Showing 72001 words to 75000 words out of 429394 words

Chapter 25 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

946

mun kai sedai na zama yar kallo, na rantse da Allah duk inda take a Nigeria sena nemota naci ubanta, sena nuna mata ni ba sa'ar ta bace idan ma itace take shirin shiga rayuwarka zan dakatar da ita sena mata abinda ko ance ta sake kallon mijin wa...."

"Ke da Allah ya isheki haka" Khalil ya fada a fusace yana janyeta daga jikinsa,idan da ace yasan sakarcin da yake damunta kenanda ko dakin baze shigo ba ze juya abinsa. Ya kwaso gajiya tunda ya fita tsaye yake akan qafafunsa shine zata qara masa wani zafin da wauta da rashin nutsuwarta, tsaki ya sake ja me qarfi ya shige bandaki ya bar Umaimah da tunda yayi mata tsawar ta saki baki tana kallonsa.

Wankansa yayo da alwala ya fito daure da towel a qugunsa har sannan tana tsaye fuska shabe shabe da hawaye kamar wata qaramar yarinya ya wuceta ya bude qaramar Akwatinsa daya sako abubuwan buqata tana ajiye yanda suka shigo da kayan bata motsa su ba sema tata Akwatin data bari a bude data dauki Hijabi. Vest da Boxers ya dauka da jallabiyya se mai da turare ya koma gefen gado ya shiga shiryawa, tamkar babu wata halitta a dakin haka ya shareta ya gama shirinsa tsaf ya dauki wayarsa ya nufi qofa daidai lokacin da aka kwada kiran Sallar Magriba Umaimah da ta sandare a tsaye babu La'asar ga Magriba tayi ta bi bayansa da sauri tana cewa

"Ina zaka tafi kumaka barni?"
"Masallaci zanje" ya fada yana bude qofar ya fice gaba daya ransa babu dadi. Duk irin burin daya gama ci akan zuwan su Kd baya tunanin ko daya daga ciki ze tabbata, yanzu dawowa yayi da niyyar idan sukayi sallah su fita yayiwo mata shopping kayan sakaqa tunda ya ce karta dakko amma bayajin ze iya dan in sun fitana bacin raine kowannen su ze sha dan bazata fasa abinda ta faro ba shi kuma ya dena daukar shirmenta dan ya kamata ace yanzu tayi hankali ta gane daidai da rashinsa.

Daya idar da sallar a Restaurant din Hotel din ya zauna yaci abinci ransa a jagule musamman yanda yaga mutane kowa da yar matarsa ko budurwa suna cin abincinsu suna nishadi, daya gama ma waje ya fita can inda suka zuba kujeru ya zauna se kusan qarfe tara ya koma dakin nasu.

Umaimah kuwa bin bayan Khalil daya rufe qofa tayi da kallo kafin ta sauke ajiyar zuciya ta koma jiki ba kwari ta zauna ta rafka tagumi, yanzu kuma meye abinda ya bata masa rai shi kuma? Amma koma menene waccen matar ce ta jawo kuma tayi alqawarin setaci uwarta wallahi bari su koma Kano zata biya kudi duk inda take a lalubo mata ita toh shi kuma da yayi wanka ya fesa turare ina zashi daga masallacin?

Kuka wiwi ta dasa, seda tayi dagaske ta iya tashi tayo Alwala tana sallar tana goge hawaye tana idarwa ta haye kan gado taci gaba da kukan dukda yunwar data ji tana taso mata har sannan kayan data zo dasu tun safe ne a jikinta, dakin data tarar tsaf ko ina a kintse ta hargitsashi da shirgi.

Tafi qarfin awa daya tana aikin kuka har akayi sallar Isha'i bata motsa daga inda take ba tana ji ana buga qofar daga waje tayi banza dasu dan tasan idan shine yana da katin qofar a hannunsa sedai ko Ma'aikatan Hotel din, idan ta tuna gurin wata ya tafi ya kulleta a daki seta sake rushewa da kuka zuciyarta nayi mata suya, Wani tunani ya zarga mata ta miqe da sauri ta isa jikin window da yake kallon Harabar hotel din inda swimming pool yake tuni gurin ya fara cika da mutane saboda duhun dare yayi ga motoci nata shigowa Mata nata yawo da shiga kala kala yanzu a haka ya ratsa su ya fita a ina ma masallacin daya ce zashi yake?

Anya ba bakin da waccen yar iskar tayi mata bane ze fara kamata wata budurwar Khalil yayi shine ze ce mata ya tafi Masallaci dan ita dai bata ga alamar masallaci a cikin hotel din nan ba ko kiran sallar da take jiyowa tana ganin daga waje ne amma ba a nan ba ai kuw fita zatayi ta nemo duk inda masallacin yake ta tsaya ta jirashi, juyawa tayi zata bar gurin seta koma da sauri saboda hango wani da tayi kamar shi a zaune.

Ido ta gwalo tana kallon sa, Khalil din ne a zaune ga wata yarinya a tsaye gabansa ta saka wata shegiyar rigar Atamfa bata ga fuskarta ba amma ta ga bayanta da dikin ya matse tsam kamar idan ta sunkuya rigar zata yage suna fuskantar juna shida ita idan ba gizo idonta ya mata bama hannayensu take gani kamar a sarqe.

Wani jiri taji ya kwasheta ta kama qarfen window ta riqe da kyau tana jera numfashi kamar wadda tayi tsere kamar kuma wadda aka tsikarawa Allura seta juya da sauri ta zari Hijabinta dake kan sallaya har tayi gaba ta hango wuqar data yabka Apple da ita akan Plate ta dauka dukda bata san me zatayi da ita ba haka ta nufi qofa batareda ta saka hijabinba ta dai riqe a hannu.

Daqarfi ta finciko qofar zata bude ta jita a bame, ta jijjiga ta gama murde murdenta qofa taqi buduwa take ta fahimci ya kulleta ne ta waje saboda yasan abinda ze fita aikatawa. Dukan qofar ta shigayi kamar mahaukaciya tana kuka amma ko gezau qofa batayi ba dan kanta ta gaji haka ta fada kan gadon tana ci gaba da kuka tamkar ranta ze fita nan da nan ciwon kai da zazzabi suka rufeta cikinta ya murda kafin kace me ta shiga kelaya Amai akan gadon har tana neman shidewa saboda yanda ya taho mata har ta hanci daidai sanda Khalil ya bude dakin ya shigo hannunsa da ledojin abincin daya taho mata dashi.

Da sauri ya dire ledar yayi kanta yana salati ganin yanda take yunqurin kamar zata amayar da kayan cikinta, ya ruqota ta fincike dukda yanayin galabaitar da take ciki be hanata harararsa ba ta ce
"Karka tabani da qazamin hannunka da kaje ka taba karuwa dashi"

Be damu da kalanta ba ya sake matsawa yana qoqarin riqota yace
"Umaimah ki tsaya na taimaka miki jikinki yayi zafi, ki bari muje Asibiti kinsan dai bake kadai bace ko" amma ina ta fitittike ta shiga kai masa duka tana kuka da zaginsa akan yaci Amanarta a kan idonta taga ya riqe karuwa kuma tsahon lokacin nan daya dauka qila daki suka kama wallahi seta kashe kowacece ai ta ganeta shidai be kulata ba kamota yake tana zillewa dayaga tana neman bashi wahala ya saka mata qarfi gaba dayanta ya dauketa ya shige toilet da ita, jikinta ya rigada ya saki saboda Zazzabi da kuma Aman da tayi se bakinta ne be mutu ba, babu yanda ta iya yayi mata wanka tas tana kuka da koma ya saka mata qaramar Riga da Hijabi ya sake daukanta a kafada ya fita da ita suka wuce Asibiti

"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un wannan wace irinmasifa ce" Khalil ya fada yana dafe kai saboda yanda Umaiman ta ware Murya tana masa ihu a mota tana zaginsa kamar wanda ya satota, a fusace ya juya ya kalleta ya daga hannu kamar ze kwada mata mari yace

"Na rantse da Allah idan baki rufe mun baki ba sena tattaka ki a nan karki dauka tsoronki nake da yasa nake rabuwa dake kina mun duk iskancin da kika ga dama,mata kuma yanzu na fara kulawa tunda baki da amfani baki iya komai ba se tashin hankali da masifa kala kala, mtsw" yaja tsaki.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* =?L?
Page 22

Tsit tayi saboda ta tsorata dan yanda yayi mata magana seta maida kanta ta kalli window taci gaba da share hawayen da suka qi tsaya mata, idan ta tuna ganin da tayi masa da karuwar dazu se taji kamar ta shaqeshi idan yaso motar ta kwace masa su mutu gaba daya kowa ya huta amma yanda ya hade girar sama data qasa ta saka ko motsi me kyau ta gagarayi, alwashi taci a zuciyarta wallahi se ya gane kurensa.

Saboda zafin da jikinta yayi dole likita yayi mata akluran saukar da zazzabi kafin ya hado mata da magungunan da zata sha tareda dogon gargadi akan sakawa ranta damuwa kodan qaramin cikin da take dauke dashi, shi ya gaya musu satikan cikin bayan da yayi mata scanning a yanzu cikin nata na sati na takwas su kuma suna sati na goma da aure haka suka kama hanya babu me cewa dan uwansa qala har suka dawo Hotel din, bata jirashi ba dukda yanda take jinta kamar zata fadi saboda rashin kwarin jiki amma haka ta shige sedai tun a reception ta rikice dan ta manta inace hanyar bangaren da suka saukan, seta samu kujera ta zauna tana mayar da numfashi, ta daga kai kenan ta hango yarinyar dazu data gani da Khalil.

Fara kyakykyawa kana ganinta kaga fulanin usul koma ace ta hada jini da Larabawa suna tsaye da wani babban mutum suna magana, mantawa Umaimah tayi da duk wani ciwo datake ji a jikinta ta miqe a zabure ta nufeta sedai bata kai ga isa kusada ita ba Khalil da shigowarsa gurin kenan ya riqeta kamar dan sanda ya kama barawo.

"Ka sakeni na koyawa waccen kilakin hankali ta yanda bazata sake gigin kula Mazan wasu ba" ta fada muryarta bata fita sosai sabo kukan data sha, be kulata ba se qara daure fuska da yayi ya shiga janta tana turjewa

"Bayero" sukaji an kirashi se ya tsaya tsak tareda Juyowa Umaimah ta sake zabura amma riqon da yayi mata bana wasa bane,gaba daya ya mannata da jikinsa sannan ya kama tsintiyar hannunta seda tayi qarar Azaba ta shiga kiciniyar qwacewa har budurwar ta qaraso inda suke.

"Lafiya dai naga kana riqeta?" Ta fada tana kallon Umaimah da Khalil ya matse kamar burodi bugun qato ta kasa kwakwkwaran motsi, tafiya ya farayi yana cewa

"Bata jn dadi ne daga Asibiti muke, baki tafi ba kenan ko kun fasa Dinner?"

"Ai yanzu goman tayi nayi meeting da wani client dina ne akan wata kwangila idan abunuwa sun zama ready zanyi maka magana ma kayi taking care of the Arcitectural part" Burdurwar ta fada har sannan tana kallon Umaimah data haqura ta fawwalawa Allah, haka ya jata qiii suna isa dakin kafinma tace wani abu ya saketa ta tafi taga taga zata fadi Allah ya taimaketa ta dafe kujera.

Nunata yayi yace
"Wallahi Umaimah karki kuskura ki kaini bango dan bazaki ji dadina ba ki kuma shiga hankalinki karki kuskura ki sake maimaitamun irin shirmen da kikayi yau idan ba haka ba Allah zaki gane shayi ruwane" yana gama fada ya shige bandaki ya barta zaune tana binsa da kallo.

Kukan baqin ciki ta sake rushewa dashi, har yayi wankan ya fito tana zaune, seda ya gama shirin baccinsa tsaf kafin ya dakko ledar Abinci data magunguna ya dawo gabanta ya zauna, hannunsa ya dora a goshinta ta janye, jikin nata har sannan da zafi rau. Tausayinta ne ya kamashi dan haka ya sassauta fuskarsa dake dinke babu fara'a cikin lallashi yace mata

"Zo kici abinci kinga jikinki da zafi har yanzu ki dena wannan koke koken ya isa haka"

"Ni bana ci, kaje ka kaiwa waccen me kama da bulalar tunda itace..."

"Umaimah" ya kira sunanta cikin dakewa amma murya a tausashe kafin ya saka kwayar idonsa cikin nata dake zubar da hawaye dolenta ta sauke idonta qasa dan bazata jure irin kallon da yake mata ba.

"Me yasa ke baki son zaman lafiya koda yaushe kin fi so ayita tashin hankali? Abinci nace kici ba wata doguwar magana ba idan kuma kinqi zan danneki na dura miki dan bazan lamunci ki ringa barmun baby da yunwa ba"

"Seka durawa babyn yaci dan indai ta bakina abinci ze wuce ya samu ba kuwa zeci ba tunda shi ka damu yaci bani ba" ta fada tana murguda masa baki tareda juya masa qeya, murmushi yayi a ransa yana jinjina irin qaunar da Umaimah takeyiwa tashin hankali, seya saka hannu biyu ya juyo da ita yace

"Allah ya baki haquri Maman baby dukkanku na damu kuci, kinga zafin jikinki qaruwa yake ki ci ko yaya ne kisha magani ki kwanta dare yana qarayi".

Shiru tayi masa tana ci gaba da jan hanci a ranta kuwa Allah kadai yasan me take ayyanawa.
"Bazaki matso kici ba?" Ya sake fada yana kallonta amma ko gezau sema miqe qafafunta da tayi ta jingina da kujerar bayanta tana shirin bacci, Abincin ya bude, Soyayyen dankali ne da Kaza dan ya se shawarma, sun rigada sunyi sanyi.

Tashi yayi ya saka a Microwave ya dumama mata sannan ya hado shayi me kauri yana ankare da yanda take satar kallonsa ya gama ya dawo gabanta ya ajiye, muqut ta hadiye yawu saboda yanda qamshin abincin ya daketa amma ta dauke kai sema ta shigayin kamar zatayi Amai, be ko bi ta kanta ba gaba dayanta ya dorata a jikinsa ya daga kofin shayin daya rigada ya saisaita ya kai mata baki, ta kauce ya saka hannu ya danne kanta dole uwar naqi ta bude baki ta shiga kwankwadar shayin dan dama a yunwace take ita kanta tasan yaudarar kanta take amma bazata iya bacci bata ci komai ba.

Tas ta kurbe shayin kafin ya sake ta yana kallon yanda zufa take keto mata kamar wadda ta watsa ruwa, kumbura baki tayi ta sauke kai qasa ta janyo kwanon dankalin ta shiga ci Khalil yaja gefe yana kallonta cikin dan lokaci ta cinye abincin tas ta shiga sauke numfashi dan ji tayi abincinya tafi da duk wani abinda yake damunta.

"Good girl, saura wanka" ya fada yana kwashe kwanukan ya hada da tun na rana data bari ya killace su gefe, ya zata zatayi musu se yaga ta tashi zugui zugui ta wuce bandakin, wanka tayi tsaf tareda Alwala ta fito zazzabinya sauka jikinta ne dai take jinsa babu kwari se quncin zuciya wanda ta dorawa kanta.

Rigar baccindaya rigada ya ciro mata ta dauka ta saka ta dora dogon hijabibta ta tada sallah Khalil na daga kan gado yana kallonta ta idar ta gama Addu'ointa ta shafa seta zame ta kwanta a gurin.

"Ya haka zaki kwanta a qasa? Ki tashi kisha maganin se ki kwanta gaba daya" Ya fada yana qarasa wa inda take, tashi zaune tayi ya balla mata maganin ya bata ruwa ta kora tana gamawa ta sake kwanciya ta duqunqune da hijabinta.

"Wai meye haka Umaimah ya zaki kwanta a qasa cikin sanyi bayan kinsan ba lafiya ce dake ba?" Ya fada yana tsaye a kanta, seta miqe zaune tana kallonsa tace

"Dan Allah bacci nakeji ka qyaleni, idan gadon ya maka girma ka kirawo karuwarka ku kwanta tare ni nan ya isheni"

"Kee Umaimah" Khalil ya daka mata tsawar da seda taji wani abu ya tsirga mata kamar zata saki fitsari a inda take,
"Ni kike hadawa da Karuwa? Ni kike kira mazinaci Umaimah kije cewa na kira karuwa mu kwanta saboda baki da mutunci?" Ya fada yana matsota jikinsa har rawa yake saboda tsabar bacin rai, seta shiga jada baya tana girgiza masa kai dan ta tsorata da yanayinsa amma dukda haka shedaniyar zuciyarta bata rusuna ba dakyar ta bude baki muryarta na rawa tace

"Wannan ta dazun wacece? Kuma ai na ganku ta window ka riqe mata hannu sannan kuka shigo ciki kuma da zaka fita ka kulleni a daki, idan ba gurin karuwa ba ina kaje?"

Hannu ya daga da niyyar kai mata mari ya sauke hannun tareda kaiwa iska naushi, yasan idan yace ze dora hannunsa a jikinta tabbas seya mata dukan mutuwa, safa da marwa ya shigayi a dakin, baya so ya bude baki yayi magana dan yasan baze furta Alkhairi ba, a yanda zuciyarsa take tafasa yana iya furta mata duk abinda yazo ransa amma baze yanke hukunci cikin fushi ba, se ya juya ya kalleta ta maqure jikin gado tana raba ido,

Kallonta yayi na wasu sakwanni a ransa tuhumar kansa yakeyi waya aikeshi ya auri wannan yarinyar? Qasa da wata uku ace ya fara fuskantar wadannan tashin hankulan, Amma qaddar ta riga fata.
Dakyar ya hadiye yawu ba tareda ya kalleta ba yace

"Tashi ki hau gado ki kwanta"
"Ni a qasa zan kwant...."
"Na rantse da girman Allah kika bari na tako inda kike Umaimah sena illataki" ya zaburo mata babu shiri ta haye kan gadon zuciyarta ta shiga lugude kamar zata fasa qirjinta ta fito ganin yana cire jallabiyar dake jikinsa, kafin ta samu damar yin wani yunquri ya kashe fitilar dakin ya zama dundum ko tafin hannunta bata iya gani ta shiga laluben inda zata sauka daga gadon damqar da yayi mata ta sakata yin ihu babu shiri, babu tausayi ko lallashin daya sabayi mata ballantana wannan soyayyar me bin jini da jijiya ya shiga sukuwa akanta kamar ya Samu dokin sallah.

Duk ihu da roqon da ta ringa masa beji taba seda yayi mata lilis ya gaji dan kansa kaso hamsin na bacin ransa ya sauka kafin ya tsallaketa ya shiga bandaki ya sakarwa kansa ruwan sanyi lokacin ko dan yatsanta bata iya dagawa jikinta ya saki gaba daya banda tana numfashi ma se ace suma tayi.

Wanka yayi ya fito har sannan tana kwance tana jan numfashi dakyar, so take taja abu ta rufe jikinta saboda zazzabin daya mata rigib ga sanyin Ac ya cika dakin amma ta kasa, kukan zuciya take hawaye na zuba ta gefen idonta tana kallonsa ya fito ya saka jallabiyarsa ya kunna fitulu masu sauqin haske ya tayar da sallah beko nuna yasan da zaman ta a dakin ba.

Yanzu ita Khalil yayiwa wannan cin mutunchin se kace ya samu Dabba sannan ya tsallaketa ya barta a haka? Jan jiki ta ringayi dakyar ta samu ta sauka daga gadon ta rarrafa ta shiga bandaki, a gefen bahon wanka ta durqusa bayan ta kunna ruwa ta shiga rera kukan baqin ciki, seda ruwan ya taru ta cicciba dakyar ta shiga ciki, ta kwashe sama da awa daya tana gasa jikinta tana kuka gaba daya jin qasanta take kamar

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login