wayarta da har ta manta da kalarta ma ita wlh.
"Gata nan, se ki siyi layi ki dora dan wancan qila sun siyar da number ko kinyi Welcome back bazeyi aiki ba".

Hannunta na rawa ta karbi wayar cike da Mamaki ta wuce falon Mama, seda ta fada mata yanda sukayi ta nuna mata wayar da kudin kafin ta wuce ta bawa Anty kudin Hijabin sannan ta shige dakinta tana juya wayar. Rasa ta inda zata fara amfani da ita tayi gaba daya se kawai ta ajiye, shekara biyar ba wasa ba, ta dai ganta da chaji full a ranta ta ringa mamaki tsahon lokacin kuma wayar batayi komai ba.
Seda yamma bayan Salman ya shigo gidan ta bashi yana murmushi yace
"Ni ya tambaya fa ya za'ayiwa waya karta lalace ai kuwa duk kwana biyu se Abba ya chaja wayar nan ba qaramin aiki kika bashi ba, ba yanda banyi dashi ba ya bani ita a lokacin ma in kin tashi amfani da ita na siya miki wata yaqi gashi ke kin manta ma yanda ake operating nata, kyanki Rakani kashi yanzu" ya fada yana gwada mata yanda zata yi amfani da wayar nan da nan ta tuno tunda daman ta sani mantawa tayi.

Shiya siyo mata layi yayi mata register sa dan da yace suje tare qi tayi, haka kawai take tsoron fita waje, bayan ta dora layi a wayar ta shiga duba numbobin kai duk sunanan babu abinda ya goge ta tsayar da idonta kan number Khalil qirjinta yana bugawa da qarfi tanajin kamar ta danna kira wani sashi na zuciyarta kuma yana hanatayin hakan, dakyar ta yaqi zuciyarta ta haqura da kiran, seta kashe wayar gaba daya ta ajiye ranta babu dadi abubuwan datayi qoqarin bunnewa suka fara dawo mata dalilin wayar nan, haka datazo bacci ta sake kunnata ta shiga hotuna ta ringa kallo lokaci daya hawaye ya shiga zubo mata data gaji da kallon hotunan ta ajiye wayar tasha kuka taqoshi kafin bacci yayi awon gaba da ita me cike da mafarkai kala kala. Kamar yanda Abba yayi Alqawari ya karbo mata form din amma ba kamar su Mama da suke zuwa sati sau biyu ba ita sau hudu ne litinin zuwa Alhamis qarfe goma zuwa daya na rana.

Ta ringa saqa da warwara akan yanda zata fara fita makarantar, to

*HALIN KISHI*

*NA MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*

*FIKRA WRITERS ASSOCIATON*
*(DON CIGABAN ADABIN HAUSA)*

Page 86

Ta ringa saqa da warwara akan yanda zata fara fita makarantar, da ranar tazo kuwa tun Asuba haka ta tashi da faduwar gaba, a sanyaye ta ringa ayyukanta. Tunanin yanda zata fuskanci mutanen unguwarsu kawai takeyi ta tabbatar ganinta seya maido da labarin baya amma ya zatayi? Ba zata cigaba da zama haka ba, dole ta fuskanci komai ta girbe shukar da ta dade tana yi. Qarfe tara da Rabi ta shirya tsaf cikin Hijabin Makarantar Ruwan Madara me haske, ta leqa Dakin Mama tana zaune a falo tace
"Har kin shirya?"
"Eh na shirya Mama" ta fada tana zama. Maman ta tura mata litattafan data ware mata wanda aka rubuto na Ajin da aka dauketa tana cewa
"Gasu nan toh, amma da kin jira Firdausi na aiketa ta siyo mun kati seta rakaki dan ba a inda kika sani ake makarantar yanzu ba"

Seta gyara zamanta ta zuba litattafan a jakar data sako Alqur'aninta, Firdausin ta shigo da aiken Mama ta karba tana gaya mata ta raka Umaiman makaranta tace toh. Harta miqe Mama ta tsayar da ita, dakinta ta shiga ta fito da baqar safa da niqab ta bata ta karba tana sakin boyayyar ajiyar zuciya. Tuntuni take shawarar neman niqab din amma tsoron kar Maman tace wani abu yasa ta haqura zata fita a haka. Dalilin Niqab din yasa ta ringa taka qafarta da kwarin guiwa har suka fita daga gidan. Seda ta tsaya tana kallon layin nasu kamar sabuwar baqauyiya. Kwalta har qofar gidansi dukda daman Hanya ce babba motoci nabi amma babu kwalta yanzu kuwa harda fitulun solar aka saka musu. Unguwar ta sake habaka sosai, shagunan data sani qanana duk sun bunqasa gidajen kansu wasu bata ma gane su ba saboda gyare gyaren da suka sha. Haka suka ringa tafiya tana kalle kalle kamar farin shiga birni, suka wuce tsohuwar Islamiyyar su wadda take hade da babban Masallacin unguwar suka qara tafiya kadan kafin suka isa sabon ginin makarantar qato hawa uku ga Ajujuqa birjik da ofisoshi.

Har gurin shugaban makarantar ta rakata, Umaimah ta daga Niqab din tana gaishe shi, kalolin iya shegen data ringa tsula masa na dawo mata a shekarun baya Yah Sheikh din ya zama babban mutum yanzu gemunsa duk furfura dukda be kai shekarun su Abba ba amma girman daya hau kansa ya qara masa kwarjini da haiba ake masa kallon Babban mutum sosai. Fuskar sa da walwala ya amsa gaisuwarta kafin ya kira wani Malami da baze wuce sa'an Salmab ba yace masa ga sabuwar dalibar Ajinsa. Ta kalli Malamin daman tun Asali abinda ya ringa hadata da makarantar kenan, Yah Sheikh baya dauko Malamai manya sedai ya debo qananan yara da acewarta basufi sa'anninsu ba suzo suna zare musu ido ku suce zasu dake su shiyasa ta raina Malam a wancan lokacin amma a yanzu cikin tsantsar ladabi ta gaida Malamin da aka ce na Ajin nasu. Yayi gaba yana cewa ta biyo shi, harta yunqura ta koma ta zauna, wannan dama ce ta samu da zata fara rage tarin haqqoqin Jama'a dake kanta.

Muryarta na rawa ta shiga roqon Yah Sheikh din gafara akan abubuwan data yi masa a baya, ya ajiye Takaddun da yake dubawa har sannan yana murmushi ya kalleta yace
"Haba Umaimah wace yafiya kuma kike nema a gurina ni ai bakiyi mun komai ba. Ko a baya nayi miki uzurin yarinta a duk abubuwan da kikeyi bani kadai ba duk sauran Malamaina bana zaton akwai wanda ya taba qullatar abinda kikayi masa a baya har yanzu duk kusan muna tare, a cikin Malaman ku Malam Sa'adu ne kadai Allah yayiwa rasuwa se Malam Lawi daya bar qasar yana Jami'atul Madina yanzu saura koda bama aiki tare suna yawan kawo mana ziyara har su bada darussa a wasu ranakun nasan wata rana zaki gansu. Ki saki ranki kinji kiyi abinda ya kawoki yawancin karatun Tishi ne akan abinda aka koya muku a baya kuma duk kin iya da an tuna miki zaki tashi se kiyi qoqari a wannan karon ba wai kiyi karatu kawai ba Aa ki maida hankali gurin fahimtar abinda kika koya tare da aiki dashi, Allah ya wuce gaba".

Jikinta a sanyaye ta fita bayan ta maida Niqab dinta. A waje ta taradda Malam Najib kamar yanda taji ya kirashi yana jiranta ya wuce gaba har Aji biyu inda aka sakata suka shiga tare ya nuna mata gurin zama cikin sauran Dalibai da sukayi shiru saboda shigowarsa. A sanyaye ta nemi guri ta zauna, murya babu Amo tayiwa wadanda ke kusa da ita sallama suka amsa suna kallonta. Malam Najib ya zauna a teburinsa ya dauko Register, seda ya kira suna kowa ta amsa wanda basu zoba ya saka musu kafin yayi gyaran murya yace
"Sabuwar Daliba menene sunanki?"

Gabanta ya fadi, dukda da Niqab a fuskarta seda ta zaro ido ta waiwaya kamar me ciwon wuya ta kalli Yan Ajin da suka zuro mata ido suna jiran amsarta a haka dai bataga fuskar sani ba duk cikinsu dukda dai ba wani kallonsu tayi dakyau ba. Seda ya sake maimaitawa kafin ta bude baki a hankali tace
"Umaimah Sabo"
"Masha Allah Malama Umaimah muna miki barka da zuwa" ya nuna wadda take kusa da ita yace
"Wannan Malama Aisha kenan itace Monitar ku, duk wani abu daya shige miki duhu ki tuntubeta, Daliban Ajin nan Dalibai ne masu hazaqa ina fatan kema

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login