Showing 414001 words to 417000 words out of 429394 words

Chapter 139 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

987

da Rashawa amma suna aikatawa ya ringa dariya kawai, washe gari kuwa da sassafe yazo suka tafi Asibitin dan jirgin yamma zebi ya tafi Abuja.

Seda gabanta ya fadi da taga Asibitin da sukaje, Asibitin Dr Al'amin inda suke zuwa a gidan Khalil. Seda ya biya kudin duka gwaje gwajen da za'ayi musu, tana jinsa yana waya da wani likita da yace Abokinsa ne ya sanar masa baya Asibitin amma kafin su gama ze shigo.

A office din Abokin nasa suka zauna bayan an dauki Jininsu, Abokin ya ringa kallonta, ita dai ba ta sanshi ba dan ko lokacin da take zuwa ba zaton suntaba haduwa gaba daya ma tunda sukaje Wata Nurse daya ta gani data sani a gurin duk sun canza ma'aikata amma shi wannan se wani kallon qurilla yake mata ya tambayi sunanta kuwa yayi sau uku harda wani gayyato wani Likita wai su gaisa da Abokinsa da Amaryarsu shima ya tasata a gaba yana kallo har seda ta tsargu ta ringa duba jikinta ko akwai abinda ta saka da ya ja suke kallo ta amma taga babu, Hijab ne dogo har qasa ta dora akan doguwar Rigar Atamfar data saka qafarta ta saka safa fuskarta da hannunta ne kadai a bude to me suke kallo a jikinta? A haka dai aka kawo musu sakamakon Gwajin komai yayi daidai sukayi sallama da Dr da daya Abokin gulmar da ya kirawo suka kama hanyar gida. Seda suka tsaya yayi mata siyayya sosai dukda tace bata so ya barshi amma ya kafe har yana cewa ai yanzu ta zama responsibility dinsa dole yayi mata.

Be zauna ba yana sauketa ya tafi saboda be qarasa shirin tafiya ha kuma sun bata lokaci a Asibitin, ta shiga gida da tulin siyayyar da yayi mata da kuma sakamakon gwajin da sukayi, ta rigada ta makara itama dole ta haqura da fita aiki dan haka ta shige daki ta kwanta dan ta dan yi bacci kafin lokacin dora Abinci yayi.

Abdulwahab ya isa gidansa ya tarar da matarsa Khadija cikin damuwar da tunda ta dawo daga gidansu jiya ya ganta a ciki. Dare yayi sanda ya dakkota dan haka be tsaya ya fahinci maganar da tazo masa da itan ba. Tana zaune akam gado inda ya fita ya barta ya sake tarar da ita da alama ma kuka tayi ya matsa kusa da ita yana taba wuyanta yace
"Wai Dija baki da lafiya ne? Tun Jiya na lura dake gaba daya baki da walwala tunda kika dawo daga Sallari ko wani abun ne ya faru acan?"

*HALIN KISHI*

*NA MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*

*FIKRA WRITERS ASSOCIATON*
*(DON CIGABAN ADABIN HAUSA)*

Page 88

A maimakon ta bashi amsa seta fashe masa da kuka tana cewa
"Nidai Abban Fahimah maganar auranka, ban hanaka ba amma dan Allah banda ita ka auri koma wacecena yarda amma banda wannan Umaiman".
Sakinta yayi ya miqe yana mata wani kallo kafin ya dauke kansa yana cewa
"Kar muyi haka dake Dija, karki lalata mana farincikin mu muna zaman lafiya kin karbi maganar nan seda abu yazo gab zaki tayar da hankali, duk wanda ma ya zigaki yace kizo ki tayar mun da hankali I'm sorry to say ke zasu cuta dan ni babu abinda ze saka na canza ra'ayi tunda tuntuni munti ta da wajewa babu yanda za'ayi yanzu kuma kizo mun da wata magana gara ma ki sanyaya zuciyarki, gobe za'a kai kudi na gaya miki kuma sati takwas za'a saka" yana gama fada ya shiga zuba kayansa a akwati ganin bata hada masa ba dan ita take shirya masa kayan.

Kuka ta ringayi duk yanda tayi qoqarin fahimtar dashi akan wacece Umaiman yayi biris yaqi fahimtarta, data ishe shi da cewar Kishine na bala'i da Umaiman yace mata ya sani, babu abinda ta boye masa kuma a hakan yaji ya gani ze aureta ya kwashi kayansa ya bar mata dakin dan gani yakeyi kawai taje gidansu ne sun zugota zata zo ta fara masa wani koke kokeb banza bayan komai da saninta kuma da yardarta yakeyi, daman yasan babu yanda za'ayi salin alin ayiwa mace kishiya ba tareda tayi tashin hankali ba. Saboda kukan nata da wuri ya bar mata gidan bayan ya jaddada mata aure babu fashi gara ma ta saki ranta taci gaba da sabgoginta kishiyar da ba gari daya ma zasu zauna ba to me ze dameta.

Ita kuwa Khadija tashin hankalin data shiga bayan jiya taje gida yayarta Ummia dake zaman gida take sake tambayarta wadda Abban Fahiman ze aura dan tunda ta gaya mata sunan Yarinyar take tunanin kamar ta santa bata haqura ba kuwa seda ta binciko inda tasan Umaiman. Ta nunawa Khadijan hotonta tace tabbas itace. A tsakar gida ta zauna ta ringa basu labarin Umaimah da tijararta tun suna poly ta santa dan sun taba hada saurayi ma a lokacin da ta gano ta hada ita da saurayin tayi musu Tijara a Lecture hall ta dire tana basu labarin Upgraded haukan Umaimah da irin ta'asar da tayi aka sakota shekara bakwai kenan tana zawarci.

Hankalin Khadija ya tashi matuqa dan ita irin mutanen nan ce da basa son damuwa, tun a daren taso Mijin nata ya saurareta amma yaqi, gashi yanzun ma yayi tafiyarsa har yana cewa yasan komai. Bata yarda da wannan ba dan a sanin da ta masa ko a social media ya jiyo labarin irin mata masu bala'in kishin nan sunyi abu ya ringa jimami kenan yana cewa ai babu dole a auransu baze dakko matar da zata zamar masa fitina kota lahantashi ba ta tabbatar yanda yake jida Injinsa idan yaji ta lahanta na wani babu abinda ze saka ya yarda ya aureta. Tunanin wanda zata gayawa maganar nan ya fahimceta ta shigayi qarshe ta yanke shawarar zuwa gidan Yayarsa ta gaya mata, ita ba ta kanta take ba Jihadi zatayo ta tabbata ko masifar ta tashi sakkowa kansa zata fara ruftawa kafin ita tunda shi ya kwasota can zata kashe shi a Abuja ta cuceta ta barta da marayun Yaya.

Abdulwahab din na fita itama tayi wanka ta tafi gidan Yaya Suwaiba babbar Yayarsu Abdul din. Tana kuka ta gama zayyana mata komai dataji, Yaya Suwaiba tayi shiru tana jinta seda ta kai qarshe kafin ta sauke ajiyar zuciya tace
"Yanzu ke Khadija ina kika jiyo wannan maganar kuma kin tabbatar da sahihancinta?"
"A gurin Yaya Ummi, ta santa tare sukayi makaranta kuma shima dana fada masa cewa yayi yasan komai kuma a hakan ze aureta" Khadijan ta sake fada tana share hawaye se Yaya Suwaiba ta gyara zama tace

"Toh nidai abinda zan fara ce miki shine kiyi haquri ki kuma bi komai a sannu. Kinsan namiji idan zeyi aure bayaji baya gani ke kuma duk abinda zaki fada yanzu za'a dauke shi a matsayin kishi kawai kuma tunda kince yasan komai kenan ba'a rufeshi ba kuma a hakan yaji ya gani ze aureta ke meye naki a ciki to tunda ma ba gari daya zaku zauna ba duk abinta ai iyakar kansa can zata tsaya ko?"

"Wlh Aa Yaya Suwaiba dan bakiji labarinta bane shiyasa kike fadar haka. Ni ba kishi nakeyi ba hasalima da yardata ze qara aure amma ni ita wannan dince kawai bana so ya nemo wata ya aura amma banda ita" Khadija ta fada tana kuka, rarrashinta Yaya Suwaiban tayi tareda yi mata alqawarin zata kira Abdulwahab tayi masa magana sannan tace mata itama tayi haquri taci gaba da addu'a idan da Alkhairi a abin Allah ya zaunar dasu lafiya in anyi idan kuma babu Allah ya watsa al'amarin salin alin ba tareda bacin rai ba. Haka ta koma gida hankalinta ya gaza kwanciya. Harga Allah ita auransa be dameta ba wadda ze auro matan ce tashin hankalinta dan ta tsorata da labarin Umaimah dataji ita bata son damuwa a rayuwarta tana zaune lafiya baza'a dakko mata wadda zata tayar mata da hankali ba.

Yaya Suwaiba kuwa kamar yanda ta mata alqawari ta kira qaninta ta gaya masa yanda sukayi da Khadijan, kai tsaye yace mata
"Yaya ki rabu da ita bafa ita zata zauna mun da mata ba bare ta zabar mun wadda zan aura. Kawai halinku ne Mata da daman bakwa rasa qirqiro tashin hankali da zarar ance za'a kawo muku wata cikin gida na tabbatar ko ba Umaimah ba duk wadda ma na ce zan aura seta san abinda zata bullo dashi dan na fasa to plan dinta beyi aiki ba dan kafin tasan wacece Umaiman na rigata sani aure kuma babu fashi dan yanzu haka ma nasan su kawu na hanyar dawowa gida dan tun dazu sukaje kai sadaki" Yaya Suwaiba ta rasa abin ce masa, ta wani fannin yana da gaskiya ko Khadija bata fito ta nuna ba kowa yasan dole tana kishin Mijinta kuma zata iya riqar duk hujjar data samu dan ta kauda maganar auran amma kuma itama zancenta abin dubawa ne a irin yanda tace ta jiyo labarin Amaryar da abinda ya kashe mata aure to amma tunda ma'auri yaji ya gani su meye nasu ciki banda suyi fatan Alkhairi.

Da taje gidansu ma tayiwa Hajiyarsu magana tana farawa ta katseta bata ma saurara taji qarshen bayanin ba tace babu ruwanta. Duk iyakar bincike Alhaji yayi yasan uban yarinyar nan basuda wani abin Ashasha tsatsonsu tsatsone me kyau da kowq zeso hada zuri'a dasu kuma magana ma ta qare tunda har an kai Sadaki an tsayar da ranar aure dan haka ta gayawa Khadijan idan zata kwantar da hankalinta ma tun wuri gara ta kwantar dan kishiya da kudinta ta siyota tunda tace ba zata bishi inda yake aiki ba ko bata da hurumi cikin maganar auransa daga haka zance ya mutu.
A bangaren Amarya kuwa shiri sukeyi babu kama qafar yaro, dukda ita a sanyaye take komai. Gani takeyi kamar bada gaske ba wai zatayi aure ta rayu da wani Namiji daban ba Khalil ba se taga abin kamar mafarki da zata iya farkawa a kowanne lokaci taga ba gaskiya bane.

Miliyan daya ya bata kudin lefe, Maman Asad tace ya turawa daman suka hada da tanadinta da kudin auran suka fara shirinsu dan bata da ko cokali na kaiwa daki kuma Abba bece musu komai ba haka Mama dan haka suka fara siyan abinda ya samu tunda bikin da saura kusan sati bakwai kafin nan dai dolr zasu magantu tunda dai ai ba zasu kaita babu kayan daki ba. Wani weekend su Bibi sukaje a nan suka samu labarin auran da Momyn nasu zatayi, Bibi ta fasa kuka, Mu'ayyad kansa da ba zatace ga alqibilarsa akan rabuqarta da Mahaifinsu ba ranar seda idonsa da jikinsa suka nuna rashin Jin dadin Al'amarin. Yayi shiru yana kallon Bibi dake rusa kuka kamar ance mata an saka ranar sarewa Umaiman kaine, a hankali cikin nutsuwarsa irin ta mahaifibsa ya kallu Umaiman yace

"Momy bazaki haqura ki dawo gidanmu ba?" Ta zura masa ido na wani lokaci, shekarunsa goma sha hudu yana shirin cika ta sha biyar. Yana da nutsuwa da kaifin tunani da basira ta tabbatar da cewar koda ace sanda ta rabu da Khalil akwai yarinta a tattare dashi amma zuwa yanzu kwakwalwarsa ta gane komai daya faru dan haka boye masa ko bagarar da zancen babu abinda ya canza. Seta gyara zama ta kalli Bibi dake gamsheqar kuka tace
"Ko kiyi shiru ko ki fita ki bamu guri". kukan ta rage dan yanzu ta fara kintsuwa tana jin magana shagwaba dai da sangarta wannan sedai idan bata samu dama ba dan yanda uban yake lelenta daukar kanta takeyi kamar wata Jiddah jaririyar wanwarsu. Umaimah ta kalli Mu'ayyad daya sunkuyar dakai qasa tun bayan da yayi mata magana tace
"Mu'ayyad bani zanyi haquri ba, Dadynku nayiwa laifi shiya kamata yayi haquri ya yafemun ko badan na dawo gidanku naci gaba da zama ba Aa ina buqatar ya yafemun duk abubuwan da suka faru a baya tsakaninmu. Ina so na bashi haquri amma na rasa ta hanyar da zanbi ya saurareni, idan na kirashi a waya bata shiga kullum sena tura masa da Text na ban haquri sama da shekara amma be taba maidamun da martani ba. Bana so na sakaku a ciki na qarawa kaina laifi a gurinsa amma inaga ta hakan ne kadai zan samu afuwa da sassauci a gurinsa. Idan ka koma gida yau ka tayani roqonsa kace masa ko minti daya ne ya bani dama na nemi yafiyarsa kota wayane ko bazece mun komai ba ya amsa wayata kawai hakan ma ya isheni".
Shiru yayi yana kallonta kafin ya sauke ajiyar zuciya yace
"Idan ya haqura zaki dawo toh?" Bibi ta fada cikin kuka har sannan seta jata jikinta tana cewa
"Ban sani ba Bibi, duk abinda Allah ya tsara mana ina fatan ya zama mana Alkhairi gaba daya a rayuwarmu. Koda ace na auri wani babu abinda ze canza zaku cigaba da rayuwa cikin walwala kamar yanda kukeyi yanzu kuma zaku cigaba da zuwa gurina ko?"

"Nidai Momy kawai ki dawo gidanmu, shikenan mu se mu tashi Mamanmu da Babanmu basa tare nidai wlh kawai ki dawo" Bibin ta sake fashewa da kuka se Umaimah tayi murmushi tana janyeta daga jikinta tace
"Ke ai matsalar kina girma amma tunaninki na nan kamar na yar baby, to idan kuma mutuwa nayi fa gana daya ya zakuyi?"
"Toh Momy mutuwa ai daban munsan ba zaki dawo ba yanzu kuwa kina da rai. Wlh Dady yana sonki, ko jiya seda naga yana kallon hotonki ni nasan daman kece bakyaso ki koma gidanmu. Momy indai saboda Mamah ne bata da matsala, tana da kirki zaku zauna lafiya da ita dan Allah indai Dady yace ki dawo ki yarda kawai kinji" Mu'ayyad ya sake fada kamar shima ze saka mata kukan. Qirjinta ya ringa bugawa da qarfi jin da tayi yace wai Khalil yana sonta har yana kallon hotonta koda yake ba abin mamaki bane ta sani Khalil na sonta kamar yanda itama take Sonsa amma babu yanda suka iya da qaddara haka Allah ya nufa a tsakaninsu kuma itace sila.
Be sake cewa komai ba itama tayi shiru, haka suka qarasa wunin ranar babu dadi. Zancen auran nata ya cirewa yaran karsashi ita kuma maganganunsu suka sake jefata a dimuwa suka qara sanyaya mata jiki matuqa. Suma gani sukeyi itace bata son zaman lafiya kuma taqi komawa gidansu ne saboda matar Babansu. Abinda ya qara sanyaya mata jiki qalau yanda Iman ko a qafarta zancen auran be shafeta ba uzurin gabata kawai ta ringayi. Daman haka take ita, babu wata shaquwa a tsakaninsu yanda take mu'amalantarta babu alamar ta dauketa matsayin uwa mahaifiya maganarta kullum Mamah kaza Mamah tayi kaza. Da akazo daukarsu kafin su tafi seda ta sake jaddadawa Mu'ayyad kan ya hadata da Dadyn nasu, tana matuqar son magana da Khalil din, bata so ta shiga sabuwar rayuwa da dakon haqqinsa ita ta sani ba zata samu nutsuwar da take fata ba.
A daren ranar suna komawa gida Bibi bata iya jiran Khalil ya dawo gida ba ta dauki wayar Humaira ta kirashi dan tasan be zama lallai Yayannata ya fada masa saqon Momy ba.

KHALIL
Yana office yana qarasa wasu ayyuka besan magriba tayi ba seda kiran wayar ya shiga ya daga yaga lokaci, cikin muryar gajiya yayi sallama tare da ce mata
"Afuwan Love, aikine ya riqeni amma gani nan tahowa yanzu in Allah ya yarda duk kewar tawace tasa kika kasa haqurin jira?"

"Dady nice" muryar Bibi ta katseshi, seya dafe kansa, Allah yaso ba qata baranbaramar yayi ba. Cire wayar yayi da kunnensa yana qarasa hade takaddun gabansa dan yasan wayar Bibi ba qarewa take ba baze wuce qorafi bane an mata wani abun ba zata iya jiransa ya dawo ba zata kira a waya dan haka yace mata
"Meya faru sweetheart har kun dawo daga gurin Momyn taku ne?" Kamar tana jira kawai tasa masa kuka,da sauri ya aje takaddun hannunsa ya dauki wayar ya mayar kunnensa, yanda take kukan harda shashsheqa ya bala'in daga masa hankali take ya fara hasashe hasashen meya faru?

"Kiyi shiru gani nan zuwa gidan ok" yana gama fada ya kashe wayar ya zirata a Aljihu ya dauki abinda yake buqata badan ya gama aikin gabansa ba ya tafi gidan. A waje ma ya ajiye motar ya taka da qafa yana shiga ya tarar da Mu'ayyad zaune bakin qofar shiga falonsu ya rafka tagumi a fuskarsa zaka karanci damuwa sosai gabansa ya sake yankewa ya fadi, to meya faru ne? Mu'ayyad dinna ganinsa ya miqe tsaye amma ya kasa yin magana Khalil ya matsa kusa dashi ya kama hannunsa yana cewa
"Wai meya same ku? wani abu akayi a can gidan ne?"

"Dady.." Mu'ayyad din ya kira sunansa se kuma ya sunkuyar da kansa qasa ya kasa cigaba da magana Khalil ya zuba masa ido yana karantarsa, Mu'ayyad yarone me shiru shiru sosai sam bashida hayaniya ko kadan halinsa sak na takwaransa Mahaifinsu yana kuma da qoqarin shanye damuwa da wuya kaga ya furta fushi ko ya nuna a fuskarsa dan haka yasan yanzun dole da akwai wani abun daya faru.
"Ina Bibi?" Ya tambayeshi swya bude baki kamar baya so yace
"Tana ciki, kuka takeyi tun dazu taqi tayi shiru".
"Me akayi mata take kuka kai kuma meya bata maka rai?" Khalil din ya sake jefa masa wata tambayar aeya kuma sunkuyar da kansa kafin ya dago kamar an fizgo maganar daga bakinsa yace
"Momy ce zatayi aure, saura 4 weeks".

Yanda kasan wanda ya harba da bindiga haka yaji har seda ya saka hannu ya dafe qirjinsa da yaji tamkar ze fado saboda razana da zancen Mu'ayyad din.
"Aure" ya maimaita kalmar a fili Mu'ayyad ya daga masa kai kafin ya qara da cewa
"Tace na roqeka ka amsa wayarta ko minti daya ne ka bata tana so kuyi magana". Tabbas yaji abinda yaron yake cewa amma kwakwalwarsa bata iya fassara masa ba, se kawai ya tura qofar ya shiga yana tafiya kamar wanda ya fito daga sahara saboda yanda wata irin kasala take bin qabobinsa tana riqe su.
Humaira na tsaye gaban Dining tana gyara kwanuka yanda ya bude qofar yasa ta waiwaya ta kalleshi, daman tasan duk inda yake dole yana hanya tunda an taba yar gwal. Yanda taga fuskarsa da yanayin sanyin jikinsa yasa ta ajiye abinda takeyi ta nufeshi tana cewa

"Lafiya kuwa?" Tayi saurin tareshi saboda tuntuben da yayi da jirgin Adil ya tafi

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login