Showing 30001 words to 33000 words out of 429394 words

Chapter 11 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

933

Ya fada a fusace yana kallon yanda kan ko wacce yayi buzubuzu kamar sababbin kamu se sosa inda ya tsula musu bulala suke, jikin bango suka maqale kowa tana sosa jiki, ya sake kallon Nuratu yace
"Harda ke ina miki kallon me hankali ashe zama da ita yasa kema kin koyi hauka ko? Uban me ya hada ku fada?" Ya daka mata tsawa, se Umaimah ta fashe da kuka tace

"Wallahi Yaya babu abinda nayi mata kawai ta hau ni da duka..." Bulalar ya kai mata duka da ita tayi azamar gocewa ta fada dakinsu da gudu tana masa Allah ya isa a zuciya. Kan Nuratu ya juya ya shiga surfa mata masifa uffan batace ba har yayi shiru dan kansa kafin ta miqe ta shige dakin Mama dan tasan idan ta shiga nasu Umaimah na ciki tabbas fada be qare ba shi kuwa Yaya Aminu samun su zeyi kamar jakai ya lafta.

Baafi minti sha biyar ba kuwa su Maman suka dawo, Aminu ne ya fada musu abinda yazo ya tarar se a sannan Salil ya fito daga daki yace "Umaimah ce da laifi dan ta riga Yaya Nuratu shigowa ta labe a bakin qofa se ji nayi sun kaure da dambe".

"Ai ko baka fada ba daman nasan itace da tsokana amma itama Nuratu da laifinta akan me zata biye mata har suyi dambe se kace wasu qananan yara" Maman ta fada.

"Ki qyale su Allah ya taimaki wata yarinya ta sake mana dambe a gida wallahi se jikinta ya gaya mata dan se nayiwa mutum mugun duka a gidannan" Aminu ya fada, daki Mama ta wuce yabi bayanta bayan sun gaisa da Anty.

Nuratu na ganin Maman ta saka kuka, babu bata lokaci ta zayyane mata duk yanda akayi a Asibiti da abinda Khalil ya gaya mata a hanya harda dalilin yin damben nasu.
"Ai shikenan" Mama data gama saurarenta ta fada tana miqewa tsaye, Allah kadai yasan abinda taji a zuciyarta se kuma wanda Ubangiji ya jarabta da fitinanniyar yarinya irin tata.

"Ai kuwa sena ci ubanta yau a gidan nan, kuma bata isa ba a wannan karon ta sake lalata magana tunda naga abinnata ya zamana tsantsar iskanci tana da buqatar a dawo da ita kan hanya" Aminu ya fada afusace yana miqewa shima se Mama tayi saurin dakatar dashi da cewa

"Karka kuskura ka taba ta, baka ji abinda akace bane shima yaron yace ya fasa toh ka barta zaman gidan nan ne ko gata gashinan. Kuma kar naji zancen a bakin wani koda mahaifin ku ne kuwa, idan sunzo da kansu sun janye a lokacin ya sani. Amma Umaimah koh idan har ta bata wannan auran bazata maida kamarsa ba" ta qarasa maganar cikin rawar murya tareda daga kanta sama a qoqarin ta na dakatar da hawayenta daga zubowa dan daman daga yanayin muryarta suka gane kuka ne yake neman zuwar mata abinda ya qara sanyayawa Aminu da Nuratu jiki.

"Dan Allah Mama karkiyi kuka, kin sani hawayen ki masifa ne a tattare da ita addu'ar dai ita zaki ci gaba dayi mata in sha Allahu wata rana se labari" Aminu ya fada sedai kamar me jira kuwa kukan ya kwace mata tace
"Na gaji, nagaji Aminu da halin qanwarku. Kullun ta Allah da zullumin ta nake kwana nake tashi a raina, yanzu idan aka fasa auran nan karo na hudu fa kenan me kake zato mutane zace a kanta? Ni kadai nasan irin qunci da baqin cikin nake fama dashi akan lamarin auranta yanzu ina murna yan satittika suka rage ta tafi shine ta ja gwalo abinda ze saka a fasa ko ai shikenan" tana gama fada ta shige daki tana ci gaba da matsar hawaye.

Nuratu dake nata hawayen a zuciyarta tana dana sanin sanarwa da Maman, amma tasan dole zata ji, kuma ita a nata dabarar ta fada mata da wuri ne saboda idan da yanda zaayiwa tufkar hanci ayi se gashi ta sake lalata al'amarin.

"Indai junin mutum munafunci dason ya hadani da uwata sedai abinsa ya qare masa in sha Allahu badai aga bayana ba sedai mutum yaga nasa, kuma aure na babu fashi duk baqin cikin mutum" Umaimah da basu san da tsayuwarta ba ta fada tana jijjiga jiki irin na tsabar fitsara da rashin kunya, Aminu ne ya yunqura kafin ya tarar da ita ta kwas ada gudu ta koma dakinsu harda sakawa qofa sakata dan tasan a yanda ya zaburo tabbas ya riqeta toh ko be kasheta ba se tayi dogon Suma.

Zama tayi akan gadonta gaba daya kuma seta rasa sukuni, hawayen da ta gani a fuskar Mama sun daga mata hankali dan ita ba jahila bace ba kuma mahaukaciya bace tasan illar da hakan ze yi mata wai me yasa a kullum itace sanadin Kukan Mama?
Bama ita kadai ba duk wanda ya tashi qorafi a gidan akanta ta fita zakka a cikin su goma sha uku da aka haifa a gidan.

Iya qoqari kuma tanayi gurin kaucewa duk abinda zaace tayi ba daidai ba amma sau tari ma tsokanarya akeyi idan ta maida martani kuma ace tayi laifi, ko kuma su dauki damuwar data shafeta su dorawa kansu kamar yanzu da wannan munafukar Yaya Nuratu taje ta fadi qarya da gaskiya ita sam bataga abin tayar da hankali a ciki ba. Aure ita ce me auren nan ko maza ashirin suka fasa auranta mijin tane bezo ba hakan kuma baze hana shi zuwa ba sannan maganar Khalil da tace ta fasa wasa takeyi bacin raine kawai yasa shima kuma tasan haka ne idan an barsu daga nan zuwa dare ma zasu shirya kansu amma shine Mama zata dauki damuwa har tana zubda hawayenta.

Tsaki taja tareda gyara kwanciya, tana so ta koma dakin ta bata haquri amma tasan muddin wancan zalimun na gidan ta kai kanta mahallaka ne gara ta bari se ya tafi, haka ta ringa juyi a gado hankalin ta sam yaqi kwanciya, yanzu fa idan Maman tana can tana ci gaba da kuka ai se tashin hankulan su mata yawa, ga abindatake ciki ga Hawayen uwa ita ina zata saka ranta?

Miqewa tayi ta bude qofar,gara taje idan ma kashe ta Aminu zeyi sedai yayi din amma seta je gurin Maman, tana zare sakatar kuwa ta jishi yana yiwa Anty sallama, dakatawa tayi har tajiyo qarar bude qofar fita kafin tayi wuf ta shige dakin Maman

Nuratu na durqushe gabanta tana ci gaba da bata baki bayan Aminu ya gama nasa ya tafi ta shiga, kallon banza suka aikawa juna kafin ta tattare fuska tana kallon Mama tace

"Yanzu Mama kawai dan anzo an gaya miki qarya da gaskiya shine zaki ringa zubda hawayenki a kaina bayan kinsan abinda hakan ze iya janyo mun? Duk fa qaryace kawai baqin ciki ake mun dan an ga na samu wanda nake so yake sona anga kwana biyu muna zamab lafiya dake babu wani abu shine ake so a hada mu"ta qarasa tana Harara Nuratu da ta dauke kai dan yanzu tayiwa Maman Alqawarin bazata sake biye mata suyi fada ba amma badan haka ba seta sake gurje bakin yarinyar nan ta nuna mata banbancin dake tsakaninsu.

"Idan daidai kikeyi Umaimah kin sani in ma akasin haka ne duka keta shafa, babu abinda yayi mun zafi da sabgarki duk yanda kika ga dama kiyi ba kuma zan sake bata raina akan abinda ya shafe ki ba in Allah ya yarda. Na kuma godewa Allah da ya saka bake kadai na haifa ba kinga idan kin sakani baqin ciki ina da wasunki da zasu sakani farin ciki dan haka kije kiyi duk yanda kimaga yayi miki rayuwarki ce ba tawa ba" tana gama fada ta miqe ta shige bandaki ta barta a tsaye dan daman tuni Nuratu ta fice itama daga dakin.

Jiki a sanyaye ta koma dakinsu, kan gadonta ta kwanta tana tunani. ita da kanta ta san tana jawo mutane da yawa ciwon kai amma ya zatayi haka Allah ya halicce ta bata da ikon canza kanta (kodai kika mayar da kanki ba). Wayarta ta janyo ta shiga neman layin Khalil, badai duk akan auransa ne Mama take wadannan maganganun ba bari ta kirashi, da dai tayi alqawarin se tayi sati bata amsa wayar sa ba idan ma yazo gida bazata fita ba amma yanzu saboda farin cikin Mama da kanta zata kira shi ta bashi haquri, ita azo kawai ma ayi abinda za'yi idan ta kama wannan Juma'ar ma a daura musu aure kawai idan yaso duk randa aka a
Shirya ayi bikin shikenan dai ta wuce gorin Mama da tsoron ko wanne lokaci ana iya fasa auran ta.

Tana can tunani wayar dake ta faman ringin ta katse, sake kira tayi nan ma baa dauka ba seda ta jera masa kira goma amma ko daya be daga ba na qarshe ma rejecting yayi kafin aka kashe wayar ma gaba dayanta kamar yanda Computer ta sanar mata sanda ta sake kira

Tayi sororo da waya a hannu tana kallo, tunda take dashi bata zaton ta taba masa kira biyu, duk sanda ta kirashi kome yake ze dakata ya kirata dan baya dagawa sedai ya kashe ya kira, ba qaramin abu yakeyi ba da ze saka ya kasa daga wayarta.
Idan ma yana da wani uzuri me muhimmanci tun kafin lokacin yana sanar mata dan kar ta kira bata same shi ba amma shine yau tayi masa missedcalls 10 be daga ba bayan tasab babu abinda yakeyi yana Asibiti gurin Hajiya ko ya tafi gida ya huta.

'Qila ma yana can tare da wannan Jamilar har yana jinhaushi dan an tabata wai yar uba amma sun wani daukaketa kamar ciki daya suka fito' ta raya a zuciyarta, a fili taja tsaki dan ita abinda yasa ta qara tsanarta kenan kasancewar ta ba ciki daya suka fito dasu Khalil din ba. Haka kawai ta bata musu lissafi su kuma sun wani jata a jiki kamar uwarsu daya gaba daya ita kam bata ga dan uban da zata hada kai dashi ba, dan Kishiya ne fa.

'Idan kuma da gaske Nuratu take da tace Khalil din yace ya fasa auranta fa dalilin daya saka yaqi daukar wayarta har yayi rejecting tareda kashe waya gaba daya?' Zuciyarta ta sake raya mata, seta miqe zaune babu shiri ta dafe qirji, Khalil ya fasa auranta tabi ina taga haske Jama'a???



PROMO
PROMO
PROMO


BEFORE 4K NOW 2500

3968303018
ZAINAB SHU AIBU
FCMB
KITURA SHEDAR BIYA =?G?
08162859027

AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA

INGANTACCEN MAGANIN SANYI MAI WANKO DUK DATTIN MARA CIWON MARA CIWON JIKI HANA HAIHUWA RASHIN NI IMA RASHIN JIN SHA AWA FITAR FARIN RUWA KAIKAYI KURAJEN PP DA NA JIKI JIN ZAFI YAYIN SADUWA FITAR FARIN RUWA MAI WARI BASUR KOMAI DADEWARSHI CIWON NONO


SHIRYE NAKE ZANYI MAKU PROMO SABODA WA ANDA BASU SHA BA SU ZO SU DA DANA MAGANIN AUNTY ZEE MOM MUJAHID DUK LABARIN DA AKE BAKU GASKENA MAGANINA KANKAT NE KOBAKISHA KOMAI BA YA ISHEKI

*DAGA ALQALAMIN MARYAM FAROUK*

*(UMMU-MAHEER)*

*MARUBUCIYAR*

*WATA KISHIYAR>?p?=?y? (ALKHAIRI CE KO SHARRI)*

*RUBUTACCIYAR QADDARAH AND NOW*

*HALIN KISHI*

*HALIN KISHI LITTAFIN KUDI NE NAIRA 500*

*GA DUK ME SO ZE TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*

*MARYAM UMAR FAROUK*

*SE A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*

Free page 10
Last free page


Tun Umaimah na daukar abin wasa har ta fara shiga rudanin rashin sanin abinda Khalil yake nufi da qin daga kiranta. Raba dare tayi tana kiran wayarsa, ya kunna amma haka zata qaraci qara ta tsinke ba tareda an daga ba, ta tura masa da SMS sunfi nawa shima babu amsa, WhatsApp kuwa idan ta tura saqon ma baya tafiya tsabar rudanin da ta shiga bata san ashe Datar ce bata kunna ba.

Kafin safiya idanunta sunyi zuru zuru kamar wadda ta kwana tana zawo saboda rashin bacci da damuwar data kwana a ciki. Tana idar da sallar Asuba ta sake gwada kiran layin, call waiting aka gaya mata. Qirjinta ya buga Dam har seda ta saka hannu biyu ta dafe wayar ta subuce daga hannunta.

Tun haduwar sa dashi a irin wannna lokacin tasan da ita kadai yake waya, ze kirata idan ya tashi sannan idan ya dawo daga masallaci ze sake kiranta zuwa gari yayi haske kafin suyi sallama toh dawa yake magana yanzu? Ta tambayi kanta.

Wayar ta dakko ta sake danna kiran layinsa, still yana waya cikin sa'a ringing biyu taji ya daga da sallama, seda ta saki wata ajiyiyar zuciya kafin cikin karyewar zuciya ta kira sunansa tace
"Khalil, me nayi maka? meyasa kaqi daga wayata tun jiya daga baya ma ka kashe wayar gaba daya?"

"Am kinga Umaimah ina wani important call ne yanzu kiran da kike tayi yana diverting attention nawa shiyasa na daga ki bari idan na gama zan kiraki" Khalil ya fada daga daya bangaren kafin ta sake cewa wani abu ya datse kiran se kawai ta cire wayar daga kunnenta ta bita da ido kamar zata ganshi a ciki, ita yau Khalil ya kashewa waya.

Tagumi tayi hannu bibbiyu gaba daya kwakwalwarta ta cunkushe ta kasa samun damar yin wani tunani, me tayi masa da ze dauki zafi haka? Ita dai a saninta indai akan abinda ya faru jiya ne beci ace yayi fushi me yawa har haka ba indai ba kuma daman yana neman hanyar da ze wulaqantata bane tuntuni amma meye abin daukar zafi anan.

Bata san tsahon lokacin data dauka tana tufka da warwara ba seda ta jiyo muryar Mama daga tsakar gida tana kwala mata kira tayi firgigit ta miqe ta fita. Kallo daya Maman tayi mata bayan data amsa gaisuwarta ta nuna mata inda kwanukan wanke wanke suke tace

"Ga wanke wanke da shara nan, ki dama kunu kafin a kawo markaden qosai, da wuri Abban ku ze fita sannan za'a kai gidan rasuwar can" tana gama fada ta juya abinta ta bar Umaimah a tsaye kamar wadda aka dasa.

Wanke wanke, shara, suyar qosai duk ita kadai? A cire shara da suyar qosan ma dai a duniya abun data tsana yabi bayan wanke wanke kuma kowa yasan da wannan musamman irin na gidansu da yake da mugun yawa kamar kwanukan gidan biki.

Ta waiwaya ta kalli kamfacecen tsakar gidan nasu dayayi kaca kaca da ganyayyakin bishiya da qasa saboda iskar da akayi cikin dare jiya wannan kafin ma ta gama ai bayanta ya karye wai ma ina su Nazifi da Arma da suke aikace aikacen tsakar gidan shine za'a ce ita zatayi yau? Yaushe rabon ma da a raba aikin gidan da ita tunda ta shiga Higher institution dan idan ma an sakata ba zatayi a dadin rai ba daga qarshe ma aka dena cewa tayin sedai idan yan hankalin suna kanta taga Maman na aiki ta karba ta qarasa shine yau za'a dawo da abinda ya wuce.

"Au kina tsaye tun dazu ko babu abinda kikayi? Ai shikenan ki bari Alhajin ya fito baki hada abin karyawa ba zakiyi bayani" Mama data sake fitowa cikin shirin fita ta fada tana kallonta.
Tsintsiya ta dauko ta fara sharar kamar mara laka a jiki ba tareda ta tankawa Maman ba daidai lokacin Anty Saratu ta fito daga dakinta suka gaisa da Maman ta juya tana kallon Umaimah tace

"Aa, Umaimah ce da shara yau kuma ina su Arman tun dazu fa naji motsin shigowarsu, nima yau baccine yafi qarfina wallahi se yanzu na samu na miqe"

"Na basu markaden qosai sukai, bari naje Yusuf na jirana a waje Rabi'a aka kai Asibiti haihuwa yanzu Yaya ta kira take gayamun babu kowa a wajenta" (Rabi'a yar yayarta ce da suke uba daya).

"Toh se kin dawo Allah ya raba, idanan gama abin karyawa a biyo ku dashi" Anty ta fada tayi hanyar kitchen tana ci gaba da cewa
"Bari toh na dora ruwan kunun kafin su kawo markaden, Allah ma ya taimaka ruwa be sauka ba jiya yanda aka baje itacen nan a waje da yau mun gayawa aya zaqinta".

Har Maman taje qaramar qofar fita daga gidan ta juyo tace " Saratu karki kama mata aikin nan, ita zatayi komai zuwa anjima idan ban dawo da wuri ba ki bata abinda za'a dafa na rana tayi" ta juya ta fice daga gidan.

Hawayen takaici ne suka zubowa Umaimah wato da wannan uban aikin za'a horata kenan? Ai wallahi gara kullum a yi mata bulala goma akan wannan uban shara da wanke wanken gidanga qarin girki da itace, ina zata tsoma ranta wai? Ba'a bar mutum yaji da abinda ya dame shi ba za'a rikito masa da wani bala'in.

"Halan wani laifin kika mata ko Umaimah?" Antyta fada taba kallo ta amma yanda kasan da dutse tayi magana haka tayi,bata damu ba ta shiga hada murhu ta dora ruwan zafi kafin ta dakko qullin kunun ta shiga damawa daidai sanda Almajiran suka kawo markadan qosan, Wanke wanken tace suyi, sega Abba ya fito daga dakinsa da waya a kunnensa.

"Kai kuje abinku idan an gama abinci ku dawo ku dauka, daga yau kun bar aikin nan har zuwa sanda za'a ce ku ci gaba" Ya fada yana kallon su Nazifin, suka tsame hannu daga kumfar da suka kada tareda daurayewa kafin suka fice daga gidan.

"Wai Alhaji ya haka ne? Ya zaka hana su yin wanke wanken bayan kasan aikinsu ne yanzu waye zeyi?" Anty ta fada bayan data dakata daga buga qullin qosan da takeyi.

Ba kiji Abinda Malika tace bane da zata fita? Ga wadda zatayi nan. Kema ki tashi daga wannan aikin kije ki hadamun ruwan wanka da wuri zan fita" yana gama fada ya juya cikin daki abinsa. Umaimah ta kalla da tayi mutuwar tsaye da tsintsiya a hann, ta fara murnar Allah ya kawo mata dauki dan sharar da takeyi kadai jin bayan ta take kamar ze cire inaga ta kama sauran ayyukan se ga Abba yazo da wannan zancen kuma.

Rau rau tayi da ido tana shirin fashewa da kuka Antyn tayi saurin dakatar da ita da cewa
"Karma kiyi asarar hawayenki bari naje na same shi wannan wane irin abu ne? Itama Maman banda abi ta ina ita ina saka Amarya aikin wahala ku da ya kamata yanzu ku qara hutawa kafin a fara gyaran jiki idan wani abin kikayi ai hanyoyin horo da yawa ba lallai seta wannan hanyar ba. Ina baze ma sabu na ace za'a sakar miki wannan uban aikin ke kadai dole da sake" ta goge hannu ta ta wuce dakin Abban tana

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login