Showing 78001 words to 81000 words out of 429394 words

Chapter 27 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

1005

Khalil daya zama mara amfani na wani lokaci ta sakar masa kukan zallar shagwaba da kissa.
Fitinannan Qamshin ta ya kai masa ziyara, qafafunsa sunyi sanyin da bazasu iya daukarsu ba se yayi saurin dafe bango da hannu daya ya riqeta gam a jikinsa da daya hannun ya gagara ce mata komai se ajiyar zuciya yake saki kamar Jaririn daya kwana besha Nono ba.

Qasa ta tafi zata tsugunna ya yi yunqurin tarota ta zame seda ta ajiye guiwoyinta a qasa ta dafa nasa da hannu biyu hawaye na bin fuskarta tace
"Bazan iya cigaba da jure fushinka ba Khalil na tuba ka yafe min, nayi nadamar duk abinda na aikata maka a kuma shirye nake da karbar duk wani hukunci daga gareka amma banda na qaurace mun, Allah kadai yasan irin quncin dana shiga na rashinka. Muna rayuwa guri daya amma ka nesanta kanka dani baka san yanda nakeji ba

Kuma Wallahi duk abinda ya faru sharrin shaidan ne yayi amfani da tarin sonka da kishinka da nakeyi ya makantar dani amma yanzu na fita daga cikin duhu na dawo haske, in sha Allahu bazan sake kwatanta makamancin abinda ya faru ba bazan sake ba, ka yafe mun kaji Ibbahna, mu koma rayuwar mu irin tada me cike da qauna da Aminci".

Shiru yayi kawai yana kallonta, yanda take maganar har akan fuskarta yana iya karantar gaskiyar zuciyarta da kuma nadamar da tayi amma fa Umaimah ce, yanzu shi ai sedai ya bawa wani labarin halinta badai a bashi ba dukda haka yana fatan Allah yasa da gaske take ta gane gaskiya dan ya tabbatar da yafita Azabtuwa da wannan zaman da sukayi, kawai ya jure ne saboda ya nuna mata kuskurenta kuma Alhamdulillahi gashi nan yaci nasara amma dukda haka bazeyi saurin bada kai bori ya hau ba, dole ya sake shata mata wasu sharuddan in har Nadamar ta gaske ce kuma ta shirya suyi zaman lafiya zata bi.

Hannu biyu ya saka ya dagota daga durqushen har sannan bata dena tsiyayar hawaye ba, cikin palour ya qarasa shiga ya zaunar dasu akan kujera daya ya kama hannayenta duka biyu yana fuskantarta, kallon cikin ido yayi mata Umaimah dake kallonsa itama tayi saurin sadda kanta qasa, cikin kasalalliyar murya wadda halin da yake ciki da kuma Dramar Umaimah suka haddasa masa yace mata

"Look at me Umaimah, i want you to look in to my eyes while I'm talking. Bana so kice baki ji ba ko ki manta wani abu da zan fada".

Hannunta ta saka ta share hawayenta kafin ta dago idanunta da suka canza kala saboda kuka ta kalle shi itama, a tare suka sauke ajiyar zuciya, ya matsa hannunta dake cikin nasa yace

"Ina sonki Umaimah irin son da bazan iya misalta miki shiba amma a kullum halayyarki tana goge wani kaso daga cikin son da nake miki, Umaimah yazo Mana a cikin Hadisi Manzon Allah SAW yace 'Jublatul qulubi ala hubbi man ahsana ilaiha, wa bugudu man aasaha ialihi'. Ita zuciya da kike gani an halicceta akan son me kyautata mata haka kuma tana qin duk wanda yake munana mata ko dabba ki ka kalla yafi zuwa gurin wanda yake bashi abinci yake kyautata masa ballantana mutum.

Ina tsoron kar wata rana a waye gari tarin soyayyar da nake yi miki ta shafe gaba daya saboda a kulle halayenki marasa kyau suna rinjayar na kirkin akan sikelina.
Soyayya ita ce gadar da take kaiwa ga aure amma kyawawan dabi'u su suke zaunar dashi kuma girmamawa da mutunta juna dolene a cikin aure bawai zabi bane.

Idan ma wasu kike kwaikwayo ko suke doraki akan hanyar da bazata bulle ba qarshe zakiyi batan baqatantan babu nan babu can dan haka tun wuri ki farka dan nasan wannan ba tarbiyyar gidan ku bace, ba itace tarbiyyar da nayi sha'awa har ta kaini ga auranki ba ce wata ce daban kika aro a gurin wadanda suke zama irin zaman bariki, mace ta zagi mijinta idan ta kama ya daketa kuma gobe suci gaba da zama har suyi dariya toh ni bazanyi irin wannan zaman dake ba, idan kuma shi kika zaba kamar yanda kika gani a yanzu na fara zan fita daga sabgarki in barmi kiyi rayuwarki ke kadai nima nayi tawa saboda hakan ze fi samar mun da zaman lafiya da kwanciyar hankali".

Cikin nutsuwa da kwantar da murya yake maganarsa ta yanda duk taurin kan wanda akeyiwa seya saurara kafin ya gama kuwa jikin ta qaura yayi la'asar liqis ta sunkuyar da kai qasa kamar gaske tana matsar kwalla.

Qara kama hannunta yayi yaci gaba da cewa
"Dan Allah Umaimah ki kwantar da hankalinki mu zauna lafiya kamar kowanne ma'aurata. Wallahi banida burin sake sako wata mace a cikin rayuwata bayanke, inasonki, ina son komai naki yayi mun irin macen da nake so na qare rayuwata da ita idan kika cire Jidalinki shikadai ne fargabata a kullum na aure ki saboda ina sonki ina son zama dake amma sam kin gaza bani kwanciyar hankalin da nake kwadayi a tare dake.

Idan naji dadinki na kwana daya se nayi fama da tashin hankalinki na sati a haka kike so na zauna dake ke kadai?
Idan aka ci gaba a haka baki tunanin wata rana zan nemi inda zan ringa samun nutsuwa da kwanciyar hankalin dana rasa a tattare dake?
Umaimah kwalliya, girki, gyaran gida ko gamsuwa a gado ba su kadai ne jindadin aure ba da akwai Nutsuwar zuciya wadda duk irin jin dadin da kake ciki idan baka da ita bazaka taba samun yanda kake so ba daga ni har ke abinda muka rasa kenan kuma kece sila.

Kullum zuciyarki da tunaninki yana kan kar wata ta kulani karna kalli wata, idan akasi ya gifta wani abu ya faru kin ringa tashin hankali kenan kina bori duk akan me azatonki hakan ne ze hanani kula mata ko qara aure duk sanda naga dama? Toh ki sani wannan halin naki tamkar kina ingizani ne zuwa ga wasun kuma duk ranar da kika kaini qarshe sedai kiji ana cewa ki matsa za'a shigo da Amarya idan yaso ki kashe mu duka kamar yanda kika sha fada kinga munyi shahada ke kuma kinyi dakon zunubi dan babu wanda ze hanani qara aure idan na tashiyi hujjar tayar mun da hankali kadai da kikeyi kullum ta isheni in qara aure kuma kowa ze goyi bayana da babu wanda besan Halinki ba idan kika cire Hajiyata amma kowa yasan Umaimah danja ce duk abinda akace kinyi za'a yarda da wanda yafishi ma duk saboda me"

Kuka ta fashe dashi me sauti tana kallonsa, idan yasan irin wutar da take ruruwa a zuciyarta da be fara kawo zancen qarin aure ko makamancinsa a hirar su ba, amma ya zatayi ko wutar zata cinyeta yau dole ta hadiye kodan ta samu su sasanta dan ita da kanta bangaren kwakwalwarta me hankali ya mata karatun ta nutsu kuma ta yarda da duk abinda yake fada za kuma ta zage dantse in Allah ya yarda kwanciyar hankali ya samu gurin zama a gidansu tunda dai yace tijararta bazata hana ya mata kishiya ba toh kuwa zaman lafiya ze hana.

Cikin kuka tace masa
"Duk naji na kuma karbi laifina ina roqonka daka yafe mun bana so Allah ya kamani da laifin bata maka rai"

"Ni ban taba riqeki a zuciyata ba, a kullum ina miki addu'ar Allah ya shiryaki yasa ki gane abinda kikeyi ba daidai bane kuma duk abinda kikayi mun na yafe har wanda ma bakiyi ba kafin yazo na rigada nayi clearing nasu" ya fada yana dan murmushi da sake janyota jikinsa.

"Nagode, kuma ka gaya mun duk abinda kake so na dena zan bari indai hakan ze saka ka huce kuma kayi farinciki" ta sake fada tana shigewa jikinta, seya dora bakinsa akan kunnenta ya sakar mata kiss me qara da seda ta zabura ta kalleshi tana bata fuska, shima bata fuskar yayi yace

"Wannan Chatting din dayake dauke miki hankali bana sonsa, bance ki dena kwata kwata ba amma kisan yanda zaki raba lokacinki ya zamana kinada lokacina dana sauran ayyukan da suke a gabanki ba danna waya ba"

"Se kuma me?" Ta fada tana kallonsa, ya daga kai kamar me tunani sannan yace
"Shikenan".
Wayarta ta janyo ta bude, Khalil ya tsaya yana kallonta ta shiga cikin WhatsApp kai tsaye tayi deleting account din kafin tayi uninstalling nasa gaba daya daga kan wayar ta miqa masa tana cewa

"Gashinan na goge gaba daya ma saboda kar na barshi ya ringa dauke mun hankali"

"Nifa bance ki goge ba, idan kuma ina so muyi video call in bana nan fa ko zaki turamun da pictures.."

"Nidai bana so tunda dai baka sonsa, shikenan mun shirya ko?" ta fada cikin shawagwaba bata ida maganar ba Ya saka hannu biyu ya kama qugunta ya qara matsota jikinsa sosai kafin ya shiga aika mata da kiss cikin kwarewa, ya kwashe kusan minti goma yana kissing nata kafin ya saketa jikinta yayi mugun sanyi saboda wata fitinanniyar kewarsa data taso mata.

"Yunwa nakeji, tunda na shigo nake jin qamshin abinci me kika dafa" Khalil ya fada yana janyewa daga jikinta kamar beyi komai ba dukda shikansa qarfin haline kawai ba amma ba qaramin ruwa ya kunnowa kansa ba, kuma yana gudun ciwon daya ji mata kwanaki ya warke koda saura.

Kukan sangarta ta saka masa ta fada jikinsa tana qoqarin sake hade bakinsu ya riqeta yana cewa

"No Umaimah bakida lafiya kuma Dr tace se kinyi two months kina hutuwa" ya fada harga zuciyarsa dagaske ya dauka se tayi wata biyun kamar yanda likita tace dan ya tsorata da hukuncin nasa ya kuma yi nadama da alqawarin baze sake hakke mata yana cikin fushi ba.

Kamar zata shige masa ciki ta qanqameshi tana cewa
"Ni na warke ka duba ma ka gani, please Ibbah i miss you badly" ta qarsa tana hade bakinsu ta shiga bashi haddar karatun daya dade yana dora mata

"Innalillahi yarinyar nan zata kasheni" Khalil ya fada a zuciyarsa jin Umaiman tasa tana masa wasu abubuwa da ko a hasashe be taba zaton ta iya su ballantana tayi masa, ashedai ba Jidali kadai ta iya ba ita din ta kowanne fanni gwanace.

Dakyar suka rabu shima seda sukaji an kwada kiran sallar Magriba a masallatai. Kallonta kawai yake yana sakin murmushi kamar wani wawa dan kuwa yau din ta shayar dashi mamaki ba kadan ba. Ita ya sakarwa filin tayi sukuwa son ranta soyayya iri iri babu wacce be gani ba seda komai ya lafa kuma ta juya ta hade da kujera yanda kasan wadda Siriki ya rutsa.

"Wai dan Allah Babe course kika je kikayo ne ko yaya ni bangane wannan al'amari ba ya daliba take neman tafi Malamin hazaqa ne?" ya fada yana kama qugunta tareda leqa fuskarta data kife a kan kujera, seta zabura saboda yanda taji ruqon nasa har tsakiyar kanta ya kwanto ta jikinsa gaba daya yana shafata yace

"Kidena zabura haka fa kina mantawa bake kadai bace yanzu ko?"
Kwacewa tayi ta yayimi Rigar shaddar daya cire ta rufe jikinta, ta dai fi babu ta miqe tsaye Khalil kuwa qara kwanciya yayi yana qare mata kallo yanda Albarkatun jikinta suka qara cika taf gaba da bayan nan masha Allah a fuska ne kadai zaka ga ramar da tayi, tafiya tayi kamar zata kife yayi saurin ruqota ta sakar masa harara tana cewa

"An sakawa mutane ido se sunje sun fadi"
"Ya akayi kika san ana kallonki, daman baya tana da ido ne?" Ya fada yana mintsinin mazaunanta ta fada qara ta kai masa duka sallamar daya jiyo daga masallaci alamar an idar da sallah ta saka shi miqewa da sauri yana salati.

"Kingani kin saka na rasa jam'i ko"
Baki ta tura ta sake nada rigar a jikinta tana janta qasa dan tadan qara rufe mata jiki ta shige daki tabar Khalil na mata waqar sittin saba'in, idan yana wani shaqiyancin kawai mamaki yake bata dan kafin suyi aure tsaf in aka ce zeyi zata rantse baze iya ba saboda yanda yake shiru babu ruwansa.

A dakinta tayi wanka ta gasa jikinta sosai da ruwan dumi, seda tayi sallar Ishah kafin ta shirya cikin wata Armless top da Three quater dan tun tana sallahr magriba taji fitar Khalil.

Palour ta fito ya tattare komai ya gyara kayansu da pillows din da suka watsar, kan Dining ta wuce saboda yunwar data taso mata kamar zata fadi, ita nata kalar laulayin kenan ci kamar gara se kuma wani lokacin ta rasa me yake mata dadi bayan wannan babu wani abu da yake damunta.

Abincin ta zuba soyayar shinkafa data ji niqaqqen nama ta janyo kwanon da ta zuba Salad ta tsiyaya dressing din akai ta juya kafin ta dibi wanda ze isheta ta rufe sauran dan tasan duk inda yake shima yana hanyar gida, tana kai lomar farko taji an bude Get, seta miqe ta dauki Qaramin mayafin data ajiye akan kujera ta yane kanta ta fita har ya shigo da mota ta qarasa ta kulle Get din tana masa sannu da zuwa.

"Yawwa Malama Umaimah sannunki" ya fada yana mata dariyar data rasa ta mecece,
"Yau kuma Malama na zama" ta mayar masa sanda suka shiga cikin palour, Jakar Laptop dinsa daya dakko ya miqa mata yana cewa

"Yau ai ko makaranta na kiraki kin wuce nan hajjaju, bari nayi sauri naci abinci muje a doramun sabon darasi dan ina buqatar qarin ilimi sosai nima" ya qarasa yana kashe mata ido daya, se sannan ta fuskanci inda ya dosa seta juya kawai ta wuce dakinsa a ranta tana mamakin Khalil, ahidai bashi da damuwa sabgar gabansa kawai yake ji fa ko kunyarta baya ji yake wannan magana toh Allah ya shirya.

Tare suka ci abincinsu cikin nutsuwa suna yan hiraraki, babu abinda yakai zaman lafiya dadi a rayuwa, basu ba hatta da gidan kansa yasan an samu daidaito a cikinsa saboda yanda suka koma sabgoginsu yanda suka saba. Bayan sun gama cin abincin suka buga Tv game seda Abin ya kusa zama rigima dan har ta fara kukan wai wayo yake mata yana mata Game over kafin ya kashe suka kwanta bayan an qara dora karatu sadara biyu.

Kwanakin da suka biyo baya kam se sambarka dan zaman lafiya dai ya samu guri yayi daram a gidan Khalil da Umaimah. Tattalin junansu sukeyi, idan ya fita har ya dawo suna maqale a waya. Wanka da kwalliya kuwa se wanda ta manta dan sosai take tashin kan Khalil da gayu na safe kafin ya fita daban na dare idan ya dawo daban ga karatun makarantar dare da take dora masa babu sassauci gaba daya ta rigada ta shagwaba Khalil din nata ji yake nan duniya kamar babu Namijin da ya kaishi sa'ar Mata itama kuma hakan take a bangarenta dan kuwa Khalil ya isa Namijin kere Sa'a.

Idan yayi kwalliya ze fita aiki ji takeyi kamar ta saka masa Niqab saboda kishinsa da takeyi na nan babu inda yaje a zuciyarta tana dai qoqari matuqa gurin ganin ta kawar da idonta akan duk abinda ze kawo tashin hankali a tsakaninsu.

Tsakaninta da maqotanta kuwa sedai idan sa'a ta gifta ta fita unguwa ko tayi baqi ta rakasu su hadu su gaisa dan ko barkar Rufaida bata samu ta shiga ba kuma tana da yaqinin yanzu tayi Arba'in koma fiye da haka dukda taji a bakin Khalil cewar bata nan, Mijin ze tafi wani aiki Kudu yace ta koma gida kafin ya dawo wai a Masallaci suka hadu yake gaya masa shiyasa ta bari se taji ta dawo zata shiga.

Wata safiyar Talata bayan Khalil ya gama shirinsa ze fita take ce masa tana so taje kitso.
"Wayon kije gida ne kina dai ji wancan zuwan da mukayi Mama tace kar ta sake ganin qafarki a gida se an nemeki shine ko sati ba'ayi ba zakice zaki kitso" Khalil dake daura agogo ya fada yana kallon fuskarta data fara canzawa saboda cikin daya bi jikinta. A lissafi wata na biyar yake yanzu amma sam babu alamar sa sedai qibar datayi ta ko ina har fuskar Allah ya taimaketa dai dogon hancin be kai ga bajewa ba.

"Dadin Iyaye da yawa kenan ai kaga iata Mama korata takeyi idan naje ita kuwa Hajiyata nasan bataqi kullum naje na wuni a gidan ba kai kuma saboda jelousy baka so ka kaini" ta bashi amsa tana masa fari da ido.

"Ke dince ai na rasa me kikewa Hajiya haka kullum bata da zance se naki komai ta samu tace a kawo miki shiyasa idan banyi dagaske ba kwacemun ita zakiyi"

"Toh ai kaima ka kwacemun Mamata ka shiga tsakaninmu,? ina murna Nuratu ta matsa zan kwato fada ta se ga sabon snatcher yanzu magana indai bakai ka fada ba komai na gaya mata bata yarda, kaga shikenan munyi 1-1, na kwace Hajiya ka kwace Mama" ta bashi amsa tana dariya,

"Yawwa na tuna yau irin Cream cheese maccaroni nan ta ranar zakiyi mun" Khalil ya fada, seta dan yamutsa fuska, shidai yana son shegun continental dishes din nan da ba dadi ne dasu ba, be kuma fahimci duk randa yaga ireirensu toh Maman Asad ta kawo mata ziyara ita ce gwanar girki ita takeyi mata amma dai tana ga dole ta ajiye quiya ta koya saboda ranar yar qure tunda gashi an fara da kansa yace tayi masa.

"Idan bazaki iya ba ki barshi naga kina ta bata fuska a sharrinki yanzu se kice ze saka ki Amai" ya fada yana daga hannu sama fuskarsa da murmushi dan sabon salon iyashegen data samo kenan, Allah ya yaye mata be dora mata ciki me laulayi ba amma se kalato shi takeyi. Idan batayi niyya ba shara se tace idan tayi Amai zata sakat sedai shi ya share balle girki yanzu kullum suna kan hanyar zuwa gidan Hajiya cin abincin dare dan tunda akaje Restaurant ranar nan wata classy babe ta biyo Khalil akan ya bata number sa aka kusa kwasar yan kallo Allah dai ya taqaita shikenan ya yaye wa kansa fita da ita. Yaje shikadai din ma tace bata yarda ba dan bata san me zeje yayi ba yanzu suda abincin waje sedai suyo order a musu delivery toh ya za'ayi zaman lafiya ai yafi zama dan sarki tubda outing din ba dole bane.

"Anjima zan fito na duba, akwai yaran da sukeyin ball a qofar gidan

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login