Showing 180001 words to 183000 words out of 429394 words

Chapter 61 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

951

kawo shi yace

"Ashsha Ashsha kiyi gaggawar yin istigfari ki nemi yafiyar ubangiji. Duk abinda kikaga Allah ya jarabci bawansa dashi yasan ze iya ne kuma Duk mumini baya rayuwa haka ba tareda jarabawa a rayuwarsa ba, idan rai ya baci ya kamata asan abinda baki ya furtawa dan a lokaci da yawa Dan Adam yana warware Ayyukansa da kansa ba tareda ya sani ba. Yanzu da kanki kin fadi kina yi mata Addu'a kina nema mata shiriya a gurin Allah sannan idan ranki ya baci kina jifanta da Kalamai masu muni wanda sune suke dada tasirantar rayuwarta.
Kinsan kaifin bakin uwa kuwa? Ko fushi kikayi da ita a zuciyarki abin seya shafeta ballantana kin bude baki kin jefeta da mummunar kalma ya za'ayi ki ambaci Yar da kika haifa a cikinki da Fitina kuma kiyi tunanin Ubangiji baze jarabceki da ita ba?
Kin zubar mata da hawaye, kin aibatata kin butulcewa Allah bisa kyautar da yayi miki ta samunta kinga kuwa bazaki taba ganin daidai akanta ba.

Dukda bansan me yarki ta aikata ba da har kike wadannan kalaman amma nasan be kama qafar abinda Dana ya aikata ba. Yanzu haka an kamashi ya haura gida ya kashe Mata da Miji da Yayansu guda biyu kuma ya amsa laifinsa akwai abinda yakai wannan tashin hankali? Kenan da kece Uwarsa take yanke zaki tsine masa yabi duniya ko? To bari kiji sanda labarin ya riski Uwarsa Tasbihi tayiwa Ubangiji ta gode masa ta shiya bata Dan ya kuma tsara cewar qaddarar sa ce a haka tun kafin ayi mu Ubangiji ya shirya yanda kowanne bawa ze gudanar da rayuwarsa ta kuma roqi ubangiji yasa hakan ya zamo amsa kaffara. Tana can kwance, kowa yasan gigitar abinda ya aikata ce ta kwantar da ita amma bakinta be mutu daga ambaton Allah da nema masa sauqi a gurinsa ba dan haka na horeki da kiyi koyi da Matata, ki yarda da qaddara a duk yanda ta riske ki daman su Yaya da Dukiya Jarabawa ce".

Yanda kasan anyi ruwa an dauke haka gurin yayi tsit babu wanda ya iya motsi me qarfi gaba daya suka raka Dattijon da ido sanda wani da suke zaton Lawyer ne yayi kiransa. Aminu ne yayi qarfin Halin bude baki dakyar yace
"Kiyi haquri Mama na kira Abdulbasit yana hanya yanzu dan sunce da Lawyer kadai zasu bari tayi magana sun hanani ganinta, yanzu ku tafi gida mu zamu tsaya muga yanda abun ze kasance in Allah ya yarda ma baze dauki lokaci ba za'a sasanta komai su dawo gida shi yasa ma ban sanarma Abba bana so hankalinsa ya tashi yana kan hanya".

Haka suka taru suka lallabasu dakyar Ma'aruf ya kwashe su a motarsa harda Mahaifiyar Rufaida suka tafi Ya rage Aminun da Khalil se Barr Abdulbasit wanda Dan Yayan Maman ne da ya qaraso yanzu.
Se a sannan Khalil ya iya bude baki yace
"Ga wayar tata a hannuna, nasanita wadda ta tura mata da hotunan dukda na duba babu wani abu da za'a samu a ciki dan ta rigada ta goge duk wani Chat da sukayi exchanging kuma tayi blocking layin kaga babu wata shaida da zata tabbatar da ita dince saboda bada layin da aka santa tayi amfani ba. Yanzu idan da hali ina so na gana da wadanda suka shigar da qarar, ina fatan idan nayi musu bayani zasu gamsu mu samu fahimtar juna ta yanda za'a warware komai cikin sauqi".

Barr Abdulbasit ne ya karbi wayar tata ya duba kamar yanda Khalil din ya fada an yi deleting message din da aka turo seya kalli Khalil yana cewa
"wannan ba wata matsala bace tunda ga amsoshin da ta bata nan suna nan kaga ko daga mam za'a samu Idea na abinda suka tattauna. Yanzu bari na fara shiga cikin na gani idan da hali se kuyi magana dasu kamar yanda ka nema tunda kaima abin ya shafeka kai tsaye" ya wuce ciki ya barsu.

A ciki kuwa bayan ya gabatar musu da kansa yayi cike ciken takaddu kafin aka sake fito masa da Umaimah, kamar yanda dai suka tambayeta shima tishi yayi akai ya dauki bayanan da yake ganin zasuyi masa amfani kafin ya koma inda Musa Kallah da Isma'il tareda sauran wakilan qungiya suke zaune. Bayan sun gaisa ya gabatar musu da kansa da kuma buqatar Khalil nason yin magana dasu kai tsaye Ismai'il ya ce Aa, seda Musa Kallah ya saka baki yace ya shigo sannan ya haqura badan yaso ba.

Tiryan tiryan Khalil ya labarta musu yanda sukayi da Khausar a wancan karon da kuma abinda ya samu a wayar Umaiman, Musa Kallah ya karbi wayar yana dubawa tareda nazarin maganganun Khalil din ya gama ya miqawa Detective din dake akan case din shima ya karba ya duba. Number suka dauka suka saka ta a computer su ta bincike, wani rashin Azanci da Khausar din tayi shine na amfani da Layi Wanda tayi register shi da sunanta dan ana shigar da number nan take duk wasu bayanai nata dake kan layin suka bayyana.

Khalil ya sauke ajiyar zuciya, daga Umaimah har Hadiza a yanzu suna buqatar daukinsa kuma kamo Khausar a hannu ne kadai ze rangwantawa Umaimah laifinta ya kuma wanke Hadiza daga Qazafin da sukayi mata. An tura da Jami'ai dasu nemo Khausar din duk inda take kasancewar yamma tayi Barr Abdulbasit ya nemi da abasu Belin Umaimah da Rufaidan zuwa gobe se su dawo a ci gaba da bincike amma qememe suka hana, a cewarsu har yanzu itace prime suspect, dan haka babu halin bada belinta har se zuwa yanda hali yayi domin koda an kawo Khausar da sun gama tattara bayanai zasu miqasu kotune gaba daya su girbi abinda suka shuka matuqar ba wadanda suka shigar da qara bane suka janye wanda kuma ba abune me yuwu ba.

Wannan ya tayar musu da hankali dan dukda abinda ta aikata dole su tausaya mata kodan halin da take ciki ga Tsohon ciki, ko iya sauron da ze cijeta tsakanin dare zuwa safiya aka barya dashi ya isheta jin jiki amma ya suka iya haka suka tafi bayan an barsu sun gansu dakyar Khalil ya fita ya siyo musu abinci da abin sha harda guzurin barguna da maganin sauro suka tafi da niyyar gobe da safe zasu dawo a dora daga inda aka tsaya.


*KAFIN SAUKAR DA KO WACE IRIN CUTA, SAI DA ALLAH SWT YA SAUKAR DA MAGANINTA. DON KIN GWADA MAGUNGUNA DA YAWA BAKI DACE BA BA SHI ZAI SA KI YANKE TSAMMANI BA. KI GWADA MAGANINMU ?AR'UWA, WATA-?ILA WARAKARKI NA TATTARE DA MAGANINMU.*
?ar'uwa mecece matsalarki? Muna ingantattun saiwoyi da sassa?e da garin magunguna na gargajiya, waWanda aka gwada kuma aka tabbatar da ingancinsu.
*Ina matan da basu taSa haihuwa ba?* Ko kuma sun taSa yi amma suka samu dogon jinkiri dalilin planning ko kuma haka kawai? Ko kuwa Sari kike yawan yi, da kin samu cikin sanadiyyar mafarki sai ya fita? ?ar'uwa albishirinki, da naira 2k kacal za mu baki ingantattun saiwoyin magunguna masu kyau, da za ki dama salala kina sha a jere har na tsawon kwanaki goma sha biyu, bayan gama sha ki zuba ido wata Waya, biyu, uku, in Allah ya yarda za ki dawo da kyakkyawan labari.

*Mijinki ne mai matsalar haihuwar?* Akwai magungunan da muke ba maza, shi ma dai da naira 2k kacal za mu haWa miki magungunan da za kiyi mishi amfani da shi. In Allah ya yarda za ki dawo mana da kyakkyawan labari.

*?ar'uwa matsanancin infection/sanyi ne damuwarki?* Ki kwantar da hankalinki. Da naira 3k kacal za mu haWa miki magunguna kala biyar, waWanda idan kika yi amfani da su duk yadda sanyi yayi miki illa kuma komai daWewarsa a jikinki za ki fatattake shi. Sunan wannan haWi *Bye bye infection.*

*Mijinki ne bai da kuzari a shimfiWa?* ?ar'uwa ko ki faWa ko kar ki faWa sanyi da basir sun gama yi ma mazajenmu illa, da naira dubu 5k kacal za mu baki dafaffen magani galan Waya wanda zai dinga shan ?aramin kofi safe da yamma. Wannan magani zai taimaka masa wajen fatattakar duk wani sanyi da basir da yake jikinsa, zai dawo da kuzarinsa sosai kamar matashin ingarman doki. Bazai ?ara neman maganin kuzari ba har'abada in Allah ya yarda.

*Ina mata, maza, yara, masu fama da lalurar Cancer/Daji?* Da naira 2k kacal za mu baku ingantattun magunguna kala huWu da za ku fatattaki daji daga jikinku.

*Ingantaccen haWin sabaya=?
?* HaWin sabayarmu duniya ne ?ar'uwa. Baza muyi miki ?aryar nonuwanki za su taso su tsaitsaya kamar na budurwa ba, amma fa za su cicciko, suyi kyau, su dinga she?i, sannan duk wata rama da take jikinki za ta cicciko, ni'ima bazai yanke miki ba saboda amfani da haWin sabayarmu.

*Muna da maganin wankin nono ga masu ciki da shayarwa.* Duk Wauri Waya 500.

*Sunana Fareeda Abdallah, a kaduna nake da zama. Amma muna aikawa da magungunanmu ko ina tsakanin Nigeria da Nijer, sai dai duk inda mai siyan magani take ita za ta biya kuWin mota ko na delivery zuwa gidanta. A tuntuSeni ta whatsapp ko a kira ni akan lambobin wayata 07039080978, 09077591726. Sai kun zo=?
?=?
?=?
?*

*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* =?L?
Page 46

A gurin Ismai'il da Musa Kallah sukayi sallama akan se goben zasu dawo, kaitsaye gidan Mama ya wuce dan be sanar da ita abinda yake faruwa ba ya bari se komai ya kammala tukunna. A can ya tarar da an sallamo Hadizan, tundaga soro yake jiyo irin Tijarar da Mama take zubawa Malama Lawisa da Hadizan akan su fitar mata daga gida ita kuma Malama Lawisa ta kafe akan babu inda Hadiza zataje dan bata da inda yafi nan din, idan ma da Wanda ze fita toh Mamance dan ita Hadizan Gadon Ubanta ne gidan.

Mama Innai da Hajiya Barira basa nan ake wannan dambaruwar sun tafi Asibitin dubota sukayi sabani, yana shiga soron yaci karo da Hadiza dake durqushe tana rusa kuka kamar ranta ze fita, gabanta ya durqusa da niyyar kamata tayi saurin sunkuyarda kanta tsakanin cinyoyinta jikinta har rawa yake saboda Azabar tsoro bata manta dukan da yayi mata ba dan ga shaidarsa nan hannunta daya tsage a nade da bandeji ba'a kwance ba.
"Dan girman Allah karka dakeni wallahi Umma Lawisa ce seda nace mata bazan dawo ba kun koreni tace se nadawo" Hadizan ta fada tana kuka kamar zata shide tsabar tausayinta besan sanda Hawaye suka fara zubo masa ba shima ya saka hannu biyu ya dagota gaba daya ya runguneta yana cewa
"Ki yafe mun yar uwata nayi nadama ki yafe mun Hadiza".

Mama da tsabar qarfin Hali ta miqe tana watso kwanukan abincin da Anty Bilkisu take kai musu suka taho dasu ta tsaya tana kallonsu, dakyar ta iya bude baki tace
"Isma'il ka rabuda yarinyar nan idan ba so kakeyi fushinta ya shafeka ba"
"Mama ki tsaya ki saurareni Hadiza bata da laifi sharri akayi mata munyi kuskure da muka kasa yi mata uzuri har bincike ya tabbatar da gaskiya ko akasin haka akan abinda ake zarginta dashi. Wallani sharri akayi mata kuma yanzu haka wadanda suka aikata suna hannun Hukuma.

Kabbara Malama Lawisa ta dauka tana kallom Mama data sandare a tsaye tana kallon Isma'il din sw tace
"Allah nagode maka daka wanke yarinyar nan tun ba'aje ko ina ba. Kin gani ko Karimatu kinga abinda ake fada miki akan kibi komai a hankali? Yanzu wa gari ya waya, da wanne ido zaki sake kallon yarki bayan duk mugayen kalaman da kika gamayi akanta kin gagara daukar qaddara gashinan tun ba'aje ko ina ba Ubangiji ya wanketa sol ya bar munafukai da jin kunya".

Jiki babu kwari Maman ta juya ta zauna a inda ta tashi, Isma'il ya kamo Hadiza da itama take cikin mamakin kalamansa, ya akayi ya gano wanda suka qulla mata wannan sharrin 'Khalil ne' Zuciyarta ta bata amsa. A gaban Maman suka zauna shida ita yana kallonta yace
"Kamar yanda na fada miki Mama an gano cewar sharri akayiwa Hadiza kuma yanzu haka ana kan bincike. An kama biyu daga cikinsu dayar ce bata rigada tazo hannu ba kuma wallahi Mama bazaki yarda ba idan kikaji su waye keda saka hannu a cikin wannan abun".

"Zan yarda mana Isma'il tunda har ka iya gamsar dani cewar Hadiza ta aikata abinda ake fada akanta babu kuma sauran wani abu da zaka fada ya bani mamaki kona kasa yarda" Maman ta fada tana kallon gefe. Yanda kasan qasa ta bude ya shige ciki haka yaji kunyar furucin Maman, shi ya kawo mata labarin ta qaryata ya kuma tabbayar mata da yayi bincike gaskiya ne se a yanzu yake nadama tabbas be kasance dan uwa na gari ba ya tabbatar idan Hadiza ce a matsayinsa zata kare shi da iyakar iya warta.
Kansa na qasa ya bude baki yace
"Ki yafe mun Hadiza na cutar dake ba akan haqqinki ba, nayi gaggawar yanke hukunci ba tareda na samu qwaqwqwarar hujjaba ki yafe mun dan Allah, kuma nayi miki alqawari bazan zauna ba har se na tabbatar da anyi miki aldalci s an bi miki kadin bata miki suna da sukayi".

"Ka dena bani haquri Yaya ba kai ba koma wanene irin wannan al'amari ya riske shi ze iya aikata abinda yafi wnada kayi. Baqin cikina guda daya ne dana rasa samun yardar ko mutum daya daga cikinku, daga kai har Mama kuka kasa shaidata amma nayi muku uzuri zamanin da muke ciki ne yayi lalacewar da bazaka iya shaidar halin Dan Adam ba saboda munfi Hawainiya saurin rikida a yanzu. Kuma ni na rigada na gayawa Khalil na yafe musu dan haka karka wahalar da kanka gurin yin shari'a da kowa, ni suka sabawa kuma na yafe musu Allah yasa hakan ya zama izina ga sauran mutane baki daya" Hadiza ta fada hawaye na sakko mata idanunta akan Mama data juyar da fuskarta gefe ta gagara ce musu komai.

Harga Allah nauyi da kunyar Hadizan ne ya kamata, ta haifeta a cikinta ta raineta, halayyarta babu wadda bata sani amma lokaci daya wani al'amari ya bijiro ta kasa bata mafaka a lokacin da duk duniya take mata kallon fasiqa.

Tana jin Malama Lawisa nata jefa mata magana, Isma'il yayi musu sallama akan gobe da safe ze zo su tafi can tare gaba daya yana kuma jaddadawa Hadizan da tayi haquri ta yafe masa ita dai tayi shiru har sannan tana durqushe gaban Mama, jira take yi tayi magan, so take taji ta yarda da ita ko kuwa har yanzu tana kan bakanta kuma bazata barta ta zauna a gidan ba.

"Ki tashi kije dakinki ki kwanta saboda jikinki" Maman ta fada kamar bata son magana ba tareda ta kalleta ba, se Hadizan ta miqe dan daman abinda take jirane ta wuce cikin dakin tana jin wani nauyi daya danne mata zuciya yana raguwa. A gaba daya abinda ya faru yardar Mahaifiyarta da Dan uwanta data rasa su suka fi komai yi mata ciwo kuma ko a yanzu idan har suna tareda ita zata iya fuskantar duk wani qalubale da ze tunkarota a gaba.

Mama kuwa Hadiza na shigewa daki ta fashe da kukan da take dannewa daidai nan kuma Mama Innani da Hajiya Barira suka shigo, masifa Hajiya Barira ta farayi akan kukan me Maman takeyi, Malama Lawisa tace
"Ku tambayeta dai, qila baqin ciki takeyi Allah ya bayyana gaskiya ya wanke yarinyar nan dukda muggan kalaman data gamayi akanta. Ni kunga tafiyata, Hadizan na ciki ga ledar Magungunanta nan kuma se an taimaka mata saboda Daurin da yake hannunta. Ke kuma Karimatu wannan ya zamar miki ishara, Jarabawa ce ubangiji ya saukar miki kuma kika gaza dauka se kije kiyita istigfari kuma ki nemi gafarar yarki dan idanbata yafe miki ba la shakka se kun tsaya a gaban Allah cikin wadanda suka yi mata qazafi" a fusace take maganar tana gamawa ta figi jakarta tayi waje bata ko tsaya amsa tambayar da suke mata ba.

Kan Maman suka juya, tana kuka ta gaya musu yanda sukayi da Isma'il,
"Nayi kuskuren daukar fushi ba tareda anyi bincike ba, yanzu da wanne baki zan bawa Hadiza haquri? Kuna kallo wasu a bakina suka qara gasgata maganar a maimakon na zama me kareta ni na sake zama silar tona mata Asiri kaicona" ta qarashe tana kuma rushewada kuka Hadiza dake maqale jikin qofa ta sulale a qasa tanaci gaba da nata kukan mara sauti. Tabbad Qazafi yanada radadi kuma wanda aka tabayiwa ne kadai ze fahimci halinda dan uwansa yake ciki amma dukda haka ta yafe musu Allah ya yafe mata nata kura kuren itama.

KHALIL
Daga CID rasa inda ze tafi ya zauna yayi, baze iya zuwa gidan Hajiya ba dan besan me ze gaya mata ba, gidansa kuma ya manto muqullin hannunsa acan SA ba kuma ze iya komawa gidansu Umaimah ya karbi nata ba dan haka kawai ya karya akalar motarsa ya kama hanyar Chilla hotel ze fi masa sauqi ya kama daki acan ya kwanta ko ze samu nutsuwa a jikinsa da zuciyarsa gaba daya. Wayarsa ya fara sakawa a chaji dan ta mutu tuntuni, Seda yayi wanka ya rama sallolin da ake binsa kafin ya zura Slippers din bandaki ya dauki wayarsa da wallet ya fita dan ya samu abinda ze saka a cikinsa da kuma Paracetamol saboda ciwon da kansa yakeyi.
Abubuwan da suka faru sun dagula masa lissafi kwarai, har yanzu daya rufe idonsa Hadiza yake gani yana kuma jin sautin Kukanta me ciwo wanda matarsa ce sila.

Ita kanta Umaimah a dayan hannun yanzun abar a tausaya mata ce. Idan da ace Hadiza ce ko yan uwanta suka shigar da qarar da abinze iya zuwa da sauqi qila a sasanta a gida ba tareda anje gaban Alqali ba amma fa Hukumar Human Right ce gabadaya yanzu ta karbi case din ahannunta, baya tunanin ko ta furta a gabansu cewar ta yafe musu kamar yanda ta gaya masa zasu yarda su janye qarar nan. Dan sauqin da yake da yaqinin zata samu shine idan an samu nasarar kama Khausar kuma ta amsa laifinta wanda ba lallai tayi hakan ba amma koma menene Umaimah ita ta jawa kanta. Rashin tunanita da Baqar

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login