Showing 36001 words to 39000 words out of 429394 words

Chapter 13 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

982

samu a gurinka bare a je ga batun murmushi ko magana me dadi, wai me yasa? Ban kai ace ina sonka bane ko yaya?"

A firgice ya dago kai daga dannan wayar da yake ya kalleta, Mansur yake so ya kira dan yana da buqatar wanda zasu tattauna wannan al'amati na Umaimah dashi sega wata sabuwar maganardaga bakin Balaraba kuma.
"Sena kashe duk macen data rabe ka" kalaman Umaimah sukayi masa shawagi a kwakwalwa, se ya kalli Balaraba cikin rarrabewar murya yace

"Ki fita indai kina son rayuwar ki"
"Ban gane ba? Saboda nace ina sonka kake nufin zaka kashe ni ko yaya?" Balaraba ta fada a kidime tana miqewa tsaye, seda ya kalli cikin office din dan ya gama tsorata da Umaimah, ji yake kamar maganar nan da suke yi ma tana ganinsa.

Qoqarin daidaita kansa yayi ganin yanda ta rikice take daga murya tun bata tara masa mutane ba yace
"Ina da wacce nake so kuma tana da tsananin kishi, idan ta samu labarin kina zuwa gurina zata iya aikata miki komai".

Se Balaraba taja tsaki ta koma ta zauna tana cewa " wallahi ka bani tsoro ni na zata ma cewa zakayi Aljana ce ta aure ka, amma mutum fa mace yar uwata zanji tsoro wadda baka ma aureta ba aikin banza kenan nida itan duk daya idan na fita Sa'a ma na same ka"

"Balaraba please go out i need privacy" ya fada yana nuna mata hanyar waje, ta yatsina fuska tana kallonsa tace
"Wai lafiyarka ma kuwa kaga yanda ka jiqe da zufa duk wannan uban sanyin AC"

"Zazzabi nake ki fita ki bani guri dan Allah" ya sake katseta, seta juya tana cewa
"Toh ai da clinic kaje aka duba ka amma kazo ka zauna haka duk wanda ya kalle ka yasan ba lafiya ba, Allah ya qara sauqi if you need help ina Reception" taja masa qofar office din ta fice.

Bin bayanta yayi ya sakawa qofar key kafin ya kuma kan couch dake gefe ya zauna, Mansur ya sake kira yaci sa'a kuwa ya daga
"Malam inada patient idan na gama zan kiraka" Mansur din ya fada bayan daya amsa wayar kafin ya kashe Khalil yayi saurin tare shi da cewa

"Kana Asibiti? Gani nan zuwa dan Allah ka sallami duk wasu patient zanzo ka dubani" qit ya kashe wayar ya shiga tattara abinda ze fita dashi, yana zuwa reception tun kafin ya bada excuse suka hau yi masa sannu dan fuskar sa ta nuna yanayin dayake ciki, dakyar ya tuqa kansa zuwa Asibitin su Mansur sanda yaje ya tarar da patient a office din haka ya azazzala Mansur daya sallame su ragowar na waje dake jira se gurin wani likitan Mansur ya kaisu.

"Wai Khalil me yak faruwa ne, ka ganka kuwa yanda ka hargitse kamar wanda kura ta biyo me yake faruwa?" Mansur ya fada sanda Khalil din ya zauna akan kujera.
"Mansur Umaimah ce, na rasa yaya zanyi da yarinyar nan gaba daya nema take ta zauta ni" Khalil ya fada.

Tsaki Mansur yayi yana kallonsa yace "Yanzu daman akan wannan gyaran malam din ne duk ka tashi hankalinka ka tashi na mutane? Ina kao kace kaji ka gani yanzu kuma meya faru, ko Jama'ar tata ne suke firgitaka?"

"Gaskiya nima na fara yarda da maganar ka da alama yarinyar nan kanta da motsi" Khalil ya fada kafin ya fara zayyanowa Mansur duk abinda ya faru tun daga case din Jalila har zuwa na Jamila da matsayar da ake akai yanzu.

Dariya Mansur ya bushe da ita da har seda Ran Khalil ya baci ya miqe yana cewa
"Wato ga Mahaukaci na kawo maka damuwata a maimakon ka bani mafita shine zaka saka ni a gaba kana dariya, ba laifinka bane laifi nane dana gaya maka" ya yi hanyar fita Mansur ya tareshi yana cewa

"Matsalata da kai saurin fushi a inda be dace ba mutumina, ga qaramar yarinya can ta gwara maka kai ka hargitse ka rasa abin yi shine ni marainin wayonka daga nayi dariya zaka yi fushi"

"Get out of my way" ya fada yana janye hannunsa daga riqon da Mansur ya masa,se Mansur din ya shanye dariyar sa yace
"Na dena toh, zauna bari na hada maka coffee ya danyi calming naka" ya zaunar dashi akan kujera kafin ya wuce inda Coffee maker take ya shiga hada musu coffee din yana kallon Khalil dake ta zare ido.

"Toh yanzu kai me ka zaba a ciki, fa fasa auran nata ta sheqe duk wacce ka kula ko kuma zaka aure din a yanda take?" Mansur ya fada yana miqa masa cup dake cike da Coffee.? Seda ya kusan shan rabi kafin ya ajiye yana kallon Mansur din yace

"I don't know Mansur, nima ban san me zanyi ba. All i know is i do love Umaimah alot, kuma ko maganar fasa auranta da nayi barazana kawai nake mata amma wannan maganar da tayi itace ta qara tsoratani ta saka mun shakku akan ta. Kisa fa Mansur she is saying it with full confidence zata kashe ko wacce mace akaina sedai itama a kasheta, what do you think she will do randa aka ce na aureta ina so na qaro wata kaga ni zata kashe kenan"

"Wannan ma ai a rubuce take Abokina kai dare zata bi ta yanka ka sedai da safe kawai ace mana Bayero ya sheqa matar sa ta masa yankan rago" Mansur ya sake fada, wata harara Khalil ya maka masa yace

"Kaidai wallahi mutumin banza ne, ana neman mafita zaka sake tayar mun da hankali, please Mansur give me solution, kaina baya aiki kwata kwata i can't think" ya qarasa maganar yana dafe kansa daya ji ya dauki ciwo.

"Nifa ko a duk abin nan banga wani abin damuwa ko tashin hankali ba,? daman yarinyar nan kasan bata da saiti ka kwasota babu yanda banyi da kai akan ka kyaleta ka nemi wata ba kace No, se yanzu da ake maganar lessthan a Month biki zakace ka fasa?

Yarinyar nan fa har certificate na brain check dinta kace Dad dinta ya nuna maka to tell you that ita dinKwankwararriyar mara jin magana ce har ana zaton tana da mental illness amma kace kaji ka gani a haka kake so se dan yanzu tayi maka wannan dan qaramin shirmen ai ni banzata za'a ja lokaci bama har haka halinta be fito ba kuma ai you should expect morethan this ma duk wani shirme da zatayi maka dole ka shanye tunda kai ka kai kanka.

Yanzu dai abinda za'i kawai dai kayi qoqari ka dora mata saiti, ka zare mata ido sosai ka kuma kora mata warning, tunda tana sonka nasan she will comply with all your conditions".

Tagumi kawai Khalil ya zabga yana kallon Mansur dake koro bayani kamar besan girman kalmar kisan da Umaimah take ambata ba ko dan bashi tace zata kashe ba oho, jin yayi shiru alamar ya gama ya saka ya numfasa yace

"No Mansur I'm scared, like I'm fucking scared wallahi. Dane fa mata suke kurari akan abu su kasa yi amma yanzu kana kallo kullum a social media se kaga sabon case na mace ta kashe Mijinta akanabinda be kai ya kawo bama and you are saying duk kurari kawai takeyi wadanda basu akita ba ma yara qanana zakaga sun aikata, yarinyar nan fa Kishi ne da ita na Bala'i".

"Toh Khalil yanzu ya kake so ayi? Kuma maganar wani kishi kowacce mace tana da irin nata, yawanci kum loud ones din nan nasu Kishin iya baki ne suyi hayaniya shikenan, amma masu shirun sunfi hadari, sune suke kashe mutum din lokaci daya a ringa mamakin bazasu iya ba.

Umaimah ka barta da shirmenta harda yarinta duk suna damunta amma maganar Kishi ko zata kashe wani saboda kai duk shirme ne tana fada ne kawai saboda ka tsorata and she succeeded ga kanan ka birkice kamar wanda ya bigi motar sojoji amma bazata iya ba, beside wanda zeyi abu ai baya fada sedai a gani a aikace" Mansur ya sake fada, se Khalil ya girgiza kai yace

"Aa Mansur, i wish you were there kaji yanda take jaddadamun da zata kashe kowa sannan zan saka kaina a ciki? Aa gaskiya, ina son Umaimah amma barinta shi yafi mun Alkhairi Mansur".

"Ok assume ka fasa auranta how about the life of innocent girls da zakayi puting at risk? Kace cewa fa tayi tunda ta rasa kowa ma baze samu ba zata kashe duk Macen data shiga rayuwarka, to is it not better to Marry her and save lives ko kuma ka zabi ka jazawa yaran mutane ko kuma zaka zauna ne babu aure?

Think about it Khalil ba fata ba ace qanwarka akayiwa haka in a month time to her wedding mijin yace ya fasa kai baka san zafin abin ba ni na sani because it happend to my sister kana kallo sanadin haka Lubabatu har depression ta shiga, tun farko ai Iyayenta basu rufe ka ba sun gaya maka komai amma zaqin soyayya ya kwasheka ka kasa ganin aibunta se yanzu?

Kishi kuma kaine zakayi abinda ze motsa mata shi indai ka kiyaye zaku zauna lafiya, idan kasan halin mutum kaci maganin zama dashi shikenan. In? dai shawara ta kake nema Khalil just go on with Umaimah, kayi Addu'a Allah yasa hakan ya zamar muku Alkhairi".

"Shikenan Mansur nagode zanje na cigaba da Addu'a Allah ya zaba mana mafi Alkhairi" Khalil ya fada yana miqewa tsaye, sukayi musabaha ya kama hanyar fita a ransa sam beji wata magana da Mansur din ta fada ta kama shi ba. Ta ina ma ze fara wannan gangancin? Shima Mansur din qin Allah ne yasa yake gaya masa haka yanzu bayan tun farko ma shine ya fara nuna baya son Alaqarsu a sannan ma zato kawai yake na tana da Aljanu, se yanzu daya samu babban dalilin rabuwa da ita yace masa wai Aa karyayi saboda bashi aka ce za'a kashe ba ina ba wannan maganar.

Daga Asibitin su Mansur Asibitin da Hajiyar sa take kwance ya wuce dan su biyun nan sune manyan abokan shawararsa, duk kuma abinda suka yanke masa dashi yake amfani toh yau Mansur yayi Failing yanzu saura Hajiya dukda be so ya tado mata da maganar tana Asibiti yaso ace se ansallame ta amma lokaci yana tafiya. Ko jiya da daddare seda tayi mitar me yasa ba'a kai lefe ba aka tsaya saboda jinyar da takeyi ta kuma ce a cikin satinda za'a shiga ko ba'a sallameta ba a saka rana akai.

Daga yanayin sallamar sa Hajiyan ta gane babu lafiya, yaja kujera ya zauna suka gaisa da Mama Talatu matar qanin Hajiyar ce da suke matuqar shiri tun qaninnata yana raye har yanzu kuma daya rasu suna zumunchi sosai yanzun ma ita take zaman jinyarta.

"Ango kasha qamshi, yanzu fa zancenka muke Hajiya tace na miqa mata waya ma ta kiraka ashe kana tafe" Mama Talatun ta tsokane shi, se yayi murmushin da be kai zuciya ba ya shiga gaishe su, mace ce me wayayya daga yanayin da Khalil dinya shigo ta fuskanci da magana a bakinsa dan haka ta miqe bayan ta tura masa kayan karin da su Habiba suka kawo tayi waje ta basu guri dan bata san maganar da yake so yayi kota sirri bace.

Hajiya dake qare masa Kallo tunda ya shiga dakin tace "Babana lafiya kuwa? Kaga fuskarka yanda tayi meya same ka bayan ka bar nan jiya, koda yake tun a daren na fahimci baka da walwala ko jikin Umaiman ne yaqi dadi?"

Sunan Umaimah data ambata ya qara saka zuciyarsa tsinkewa, toh Mansur ma yaqi bashi goyon baya inaga Hajiya datafi kowa son hadinsa da Umaimah bama ya zaton zata saurari duk abinda ze zo dashi amma koma yaya ne dole ya gaya mata tunda dai bashi da wadda ta fita.

Kansa ya shiga sosawa ba tareda sunhada ido ba yace
"Hajiya daman akan maganar tane, inaga Kawai a dakata da maganar kai kayan nan yanzu"

"Kamar yaya a dakatar da kai kaya Babana? Ina saura sati hudu daurin aure ya kama yau? Idanba'a kai lefe yanzu ba har se yaushe za'a kai musu bayan da tun satin daya wuce za'aje wannan tsautsayin ya faru, idan ma dan maganar kudi da akace ka bada ne baka dasu ka barshi zan gayawa Sa'adah ta ranta a qarasa komai in yaso ni daga baya se na bata" Hajiyan ta fada cikin kulawa tana kallonsa.

Tasan harkar biki da cin kudi kuma Khalil din yayi Namijin qoqari sosai tundaga kan gyaran gidansa daya dawo kamar sabo kai bakace an taba rayuwa a ciki ba har zuwa kan lefen sosai ya saki kudi akayi masa siyayya dukda Yan uwansa Mata sun saka hannu amma shi yayi rabi da kwatan kayansa.

"Hajiya ba maganar Kudi bace ta saka ita Umaiman ce kawai nake ganin kamar zamn mu baze yuwu ba saboda HALIN KISHInta" Ya sake fada kansa a qasa. Se Hajiya ta saki murmushi taredagyara zamnta dakyau tana kallonsa tace

"Se yanzu kenan yan tsurku da munafuncin suka tarar dakai, Baban yaushe ka fara saurarar qananun maganganu na mutane?
Tun sanda ka fara neman auran yarinyar nan babu kalar gulma da tsugudidin da ba'a kawo mun akan ta ba ance baqin kishi ne da ita, bata da nutsuwa, aa mutuniyar banza ce kai har akwai wadda tace ta zubar da ciki shi yasa sau uku ana saka mata ranar aure ana fasawa".


PROMO
PROMO
PROMO


BEFORE 4K NOW 2500

3968303018
ZAINAB SHU AIBU
FCMB
KITURA SHEDAR BIYA =?G?
08162859027

AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA

INGANTACCEN MAGANIN SANYI MAI WANKO DUK DATTIN MARA CIWON MARA CIWON JIKI HANA HAIHUWA RASHIN NI IMA RASHIN JIN SHA AWA FITAR FARIN RUWA KAIKAYI KURAJEN PP DA NA JIKI JIN ZAFI YAYIN SADUWA FITAR FARIN RUWA MAI WARI BASUR KOMAI DADEWARSHI CIWON NONO


SHIRYE NAKE ZANYI MAKU PROMO SABODA WA ANDA BASU SHA BA SU ZO SU DA DANA MAGANIN AUNTY ZEE MOM MUJAHID DUK LABARIN DA AKE BAKU GASKENA MAGANINA KANKAT NE KOBAKISHA KOMAI BA YA ISHEKI

*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK(UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* =?L?
PAGE 12

Da sauri Khalil ya daga kai ya kalli Hajiyan jin wannan qundumemen batu, ta daga masa kai da sigar tabbatarwa kafintaci gaba da cewa
"Tabbas, magana ba irin wadda ba'a gaya mun ba amma duk naji na toshe kunnena saboda nasan da cewar qarya ce. Tun kafin naje gidan yarinyar seda yar uwarta ta zayyana mun komai akanta tun kama daga kan Kishin da mutane suke ganin tanayi yayi yawa har halin tsiwarta da komai yar uwarta bata boye mun ba.

Haka zalika da naje gidan su Mahaifiyarta ta sake tisa mun tamkar yanda yar uwarta ta fada abinda ya qara musu qima kenan a idona dukda take tasu ce basu boye aibunta ba sun bayyana wanda shine gaskiya dan aure ba'ayi masa rufa rufa, idanma an rufe shi hali baya buya dole wata rana ze bayyana kansa kuma kaima nasan ka san komai kuma kaga kaji ka gani kana sonta a hakan, se yanzu da dan lokaci ya rage sannan zaka bari hudu bar shedan da gulmar mutane tayi tasiri a zuciyarka?

Meye matsalar ta, kishi koh? Toh kaje ka tambayi Hajiyar Gaya (Mahaifiyarta) zata baka tarihin quruciyata, kuma yau da Mahaifinka yana raye da ka tambayeshi shima ya baka labarin Kishina dukda haka kana iya zuwa gurin Babanku Jibril (Babban Aminin Mahaifinsu ne) dan dashi aka sha gwagwarmayar komai.

Dan haka idanma abinda ya gigitaka kenan kazo kamar wanda aka biyo toh kama dena wani tunani akan batun kishi kowacce mace zaka aura tana da kishi sedai kawai na wata yafi na wata zafi, kuma wata tafi wata iya danne nata, in dai kuma kace zaka ringa daukar zugar mutane akan iyalinka toh kana tareda matsala kuwa. Dan wani qyashi da hassada ce zata saka ya ringa kawo maka gulmar da zata haifar da rashin zaman lafiya a gidan ka".

Shiru Khalil yayi, daga yanda hajiya take jero masa bayanin nan ya tabbatar da babu wata kalma da zeyi amfani da ita da zata saka ta ga baqin Umaimah, amma dukda haka baze sare ba dan shi harga Allah ya tsorata da auranta saboda duk wadanda zasu ce yayi basune zasu zauna da ita. Ba fata ba kuma ranar da abin qi ya faru ace shi ya jawo wa kansa dan haka tun kafin azo wannan qadamin dole ya nemar wa kansa mafita, idan Kuma Allah ya qaddara faruwar auransu shi kenan, amma dai Allah ya gani yayi iyawarsa dan ya tseratar da kansa daga wahala.

Zaman sa ya gyara yace "Hajiya wannan ba zancen zugar Mutane bane, jiya fa Hajiya saboda mun riqe hannu da Jamila shine tayi fushi ta tafi ko mota ta qin hawa tayi se Nuratu kawai na mayar gida ita ta hau Adaidaita, sannan bakiji abinda ta ringa fadamun ba har cewa tayi ta fasa auran ma gaba daya ita.
Toh Hajiya tayi haka akan Jamila da tasan babu aure a tsakanin mu inaga kuma idan ta ganni tareda wata macen? Ni dai tsoro nakeji Hajiya, kina kallo dai yarinyar nan matar Hafizu na can qasan layi da ta cakawa masa wuqa saboda zeyi aure, yanzu da yazo da qarar kwana da tuni fa an manta da babinsa".

Seda Hajiya ta gama jin sa tsaf ta kalle shi da hararar wasa tace "Nidai Babana takwaranka kafin ya mutu se da yayi mata takwas kuma hurhudu suka zauna idan wata ta rasu ya maye da wata kana kallo da dai wayon ka ya bar hudu rayayyu gashi nan kuma har yanzu suna zaune a cikin gida guda dukda baya nan, se kai kake tsoron guda daya jal Khalil? Kuma banda abinka Mijin da ake so ai shi ake kishi.

Da bata sonka idan matan duniya zaka kula ko a qasan takalminta sannan maganar Jamila ai dole tayi kishi yanda kuke abu kamar wasu qananan yara su Allah ne be taba kai idon Mazajensu sunga kuna wannan rungumar da riqe hannun ba da tuni sun taka muku burki, nasan kuma kai yanzu da ace zatayi haka da nata dan uwan se anji kanku dan kaima ai zani ce ta taradda muje zuwa kishin ne da kai.

? Haba idan mutum ya girma yasan ya girma mana ai koda suke muharramanka kunyi girman da kun wuce

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login