Showing 276001 words to 279000 words out of 429394 words

Chapter 93 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

965

kanta sau biyu ta shigeta daga randa aka kawota se da zasu bikin wata qanwar qawarsu ita da Safina ta uzzura mata seta ari motar ta dauka a sace ba tareda ya saniba. A qalla kudin motar ya haura naira Miliyan Goma sha biyar dan sanda ya siyeta ba qaramin fada Hajiya tayi masa ba a cewarta almubazzaranci ne. Ba tareda tunanin komai ba ta matsa gefe inda aka saka musu rumfar shan iska da kujeru, duwatsu ne a gurin ta sunkuya ta tsinci manya da take ganin zasuyi mata aikin da take so tayi ta kwashe su da dama kafin ta durfafi motar. Seda ta cire rigar da aka rufeta da ita kafin taja da baya ta tsaya. Tunani tayi duwatsun bazasu mata aikin da take so ba ta zubar dasu a gurin, cikin gidan ta wuce kai tsaye ta shiga kitchen ta dakko qatuwar tabaryata dawo gurin motar babu tunanin komai ta fara takan glass din baya da yafi kowanne tsada, seda tayiwa gilasan motar rugurugu ta hada harda jikin qarfen motar ta lotsa inda zata iya kafin ta haqura ta yarda tabaryar a gurin tana haki kamar kamar wadda aka saka dole.

Ciki ta koma ta dakko muqullin tata motar ta fice daga gidan, kai tsaye gidan safina ta nufa tana da buqatar ta ba zata iya ita kadai ba dan ta tabbatar babu qarya a kalaman Khalil ita kuma tayi alqawarin bazasu tabbata ba.

CIKIN GIDA
Umaimah na barin Gidan Anty Amina da Jamila suka fito da shirin tafiya. A gigice Anty Aminan ta shiga kwalawa Sammani me gadi kira ya shigo compound din hankali tashe sedai abinda ya gani yasa ya gane dalilin kiran nan da nan ya tsure har ya fisu shiga rudani, Jamila ce tayi qarfin halin tambayarsa wayayi wannan aika aikar Sammani ya watsa hannaye sama yana rantsuwa yace
"Na rantse da kwarankwatsa Hajiya bam sani ba, tunda Alhaji ze fita ya aikeni can bayan layi gidan da akayi rasuwa ya bamu Buhun shinkafa da kudi yace mu kai musu, ina dawowa kuma na zauna a bakin qofa ko ciki ban shigo ba se yanzu".

Hannu kawai ta daga masa alamar yaje, Anty Aminan ta janyo waya zata kira Khalil Jamila ta hanata tace su koma gurin Hajiya. A falo suka tarar da ita tana waya suka zauna kowacce ranta a dagule har Hajiyan ta gama wayar, tana shirin yin magana Jalilah ta fito daga kitchen da farantin Indomin da ta saka Habiba ta dafa mata, kallonsu tayi ganin yanda sukayi wani sanyi se kace wanda aka fadawa Rasuwa ta ajiye farantin tana cewa
"Aa, ku kuma fa ya haka kun fita da fara'a kun dawo kamar Wanda akayiwa mutuwa?"

Anty Amina ce ta kalli Hajiya tace
"Hajiya, yanzu muna fita muka tarar da motar anyi anyi kwash kwatsa da gilasanta, na tambayi sammani yace besan wanene yayi ba"
"Wace motar?" Jalilah ta tambaya tana dafe qirji Jamila ta bata amsa da cewa
"Mercedes dinsa"
"Babu shakka labari yakai kunnen Umaimah, to wallahi Allah duk wata asara da tayi masa tamkar ta qara zugi ne da qara matso da lokacin auran nan, tunda ta riga taji kuma babu abinda za'a jira Hajiya ki kira su Baba Abu suje su nemo auran nan kuma ko yanzu ta kama a daurashi kawai idan yaso ta hadiye zuciya ta mutu qarewar fasa masa mota, kuma duk abinda ta lalata seta biya bazamu sake daukar Asara bisa ganganci ba" Jalilah ta fada tana huci yanda kasan motarta akace an lalata.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* =?L?
Page 63


UMAIMAH
Bayan fitarta gida kai tsaye gidan Safina ta wuce dan tana da buqatar abokin shawara akan ta inda zata bullowa lamarin. tana tafe a hanya kuka takeyi wiwi kamar wadda aka aikowa uwarta ta mutu, kalaman Khalil na mata yawo akai tana jinsu kamar wasu Allurai ne ake caka mata su a kwakwalwa a haka ta qarasa gidan tana shiga ta zube a falon Safina tana ci gaba da Kuka, Safina dake kwance kan kujera tana kallo ta miqe da sauri ta nufeta hankali tashe tana tambayarta lafiya amma Umaiman ta kasa ce mata komai se ihu take kamar wata zautacciya. Sda tayi me isarta ta samu sauqin abinda takeji kafin ta bude baki dakyar tace
"Safina na shiga uku na lalace dagaske Khalil aure zeyi har yana gaya mun rayuwata bata da muhimmanci a gurinsa yanzu dani ko babu baze chanza komai ba, ki taimakeni Safina zuciyata zata fashe" ta qarasa tana rushewa da wani sabon kukan.

Tsaki Safinan taja tareda komawa inda ta tashi tana kallon Umaimah dake kuka tamkar Mama ta mutu tace
"Amma wallahi kedai anyi banza yanzu daman saboda Namiji da wata kishiya da bata rigada ta shigo bama kikazo zaki saka jinina ya hau na zata ma wata mutuwar akayi miki, to uban me kike so yanzu ni nayi miki? Ina cewa kikayi zaki samarwa kanki mafita to yanzu basirar taki ce ta yanke da zaki sake dawomun kin wani kuka wiwi akan wani Khalil se kace da Gold akayi shi? Ki tafi inda za'a saka miki shi a kwalba se yanda kika yi dashi kin zauna kina batawa kanki lokaci kina zubar da mutunchinki a gari kowa yana miki kallon Mahaukaciya ina dalili, ni kinga bazan iya na ki dena zuwa kina raba baqin cikin ki dani bayan ga hanyar magancewa kin zauna taurin kai ke bazaki je ba".

"Ni na gaya miki ki bani wata shawarar banda ta zuwa gurin Malami dan ni bazan iya yawo kullum ina kaiwa qaton banza kudina yana cinyewa ba qila ma duk qarya ze ringa hadamun nazo nayi biyu babu" Umaiman ta fada tana goge fuskarta se Safina ta sake galla mata harara tace
"Ai idan baki kaiwa qaton banza yaci ba kyayita yawon Police station da kwanan Cell ko? Kinga nifa ban kiraki ba, shawara dai kike nema a gurina na baki kuma kince batayi miki ba dan haka kiyiwa Allah ki qyaleni nidai kiyi sabgarki ke kadai dan bana son abinda zesa kije kiyi wani cin kan sunana ya fito a ciki banji ba ban gani ba a zo a daureni. Duk ranar da kika shirya kika kuma yarda kizo na kaiki inda ko sunan Mace indai bake ba Khalil baze ambata a bakinsa ba. A kama miki shi a hannunki ba wani mugun abu zakiyi masa ba Kishiya ce bakya so shikenan a cire masa tunanin duk wata mace daga ransa se ke kadai ba shikenan ba meye wani abun zafi anan? Idan ma qyashin bada abin Sadakar kikeji muje ni zan biya miki kodan ki qylaleni na huta haka dan Allah".

Dukda bata so amma haka ta yarda da zuwa gurin Malam Sha yanzu magani yanzu saboda hujjojin da Safinan ta bata tana ganin zata iya amfani da hakan a matsayin matakin gaggawa na daqile abinda yake shirin faruwa kafin ta tsara gagarumin shirin a gaba, dan ita ba zata qarar da lokacinta da abinda ta tara a gurin Malamai ba. Babu bata lokaci Safinan ta shirya suka fita bayan ta kira Malamin nata ta sanar masa da zuwansu. Can wata unguwa sukaje a wajen gari.

Irin motocin da ta gani a qofar gidan Malamin ya bata Mamaki, haka a dakin da ake karbar lambar ganin Malam din Matane da Maza manya da kana ganinsu kasan sun kama qasa duk suke zazzaune suna jiran layi yazo kansu suga Malam din. Safina ce taje gurin wanda take bada lambar sukayi magana ta dawo inda take tace mata suje, wani daki qarami na daban suka shiga suka zauna ta kalli Safinan kafin tayi magana tace mata
"Kin san ni VIP ce tun kafin malam yayi suna a sanshi a duniya muke tare dashi. Asali malamin Kakarmune gashi anzo kaina nima ina cin gajiyarsa".

"Ikon Allah" Umaimah ta fada a ranta wato su Ahalinsu gaba daya sun maida bin malamai sana'a kenan tunda gashi har gado sukeyi toh Allah ya kyau. Suna nan zaune mamakin jama'ar data gani yasa ta manta ma da abinda ya fito da ita. Wato dagaske Safina take da tace duk macen data cika ta tumbatsa tana da Malami ko Bokan daya tsaya mata yanzu lalacewar harta wuce kan Mata harda Maza a yawo gidan Malamai to ita dai ba zata iya ba.

Tunawa tayi da maganar da Khalil ya gaya mata dazu da safen take zuciyarta ta dauki zafi hawaye ya kawo idonta, har ace an kai matsayin da Khalil zece koda ita ko babu ze iya rayuwa saboda ya samu wata? Wannan dalilin ne kadai yasa ta yarda da tayin safina kuma a shirye take data sabauta koma wacece take shirin kwace mata Miji, Khalil dinta dai bata da buqatar yin wani aiki akansa dan natane, ta sani itama me shirin shigar mata Hancin da Asiri ta neme shi dan haka zata kwato abinta kota halin qaqa kuma tana buqatar tayi hakan da sauri. Kallon Safinah dake faman danna waya tayi tace

"Nifa Safina zuciyata bata aminta da wannan abin ba kuma na tabbata koda anyi aikin baze yuwu ba tunda daman shi Asiri ai seka yarda dashi yake ci kuma ni kin san uzurina na sauri ne, kawai kinga ma fasa mu tafi zanje nayi duk me yuwuwa na samarwa kaina mafita iya wannan jiran banzan da mukeyi ya tabbatar mun bazan samu abinda nake buqata ba" Umaimah ta fada tana kallon Safina, murmushi Safina tayi tareda dafata tace

"Dadina dake Umaimah garaje wai me kike ci na baka na zuba ne? Wai bakiji sunan Malam bane? In kiyarsa fa sha yanzu magani yanzu ke dakanki ya kamata ki bada shaidar hakan tunda yayi mun kuma kin gani, duka dan jiran da zamuyi na minti nawa ne ko kuwa ke kinfi gane kje kiyi hauka ayita yawo dake a duniya ana surutu ki qarawa kanki baqin jini a gurin wanda kikeyi saboda shi din?
Ke yanzu baki ma tunanin abubuwan da kikayi a baya ne suka tunzurashi ga yin auran yanzu toh wallahi kika kuskura kika sake gwada wani shirmen na tabbatar ya sakeki ba wani abin wahala ze zamar masa ba tunda da bakinsa ya gaya miki yanzu bakya gabansa dake ko babu ke babu abinda ze fasayi to gara ki taimaki kanki kibi komai a sannu, ta qarqashin qasa ake yaqi yanzu ki koma gefe kisha kallo kina zaune zakiji zuwan da dawowar kuma babu wanda ze zargeki balle a sakaki a bakin duniya".

Janye hannunta da Safinan ta riqe tayi zatayi magana wani saurayi ya shigo dakin da suke zaune yace
"Hajiya Malam yace ku shiga bangaren Amarya ku jirashi daya sallami wadda take ciki ze shigo yanzu" yana gama fadar haka ya juya se Safina ta miqe ganin haka itama ta miqe tabi bayanta dukda zuciyarta cike take da wasi wasi. Cikin gidan Malam din suka shiga, part uku ne qerarru a ciki, kallo Umaimah tabi gidan dashi, Safina taja ta tana cewa
"Kinga badda kama ba?"
Ita dai tabita da "Uhm" a ranta tana sake qaryata aikin Malamin dan quru quru yanzu ta samu hujjar cewar dan damfarane. Yana can yana tatike masu dakon Asara ya danqara gida na gani na fada da kudin su yana shata musu qarairayi.

A falon Amaryar Malam din suka zauna, Umaimah dai se bin gurin take da kallo yanda ya gaji da haduwa abubuwan more rayuwa kuwa babu wanda babu a ciki. Seda me aikinta ta kawo musu ruwa da Lemo kafin ta fito, fara kyakykyawar yarinya da bazata haura shekara Ashirin ba da fara'arta suka gaisa da Safina wadda alamu ya nuna akwai sabo sosai a tsakaninsu kafin ta gaida Umaimah dake binta da kallo. Tashi tayi tace tana zuwa ta shige kitchen, Safina tayi qasa da murya tace
"Kin ganta yar qawar Hajiyarmu ce in gaya miki daga zuwa karban taimako wai Aljanu na damunta se ji mukayi wai Malam take so shi zata aura harfa an kawo mata kudin aure wani yaro dan masu kudi a gurinsa fa aka ringa aikin har suka shawo kan yaron ya fito za'ayi aure se gashi yarinyar nan ta dage se shi seda akayi auran nan yanzu watanta biyar kenan aiko uwar saboda Haushi tace ko cokali bazata siya mata ba yace babu komai saboda auran nata fa ya rushe gidan gaba daya ya tada wannan ginin kiga Aljannar duniyar daya zuba mata"

"Aikuwa taga taimako kinga an yi daidai kudin ku da kuke kawo masa dashi ya hada yayi mata kayan dakin da duk baku saka irinsu ba ma ai" Umaimah ta fada cikin gatsali. Sallamar Malam ta hana Safina bata amsa, Matashin Magidanci da baze wuce shekaru Arba'in da motsi ba ya shigo yasha Babbar Riga ta Shadda Getzner se maiqo take ga uban rawani ya kafa da zabgegen carbinsa a hannu. Ya washe baki yana yi musu sannu da zuwa Safina ke amsa masa Umaimah dai tunda ta gaidashi sau daya ta sake fuska dan ganinsa ya sake saka ta qin yarda da lamarin Na Safina. Wannan ne Malamin da take zuzutawa ta tabbata dai dan 419 ne shima yake kwasar rabonsa kawai.

"Hajiya Safina idonki kenan, ai nace tunda kin samu kan Yallabai an dena jinki" Malamin ya fada se Safina tayi dariya tace
"Ba haka bane Malam, kwana biyun ne ban fiya zama ba wlh amma ina nan zanyi zuwa na musamman, yanzu ma qawata na rako, abu ne ya taso mata Urgent shine nace bari na rakota inda za'a share mata hawaye".

"To to menene matsalar? Ko da yake ina zuwa" Malam ya fada kafin ya miqe ya shiga wani daki dake cikin falon. Amarya ta dawo me aiki na biye da ita da Qaton Try da ta doro kulolin abinci ta ajiye musu Safina tayi mata sannu ita dai Umaimah binta kawai take da kallo harta wuce ta koma dakinta. Minti kusan biyar Malam ya dawo da wata qaramar Jaka ya shimfida buzu a qasa ya zauna ya bude jakar ya ciro qaramin carbi da wasu kwalaben turare. Seda ya gama shafe carbin da turaren yana mammotsa baki kafinya kalli Umaimah yace
"Bismillah"
Kallon Safina tayi da rashin fahimta se tace mata
"Ki matsa kusa yake nufi".
Muskutawa tayi gefe tana sake kallon bakin Malamin dake ta motsi seya miqo mata carbin hannunsa yace ta zabi guda uku ta zaba seda suka maimaita sau uku kafin yaci gaba da jan carbin yana muimui da baki. Shiru gurin ya dauka Malam nata juya carbi yana girgiza kai daga qarshe ya ajiye yana kallon Umaimah da Safina da suka zura masa iso suna kallonsa yace

"Maganar gaskiya akwai Matsala babba".
A tare suka gwale ido suna kallonsa, Safina data dafe qirji tace
"Matsala wace iri malam?" Seya karkace ya gyara zama yace
"Mijinki ya fada soyayya da wata yarinya kuma munga akwai qauna a zuciyarsa hakan yana nufin aure kenan"

"Toh Malam ai munsan da wannan dalilin daya kawo mu kenan muke so a dakatar da auran" Safina ta fada seya sake jan carbi ya hau irga kusan minti biyar kafin ya sake kallon Umaimah yace
"Maganar Gaskiya Hajiya naga aure sedai lokacin yinsa ne ban sani ba, sannan akwai mutuwa kuma akwai mutuwar aure duka gaba daya amma zamu iya shawo kan matsalar gaba daya in Allah yaso"

"Kaga Malam ka tafi kai tsaye ka gaya mana abinda ka gani ba wani magana a duqunqune ba, nifa daman shi yasa na gaya miki bazanzo ba, akan me mutum be gama da tashin hankalin da yake ciki ba za'a qara kawo masa wani? Mutuwa daman dole ka ganta dan koma wacece take shirin shiga sabgar Mijina Ajalinta ta siya mutuwar aure kuma ka ganta a gidanka. Ni kinga tafiyata da nasan batamun lokaci zaki saka ayi wlh da ban biyo ki ba" Umaimah ta fada a fusace tana miqewa tsaye, riqeta Safina da hankalinta yafi na Umaiman tashi tayi tana kallonta tace

"Umaimah ki nutsu ki fahimci abinda yake fada, kin rigada kinji matsala s ki jira kiji yanda za'a maganceta"
"Karki rainamun hankali mana Safina, Mutuwar ze hana faruwarta ko auran wanne yake da ikon dakatarwa a ciki? Kinga karki qara batamun rai ki barni na tafi naje nayi wadda zata fishsheni kedai da kikaga zaki iya seki zauna yayi ta karanta miki qanzon kurege" ta fada tana fincikewa se Safina ta sake riqeta, miqewa Malam yayi yana kallonsu yace
"Bari naje, idan ta shirya kya yimun magana na bar mutane suna jirana a waje"

"Aa kayi haquri dan Allah Malam, wallahi damuwar da take ciki ce tayi mata yawa har ta fara taba tunaninta amma tana da buqatar taimakonka matuqa wallahi. Ka taimaka mana duk abinda ya dace ayi dan hana faruwar auran nan kayi shi kawai Malam" Safina ta fada se Malam yace

"Toh Hajiya naga wadda take da damuwar nan tace bata da buqatar aiki ke menene naki a ciki ne ki barta kawai taje, nidai na gaya miki akwai aure, akwai mutuwar aure sanann akwai mutuwa duk kuma inda zakije kije nasan bazakiji sabanin wannan binciken ba".

Yanda kasan wanda aka zarewa Laka haka Umaimah ta bishi da kallo ta kasa motsawa ta tafi daga gurin kamar yanda tayi niyya.
"zauna" Safina ta fada tana kama hannunta seta zauna kuwa babu musu zuciyarta tana wani irin bugu na tsoro data rasa tsoron menene.

"Yanzu Malam ya za'ayi a shawo kan matsalar nan" Safina ta fada bayan da Malam din shima ya koma ya zauna yana wani munafikin murmushi da suka rasa na menene. Carbinsa ya sake dauka yaci gaba da motsa baki Umaimah ta zura masa ido kamar me son gane abinda yake fada ya gama surutunsa ya watsa carbin yace ta dauka jiki babu laka ta dauka ta miqa masa ya karba yaci gaba da ja zuwa can ya kalleta yace
"Da akwai aikin da zamuyi wanda ze iya dakatar da auran amma fa se kin bada hadin kai tukunna"
Shiru tayi bata ce komai ba dan haka yaci gaba da cewa
"Kusan ke zakiyi aikin ma da kanki nawa kawai tallafine na makamai da zasu taimaka miki amma fa kibi a sannu".

Nan ma shirun tayi se Safina ce tace
"Zatayi duk yanda aka ce Malam babu matsala in sha Allahu". Miqewa yayi ya

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login