Showing 33001 words to 36000 words out of 429394 words

Chapter 12 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

1575

ci gaba da mita.

Karon farko da Umaimah taji yau Antyn ta mata abin arziqi dan ko babu komai ta nuna tausayawa akan ta abinda uwa da uban da suka haifeta basu mata ba. Sharar taci gaba dayi tana share hawaye, a kan window ta ajiye wayarta yabda da Khalil ya kira zataji qara amma har sannan bataji ko qarar shigowar saqo ba ga wannan sabon bala'in da taje ciki kuma haka ta qarasa sharar ta kwashe,

Ruwan kunun ya tafasa har sannan kuma Antyn bata dawo ba, tasan halin Abban sarai dan haka sahunta a likafa gara tayi abinda zata iya kafin ya fito ya nemi abin kari, ruwan ta sauke a garin juyewa ya dan zubo mata a qafa saboda gaba daya hankalinta baya kan abinda take yi ta kuwa saki qara ta wancakalar da tukunyar a qasa tana yarfe hannu tareda sosa inda ruwanya zuba.

Daga cikin daki inda Anty da Abban suke dauki ba dadi suka leqo a tare, da sauri ta qaraso gurin tana cewa "meya faru? Badai qonewa kikayi ba?" Umaimah babu bakin magana se kuka take tana yarfe hannu, Anty ta dubi Abba daya ja ya kwafe a a tsaye tace

"Ka gani ko gashi nan haka kawai kun jawo ta qona qafarta, fisabilillahi Alhaji me yasa kake haka? Duk fa abinda Nasiha da Addu'a basuyi maganin sa ba duka ko aikin wahala bazeyi ba. Yanzu gashi nan tun baa je ko ina ba ta qona qafa ta yaya kake zaton zata iya da aikin gidan nan ita kadai? Ko mu din da muke yi ai muna da mataimaka ballantana" ta ci gaba da mita dan itama gwanace a fannin kafin ta debo qulli ta zuba mata akan qafar bayan data tofa mata Addu'a tace
"Tafi ki zauna haka kawai da safiyar nan an jawo miki"

"Ruwan bada yawa ya zuba ba ba? Ko zamuje a duba mata qafar?" Abba ya fada yana kallo ta, se Umaimah ta girgiza kai har sannan tana hawayen tace "Aa Abba baze tashi ba tunda Anty tayi mun tofi, anjima se naje gurin Ya'u me Chemist ya bani magani"

"Allah ya sawwaqe" ya fada tare da juyawa dakinsa.
Umaimah ta dingisa ta dauki wayarta ta shige daki, seda ta wanko qafar a Bandaki kafin ta zauna kan gadonta tana sauke ajiyar zuciya fa ruwan kadan ne ya dan zubar mata, yanda abin yazo mata a bazata ne ya sakata sakin tukunyar ta fake da hakan ne kawai saboda ta samu mafita gashi kuma Allah ya fiddata.

Number Khalil ta danna zata kira sega kiran sa ya shigo cikin azama ta daga tareda fashe wa da kuka kamar wadda aka cewa Mamanta ta mutu. Be ce mata qala ba ya barta tayi iya yinta, abinda ya ringa qarawa kukan nata qaimi shirun da yayi mata, ta saba idan tana so ta daga masa hankalo kawai zata kirashi ta fasa kuka shi kuma ya ringa lallashi da banbaki kenan har se tayi shiru amma yau yana jinta yai buris da ita dan kanta tayi shiru kafin tace

"Wai me nayi maka Khalil kake Azabtar dani haka? Kasan yanda nake ji kuwa? Ko so kake se zuciyata ta buga na mutu sannan zaka yarda da sonka ya gama yi mun illah?"

Daga bangaren Khalil dake zaune a office dinsa ya rufe ido ya dafe kansa da hannu daya, shi kadai yasan wahalar daya sha daga jiya zuwa yau saboda rashin magana da ita, gaza jure ganin tana kira baya dagawa yayi abinda ya saka ya kashe wayar gaba daya kenan daga baya kuma ya kunna ya sakata a cikin drawer kawai dan juriyarsa ta kusa qarewa.

Yanzun da take wannan kukan jinsa yake kamar ana masa yayyafin ruwan zafi, ita take kukan shi yake jin zafin abin a ransa amma yaya zeyi? Umaimah bata dace dashi ba. Dole ta qarfin tuwo ya yakiceta daga ransa in har yana neman zaman lafiya a rayuwarsa amma yaga abin da kamar wuya dan ji yakeyi wutar son ta tana qara ruruwa a zuciyar sa a maimakon tayi qasa.

"Khalil Khalil kana jina kayi shiru" Umaimah ta fada abinda ya dawo dashi daga tunanin daya tafi kenan, gyaran murya yayi yana jin wani na taso masa akan abinda yake shirin aikatawa amma yasan shine kadai gatan da zeyi musu daga shi har ita,

"Umaimah duk wannan drama da kike yi ta mecece wai? Kin manta irin zagin da kikayi mun jiya da irin kalaman da kika gaya mun? Kefa kika fada da bakinki babu ke babu ni na fita daga sabgarki to me kuma kike so nayi miki yanzu?"

"Duk abinda na fada maka bacin rai ne ya saka, kasan yanda nake sonka nake kishinka wallahi Khalil idan na ganka da wata mace ji nake yi kamar na kashe kaina tsabar baqin ciki kuma duk abinda na fada maka ba daga zuciyata bane kawai raina ne ya baci amma ba da gaske nake ba" Umaimah tayi saurin katse shi.

Se yayi wani dan murmushi kafin yace "Bacin rai se ya saka hankali ya gushe kuma? Sannan Kishi ya rufe miki ido kin kasa banbance yan uwana da sauran Mata, idan kinyi haka akan yar uwata ta jini da babu aure a tsakanina da ita Umaimah me ze faru kuma duk randa kika ganni da wata daban, kinga komai yana iya faruwa kenan.

Bazan iya saka rayuwata a cikin matsala ba, zan aureki ne saboda ki yi daidai da tsarina ina sonki ina kuma samun farin ciki a gurinki bansan wannan rashin hankali shi kike kira da kishin da kika ce kina dashi ba, a ban aureki ba kin zage ni saboda wata kinga kuwa idan mu kayi aure tsaf zaki iya neman rayuwata dalilin wannan baqin HALIN KISHIn,
Se yanzu na gano ainihin abinda ya saka sauran samarinki fasawa nima Allah ne ya soni da rahama ya kawo faruwar hakan da qila watarana ina bacvi sedai kawai na farka na ganni a lahira dalilin abinda bansan mafarinsa".

"Allah ya tsareni da kashe ka, ina sonla Khalil dana rasa ka gara na rasa raina, dagaske zanyi fito na fito da duk wadda tace zata shiga tsakanina da kai amma bazan taba bari wani abu ya shafi lafiyarka ba, zan kareka da iya kar kulawata, zan baka farin ciki har qarshen rayuwata saboda kai din kaine Rayuwata" Umaimah ta fada tana fashewa da wani sabon kukan daya ke jinsa har cikin ransa, so yake yace tayi haquri ta dena amma ya rigada yayi making mind di sa akan tarayyarsu ba kuma ya son wani abu da ze karya masa lago, ko wannan doguwar maganar da suke yi ji yake kamar ze rasa qarfin guiwarsa.

"Wallahi Khalil ina sonka, idan kace zaka barni rayuwata zata shiga cikin garari, zan iya rasa raina idanka rabu dani saboda na rigada na saddaqar maka da ruhina. Nayi maka alqawari zan zama me maka biyayya bazan taba tsallake umarninka ba, bazan sake tayar maka da hankali akan wani abu ba zan shanye komai saboda farin cikinka koda hakan yana nufin yankewar numfashi na saboda na sani wata rana kishinka ze iya zama ajalina" Umaimata sake fada cikin wani irin kuka me tsuma zuciya da ya saka jikin Khalil daukar rawa, a maimakon ya samu nutsuwa da? kalamanta sema qara shiga rudu da tashin hankali yakeyi, tabbas yana son Umaimah ko yace yana Qaunarta, amma ita a nata bangaren wannan ya zarce Love sedai a kirashi da Obsession.

"Umaimah ki dena kuka haka, kiyi haquri amma bana tunanin zamu rayu tare, wannan tsananin kishinda kike dashi a kaina ze iya zamar mana tangarda a cikin rayuwar auranmu saboda a kullum zuciyarki zata ringa raya miki abubuwan da ba haka suke ba, kinga kuma ke yanda kike handling bacin rai, bana so muyi abinda wata rana za muzo muna dana sani.
Ina sonki amma bazan iya auranki ba, Kiyi haquri muyi Addu'a Allah ya hada kowannen mu da Alkhairinsa" Khalil ya sake fada abinda ya janyo tsayawar ji da tunanin Umaimah na wani lokaci, sedata kwashi kusan minti biyar shi kansa A nasa bangaren seda Numfashinsa ya rage sauri na wasu sakanni kafin yaci gaba, jiran amsa yake daga bangarenta amma yaji shiru, har ya yi tunanin ko Network ne ya dauke yaji yo ta tana magana cikin wani irin sauti me kama da wadda kw komawa da numfashinta tace

"Khalil daman ka shiga rayuwa ta ne saboda kaga bayana? Waya turo ka? Me nayi wa wani daya zabi hukuntani da irin wannan hukuncin me tsanani, kasan yanda Sonka ya yi wa zuciyata illah? Ka qaddara a ranka Khalil tunda na rasa ka babu wata mace data isa ta rabeka, yanda zanqare rayuwata babu aure kaima haka idan kuwa har kayi gigin kula wata to tamkar ka siya mata tikitin tafiya lahira ne dan kuwa sena kasheta, muddin ina numfashi sena kashe duk wata Mace data shiga cikin rayuwarka.

Saboda ni aka halicce ka babu macen data isa ta ratsa zuciyarka bayan ni, idan kuma kana ganin wasa ne ka gwada Khalil, ka gwada kula wata mace wallahi sena ga bayanta" ta qarasa tana sakinwani siririn kuka daya saka Khalil zabura ya miqe dan tunda ta fara magana hankalinsa yayi qololuwar tashi, kafin yace wani abu ta kashe wayar.

"Innalillahi wa'inna ilahi raji'un" yake maimaitawa yana zagaye office din, dukda kasancewar Ac a kunne take amma zufa ce take keto masa ta ko ina kamar wanda yake naquda, wannan shi ake kira da anyi gudun gara an tadda zago. Shi daya ke neman rabuwa da ita saboda gudun tashin hankali gashi ya gayyatowa kansa babban tashin hankalin daya shallake na da.

Kisa fa take iqirarin yi akansa kenan shi kansa tasa rayuwar a cikin hadari take, idan har zata kashe wata saboda shi toh shine ze zama target dinta na farko kenan yanzu yaya zeyi? Meye mafita?
Zabi biyu gare shi a yanzu, kodai yayi jahadi ya auri Umaimah ya siyi tashin hankali da kudinsa ko kuma ya barta ta zama barazana ga rayuwar duk wata mace da ze kula, duk cikin wadannan zabin kuma babu wanda yake jin ze dauka dole akwai wata hanya bayan wannan, dole ya nemawa kansa mafita daga Tarkon Umaimah.

End of free page

Domin jin yanda zata kaya tsakanin Umaimah da Khalil Ku hanzarta biyan 500 dinku zuwa Asusun
8142548705
Opay
Maryam Farouk

Seku tura shedar biyan zuwa ga
07061838488

Yanzu ma aka fara wasan, Littafin Halin kishi yazo muku da sabon salo tareda tabo jigon da yake jijjiga mata a halin yanzu, ina me baku tabbacin bazakuyi nadamar bibiyar labarin Umaimah ba, kudai ku hanzarta biyan kudin karatun ku se naji ku =؃?
PROMO
PROMO
PROMO


BEFORE 4K NOW 2500

3968303018
ZAINAB SHU AIBU
FCMB
KITURA SHEDAR BIYA =?G?
08162859027

AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA

INGANTACCEN MAGANIN SANYI MAI WANKO DUK DATTIN MARA CIWON MARA CIWON JIKI HANA HAIHUWA RASHIN NI IMA RASHIN JIN SHA AWA FITAR FARIN RUWA KAIKAYI KURAJEN PP DA NA JIKI JIN ZAFI YAYIN SADUWA FITAR FARIN RUWA MAI WARI BASUR KOMAI DADEWARSHI CIWON NONO


SHIRYE NAKE ZANYI MAKU PROMO SABODA WA ANDA BASU SHA BA SU ZO SU DA DANA MAGANIN AUNTY ZEE MOM MUJAHID DUK LABARIN DA AKE BAKU GASKENA MAGANINA KANKAT NE KOBAKISHA KOMAI BA YA ISHEKI

*HALIN KISHI*
*(NADAMAR UMAIMAH)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* =?L?
Page 11

Umaimah

Kuke take tamkar ranta ze fita ta kasa yarda wai Khalil yace ya fasa auranta, wai me yasa? Me takeyi wanda har suke kasa jurewa suke iqirarin bazasu iya ajiyeta a gidan su ba? Laifine dan tayi kishin abinda take so? Ita a ganinta ai abin Alfaharin namiji ne ma ayi kishinsa amma a maimakon ta burge se gashi hakan ya zamar mata kamar wani tabo da kowanne namiji ya tashi yake fakewa da shi ya gujeta.

"Wayyo Allah na na shiga uku zuciyata zata fashe" ta fada cikin kuka tana dafe qirjinta da take jin kamar ana hura mata wuta. Anty na tsakar gida tana suyar qosai har sannan tana mitar abinda ya faru ta kwallo mata kira akan tazo ta debi Abin karyawa kafin yayi sanyi, ta kirata yafi sau uku dan haka data tsame na kaskon seta miqe ta dauko plate da cup ta zuba mata komai ta wuce dakin tana cewa "Qila qafarce, a zafin nan ka qone ai dole mutun yaji jiki. Gaskiya dole ma a kaota Asibiti a duba ko bata tashi ba sa bata abinda zata shafa ya rage zugi" dai dai nan ta isa qofar dakin wanda tun daga wajen take jiyo nishi da kuka kukan da Umaimah takeyi tamkar me Naquda.

Cikin tashin hankali ta ajiye kayan kan mudubi ta hau jijjiga Umaimah dake kwance a qasa tana juyi fuskarta tayi kaca kaca da Jini da alama Habo tayi in banda wayyo wayyo babu abinda take fadi.
Na shiga Uku nu Saratu, Umaimah meya same ki? Alhaji" Anty ta kwala kiran Abba se gashi a firgice dan da qarfi tayi kiran kuma kanaji kasan bana lafiya bane

Yanda yaga Umaiman shi kansa hankalinsa ya tashi, bugun lugude zuciyarsa ta shigayi a ransa yana tunanin jinin daya gani a jikinta na meye? Kardai yarinyar nan nema tayi ta lahanta kanta akan rashin hankali?

"Alhaji ka kamata mu kaita Asibiti ka tsaya kana kallon mu" Anty ta fada cikin kuka, seya sunkuya ya dauki Umaiman cak ya juya ya fita, bin bayan sa tayi saboda rudewa ko mayafi bata saka ba seda ta kai qofa ta tuna da mai data bari a kan wuta gashi babu kowa a gidan kar kuma wani abun ya sake faruwa dan haka ta koma jikinta na rawa da kyar ta iya tattara hankalinta ta sauke Man gefe ta kashe wutar kafin ta rurrufe sauran kayayyakin ta figi Zanin data samu akan Igiya tayi waje jin An fita da mota.

Emergency aka karbi Umaimah, Abba, Anty da Salman da suka kawo ta se zarya suke a qofar dakin da take likitoci nata shige da fice amma babu wanda yace musu komai. Seda aka kwashi kusan Awa daya kafin wani likita ya fito fuskar sa dauke da damuwa ya kalli Abba yace "Bismiah Alhaji muje office ina son magana dakai"

"Dr a wane hali take? Zamu iya shiga mu ganta? Anty tasha gabansa tana tambaya, seya girgiza mata kai Alamar Aa yace
" Babu matsala hajiya munyi qoqarin ganin ta fita daga dukkan hadari yanzu munyi mata Allurar bacci ne wanda dakyar ta dauke ta shi yasa baza muso ayi wani motsi me qarfi a kusa da ita ba, idan ta tashi se ku shiga ku ganta".

Guri ta samu ta zauna tareda Salman Abban ya wuce shida likita, yanda ta shiga tashin hankali tamkar ita ta haifi Umaiman a cikinta, koda yake basu banbanta yaran, yanda Mama ta ja nata ta riqe kamar ita ta haife su dole itama ta cusawa zuciyarta irin wannan aqida duk kuwa da zuga ta yan uwa da qawaye harma da wadanda abin be shafa ba amma da ta toshe kunnenta gashi nan sama da shekaru Ashirin suna zaune lafiya idan ka cire qananan sabani da ake samu tsakanin ko wandanne yan Adam.

Suna da kyakykyawar fahimta da alaqa me kyau wanda kuma Maman ce ta assasa. Daman ita Uwargida itace bango, duk yanda ta tsara ta tafiyar da rayuwar gida haka ake dorewa koda kuwa ace an samu fitinanniyar Amarya indai Uwargida ta tsaya akan gaskiya da Adalci ana samun daidaito.

A office din likita bayan sun zauna ya dubi Abba yace
"Damuwa ce tayiwa yarinyarka yawa data haddasa wa jininta hawa, kuma idan abin yaci gaba bama fata amma ze iya shafar zuciyarta ko ta kamu da ciwon damuwa (Depression).
Amma Alhaji a shekarun ta wane abu ne ya dameta haka da har yake barazana da rayuwarta?"

Abba da tashin hankalin sa ya nunku, Umaimah keda hawan jini a yan shekarun ta da basu wuce Ashirin da daya? ba yanzu bazata samawa kanta salama a rayuwa ba kullum daga wannan matsalar ta kau wata zata kunno kai shi yama rasa abinda zeyi akan lamarin Umaimah.

Yanzu dai Alhaji zamuyi iya qoqarin gurin bata kulawar data kamata sauran aiki kuma yana gurinku, dole kuyi qoqarin sanin damuwarta domin a maganceta amma fa cikin rarrashi bada fada, Allah ya bata lafiya" Likitan ya sake fada kafin ya turawa Abban takadda dayayi rubuce rubuce akai yace yaje gurin biyan kudi da kuma pharmacy a karbi magani. Godiya yayi masa jiki a sanyaye ya tashi ya fita.

Salman ya bawa takardar da katin bankinsa yaje ya biya kudin sannan ya kira Mama ya shaida mata abinda ake ciki, "Allah ya bata lafiya tace" sukayi sallama, Abban na shirin tafiya saboda ana jiransa zasuje Gumel wata Gaisuwa ta Abokinsu sega Anty Laure qanwar Mama nan tazo???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?, nan suka barta suka wuce shida Anty Saratu da take son zuwa ta debo abubuwan da zasu buqata.

Sanda ta koma gidan yaran sun dawo daga makarantar Asuba, da yake weekend har Sharifa da Abida yammatan ta sun qarasa abin karin sunci tunda Su Nazifi sun gaya musu sunje Asibiti ne, su ta barwa girkin rana ta gaya musu idan sun gama su kai Asibitin kafin ta debarwa Umaimah duk abinda tasan zata buqata ta sake komawa Asibin har sannan Umaiman bata farka ba, Anty Laure dai tace mata ta farka tana surutai aka qarayi mata wata allurar baccin.

Khalil
A bangaren Khalil kuwa kasa zama yayi a office din, yana tsaye daya daga cikin ma'aikatan sashin su ta shiga office din Balaraba tasha gayu se yauqi takeyi, tuntuni ya gane abinda take nufi dashi amma ko a fuska be taba nuna mata ya fahimceta ba, za dai su gaisa idan aiki ya hada su suyi amma ya qi bata qofar da zata gabatar masa da qudirinsa.

Yanzun ma yana cikin wannan hali na tashin hankali da rudu ta shigo tana karairaya ta zauna a kurar dake gaban office din,
"Architect ashe ka shigo banga wuce warka ba kuma yau na shigo da wuri" ta fada tana fari da ido,
"Uhm" kawai ya iya ce mata dan bashi da nutsuwar jan wata magana a yanzu, seta sake gyara zama tana narke fuska tace

"Ni na rasa yanda akayi so ya zama laifi Khalil, tunda ka fahimci ina sonka shi kenan ko kallo me daraja na dena

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login