Showing 249001 words to 252000 words out of 429394 words

Chapter 84 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

1047

Kwanan nan ma da sukaje yiwa Hajiyar murnat sabon gida seda ta tambayi Habiba Mu'ayyad din tace yana gidansu Umaimah a sannan basu rigada sun tare ba ita yanzun ma seda tayi noyyar tambayar Khalil din kawai yanda ya hade rai ne yasa ta kasa masa magana se wani muzurai yakeyi kamat wanda akayiwa laifi.

Khalil kuwa be qarasa gida ba kusan goma da rabi dan ya tsaya ya siyawa su Umaimah Gasashshen nama data ce ya taho musu dashi da fura. Hajiya ya fara kaiwa nasu har sun kwanta Habiba ta karba ta saka a Fridge yaran ma sunyi bacci kafin ya wuce part dinsu. A falon qasa ya tarar da Umaiman tana kallon wani hausa film a Arewa 24. Tayi masa sannu da zuwa bayan ta karbi ledojin daya shigo dasu ta wuce kitchen shi kuma ya hau sama dan yayi wanka. Sanda ya sako harta sake dumama Naman a Micro wave ta zuba a plate tana zaune tana shan fura ya zauna kusada ita ta miqa masa furar yace Aa a qoshe yake shi yaci tuwo a gidan Mama.

Hira sukeyi dukda rabin hankalinta nakan kallon da takeyi seya tashi ya shiga kitchen ya dora qaramar tukunya akan Gas bayan ya zuba Spices din Shayi ya kunna. Yana tsaye yana jiran ruwan ya tafasa, haka kawai ta fado masa a rai, a cikin kansa yake jin muryarta me sanyi tana masa yawo yaja tsaki to akan me ze wani ringa tuna yarinyar kuma.

A Mug ya juye ruwan bayan ya tasafa ya zuba sugar cubes ya koma falon, Umaimah data gama cin Namanta da fura ta hada sauran zata kai kitchen din ya fito se ya karbi farantin naman ta wuce ciki ta ajiye sauran kowanne a muhallinsa. Kadan yaci Naman ya shanye shayin gaba daya ji yake kansa yana neman yayi masa ciwo saboda wani tunanin shirme da kwakwalwarsa take kawo masa na yarinyar, meye hadin sa da ita da zata ringa fado masa a rai haka kawai saboda son ta hana shi sukuni. Har sukaje kwanciya ya rasa abinda yake masa dadi lokaci lokaci yakan saki tsaki Umaimah dake saka rigar bacci ta kalle shi tace
"Wai nikam lafiya kake ta tsaki kai kadai"?

Tsakin ya kumayi kafin ya nufi bandaki yana ce mata babu komai. Bata tsawwala ba dan yanzu kaffa kaffa take da duk abinda ze saka ya sake birkice mata. Tana kwanciya ko minti biyar batayi ba bacci ya dauke dan yanzu haka take data aje haqarqarinta a qasa bacci ze kwasheta har mamakin irin wannan bacci haka takeyi.

Khalil kuwa bayan yayi wanka ya kwanta sam barci ya gagara zuwar masa. Abin daga haushi se ya koma bashi Mamaki irin yanda haka kawai yarinya ke neman shiga rayuwarsa ta hanashi zaman lafiya.
Tsaki ya sake ja a karo na babu Adadi ya juya kwanciyarsa yana rufe ido, hotonta ya gani sanda ta fito babu Hijabi a jikinta. Doguwar qirar jikinta da babu wani abu da zece ya rudeshi da har ze saka ya ringa tunaninta tanayi masa gizo se ya miqe ya wuce bandaki ya dauro Alwala ganin ya kasa bacci.

Nafila yayi tayi har seda bacci yaci qarfinsa kafin ya kwanta. Da Asuba dakyar ya iya farkawa daga baccin da yake cike da mafarkin Humairah. Zuwa yanzu lamarinya ya fara bashi tsoro tunani yakeyi anya ba Mayya bace yarinyar take neman lashe masa kurwa? Idanba haka ba meye darin gaminsu da zata zo masa a mafarki, to koma dai yaya ne yafi qarfinta ba zata ci galaba akansa ba ze kuma sake dagewa sa Addu'a da kuma neman magani yana zaman zamansa Mansur ya ja masa ko a ina ma suka samota oho dan ya ya tabbatar duk yanda akayi suma basu san Mayyar bace shiyasa suke zaune da ita.

Haka yaje ya dawo daga masallaci yana ta ta'ajibin lamarin Humaira a ransa. Bacci ya sake komawa dan rashin kwanciya da wurin da beyi ba ya saka baccin be ishe shi ba. Da yake Asabarce ne tashi da wuri ba har gurin goma na safe. Umaimah bata dakin sanda ya farka ya dai ji qamshin turarukanta alamar anan tayi wanka ta shirya dan haka shima yayi wankan yana Jin cikinsa na qugin neman abinci. Falo ya fito, nan ya tarar da Mu'ayyad da Bibi suna cin Doya da Ketchup suka tashi da gudu suka fada jikinsa ya dagata sama ya riqe hannun Mu'ayyad din suka koma inda suka tashi.

A tare suka gaida shi ya amsa yana tambayarsu Umaimah Mu'ayyad yace masa tana gurin Hajiya. Da kansa ya sauka qasa ya debo abin karyawa ya dawo suka qarasa da yaran.
"Dady yau kacewa Anty Habiba ta kaini gidansu Humairah" Bibi data kwanta a jikinsa ta fada. Wani duka qirjinsa yayi jin sunan data ambata. Idan be manta ba haka yaji Hajiya ta kirata jiya nan take tunanin yarinyar da yayi yaqi dashi dakyar ya sake bijiro masa. Maganar da Mu'ayyad yakeyi ce ta dawo dashi daga tunanin daya tafi yana cewa

"Dady itafa Humairan bata zuwa nan gidan sw Bibi ce kullum zata ce akaita shine Anty Habiba tace itama ta dena zuwa gidansu".
Rigima Bibin ta saka akan se an kaita gidansu Humairan, sunan kadai da take ta maimaitawa faduwar gaba yake haifar masa. Umaimah ta shigo ta tarar dasu ita ta lallabata akan ta bari seda yamma akaita gidansu qawar tata yanzu basa nan da haka suka tattara suka wuce bangaren Hajiya.

Kallon Khalil tayi da sam beyi kama da wanda yake tareda su ba, seda ta taba hannunsa kafin yayi firgigit kamar wanda ya farka daga bacci yana zare iso dan gaba daya wani tunani yakeyi da idan an rutsashi bazece ga abinda yake tunanowa ba.
"Lafiya dai Abban Mu'ayyad, ko wani abu yana damunka?" Umaiman ta fada tana tsare shi da ido. Gefe ya kalla ya ce mata

"Lafiya lau. Me kika gani?" Se ta sake zura masa ido tana qoqarin gano dagaske lafiyar yake ko akasin haka. Tun da Asuba ta lura kamar baya cikin nutsuwa haka daya koma bacci yanda ya ringa juyi har yana wasu surutai da bata gane abinda yake fada ya sake gasgata mata cewar bashi da lafiyar dan haka takai hannunta jikinsa tana cewa
"Yanayinka ya nuna baka jin dadi, ko zazzabi kakeyi? Ya kamata kaje Asibiti kasan dai ciwonka yanda yakeyi maka babu dadi gara ka tareshi tunda wuri".

Hannun da take taba wuyansa ya janye yana miqewa tsaye yace
"Keni lafiyata qalau fa wane irin zazzabi ana zaune qalau" seda yayi gaba se kuma ya waigo yana kallonta yace
"Yaushe ne naga kuna hayaqi keda yara kika ce na miyagune? Idan yana kusa dan kawo mun nima na turara".

Dariyar da bata shiryawa bace ta kwace mata ta shiga qyaqyatata babu ji babu gani har tana zamowa daga kan kurar da take. Khalil ya shaqa yayi fam yana kallonta, to meye abin dariya kuma daga cewa ta bashi hayaqin Miyagu se kace wanda yace wani abu daban. Cikin bacin rai ya kalleta yace
"Meye haka daga tambaya zaki tasani gaba kina mun dariya kamar wani mara hankali".

Seda ta hadiye dariyar dukda haka bakinta a washe tace
"To ai kaine da abin dariya, yau kuma da bakinka kake neman maganin Miyagu a ina kukayi arangama Allah sa ba a yawon zuwa Jeji Site suka qwamusheka ba. Ashe shiyasa jiya ka ringa surutai a bacci ai dana sani tun a sannan zan banka maka hayaqin suyi ta kansu" ta qarasa tana fashewa da wata dariyar. Tsaki yaja saboda takaici ba tareda ya sake ce mata komai ba ya shige daki abinsa. Tunani yakeyi da tace yayi surutai gaskiya ne ko wasa take masa? Amma dai koma yayin da gaske yasan ba abinda yake gani a mafarkin ne ya fada a zahiri ba dan idan haka, da yanzu ba dariya takeyi ba qila tashin hankali suke kwasa.

Ranar haka suka wuni tana zolayarsa daya gaji ya fice ya bar mata gidan. Ta isheshi da magana ga uban hayaqi data bulbulo ta kawo masa harda dakko bargo wai ya rufa abin yafi ratsa shi. Haka ko ya biye mata yayi hayaqin dan harga Allah ya gama yarda da cewar Humairan mayya ce dan wallahi har gizo take masa yana ganin suffarta na giftawa a gidan. Sau kusan uku yana daukar waya da niyyar kiran Mansur akan yaji salsalar wacece ita ya kuma tambayeshi ko yasan suna da alaqa da Maita se ya kasa. Tsoro yake kar magana ta koma mata ta qarashi cinyeshi a dare daya qila ta hada harda Mansur din dan dai shi ya tabbatar da ba yar uwarsu bace wannan be kuma san inda suka kwasota ba. Yasan kusan dangin Mansur kaf na uwa da Uba, Bare barine baqaqe ita kuma wannan gata nan kamar Zabiya daman tunda yaga kyanta yayi yawa yasan da walakin wai goro a Miya.






*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* =?L?
Page 58

Wasa wasa tunanin Humairah ya samu gurin zama a zuciyar Khalil. Haka kawai take fado masa, dan shi hayaqin da Umaimah ta samu nayi tana faman banka masa a maimakon ta sakar masa kurwa ma qara damqe ta tayi. Cikin qasa da sati biyu tsabar tunaninta har rama yayi abinda yasa hankalin Umaimah ya fara tashi kenan harta kasa daurewa ta sanarwa da Hajiya halin da ake ciki dan da gaske ta yarda da cewar Mayun ne suka kama mata Miji. Hankalin Hajiya ya tashi itama, babu shiri ta bazama karbo masa rubutu dasu hayaqi a cewarta babu wasu Mayu sedai Mahassada da masu kambun baka ne suke neman sakashi a gaba saboda daukakar da Allah ya kawo masa.

Khalil kuwa jinsu kawai yakeyi dan zuwa sannan lamarin tsoro yake bashi da gaske. Babu ranar Allah da ze kwanta ba tareda yayi mafarkin Yarinyar ba, kuma mafarki me nutsuwa dan wata rayuwa yake ganin suna shimfidawa irin wadda ko a sanda yake zirgillin Son Umaimah be hasaso musu irinta ba wannan dalili yasa ya qara mata Matsayi daga Mayya zuwa Aljana. Ya yarda kawai waddaya gani a Gidan su Mansur ba itace ainihin mutum dinba. Aljana ce ta bishi gidan ta samu damar dabaibaye tunaninsa ta jikin Humairan.

Da wuri ranar ya tashi aiki dan baya jin dadin jikinsa da baze fita bama to da akwai wasu takaddu daya taho dasu gida jiya kuma a ranar zasu aika dasu ???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?wani waje shiyasa ya fita. Yana tafe akan Titi kamar bayason tuqin da yakeyi, gaba daya tunaninsa ya rabu gida biyu. Da niyyar tafiya gida ya kwanta ya baro office amma kuma se gani yayi ya dauki hanyar gidansu Mansur. Wani mugun Azalzalarsa zuciyarsa takeyi tun kusan kwana biyu yakejin yana son sake ganin yarinyar. Magana yake so suyi dan ya fuskanci wace kalar mutumce ita kafin ya dauki Matakin gaggawa saboda nema take ta zauta shi. Sau biyu yana kuskuren kiran Sunan wasu da nata gara yayiwa tufkar hanci ya roqeta ta fita daga rayuwarsa tun abu be tabarbare ba.

Seda ya kai qofar gidan kafin ya tsaya kuma yana tunanin idan ya shiga me zecewa Maman? Bama wannan ba yana iya cewa gaidata yazo to ita kuma yarinyar ta yaya har ze samu damar magana da ita dan bayaso Maman tasan abinda ya kawo shi. Rasa mafita yayi wata zuciyar na gaya masa ya juya kawai yaci gaba da binta da Li'ilafi inda zuciyar dake mararin ganinta ta hana faruwar hakan dole ya saduda ya balle murfin motar ya fita Habibu dake zaune da Abokanan sa a Majalisa yana hangoshi ya taso dan daman tun tsayuwar motar yake kallonta kamar ta Khalil din amma beyi gaggawar tashi ba.

Cikin girmamawa ya gaida shi ya amsa yana tambayarsa makaranta yace masa yazo kawo SIWES letter nr gobr zero koma Dutsin Ma din. Tare suka shiga gidan. A falon Mama ya zauna Habibu ya wuce dakinta da niyyar ya kirata sukaci karo da Humairah dake shirin fitowa itama taci kwalliya kamar me shirin zuwa Biki.
"Ke ina Mama?" Habibun ya fada yana kallonta, cikin nutsuwarta tace
"Ta shiga gidan Hajiya Asabe, Anty Ummi ce ta haihu an dawo da ita gida nima can zanje tace idan na gama abinda nakeyi bata dawo ba na bita".

Kallonta yayi sama da qasa kafin yace
"Shine kika ci uban kwalliya haka ke zaki gidan surukai ko?"
Mayafin jikinta taja ta rufe fuskarta tana murmushi irin taji kunya kafin tace
"Kai Yaya wanka fa kawai nayi ko so kake na fita busu busu dani?"

"Yarinya in ma zaki dawo daga rakiyar wannan Cima zaunen tun wuri kiyi ga mutanen kirki nan suna Sonki kin zauna kina batawa kanki lokaci akan wanda bashi da Future" Habibu ya fada yana juyowa ya dawo gurin da Khalil ke zaune.

Humaira ko yanda kasan wadda Habibun ya durawa Iyayenta Ashar haka ta bishi da kallo kafin kace me hawaye sun fara zarya akan fuskarta. Khalil da tun fitiwarta yake kallonta yana kuma sauraran duk abinda suke cewa wata irin faduwar gaba yaji sanda Habibun yake zancen tana bata lojacinta akan wani bayan ga masu sonta da gaske, ji yayi kamar an kwada masa guduma maganar ta dake shi sosai kafin ya farfado kuma hawayen da ya gani suna sunturi a fuskarta suka sake jefa Zuciyarsa cikin wani yanayi.
"Yah Ilahi me yake shirin faruwa dani ne akan wannan yarinyar?" Ya jefawa kansa tambayar da babu me bashi amsa.

Maganar Habibu daya ajiye masa ruwa da Lemo ta dawo dashi daga kallon daya raka Humaira dashi se sharar hawaye take kamar wadda Habibu ya mara.
"Mamakin shagawabarta kake ko Yaya? Haka take fa yarinyar nan kallonta kayi idan taso sharri seta saka maka kuka dan ma Mama bata nan da yanzu ta hau sababi an taba mata Marainiya se kace akanta aka fara rasa Iyaye".

Maida kallonsa yayi kan Habibun yace
"Wacece ita?" Se Habibu ya zauna akan kujera yace
"Yar gidan Baba Sani ce Qanin Mama na Jalingo, kasan ya dade da rasuwa da Mamanta tayi aure ta maida ta gurin Hajiya ita kuma kasan ba Lafiya ta cika ba shine Mama ta dakkota bata fi shekara biyu a nan din bama itama Maman tata ta rasu, shikenan fa Mama ta dauki Son duniya ta dora mata ni da nake Autan ma ta kwace mun Matsayi se yanda tace a gidan nan Mama takeyi idan kuwa kana so kaga bacin ran Mama ka taba Humairah shiyasa ta daure mata gindi take son ranta a gidan nan".

A duk surutan Habibun babu abinda ya tsinta se Kalmar Marainiya data rasa uwa da Uba. Wani Tausayinta yaji ya masa rubdugu ya kanainayeshi. Tun Asalinsa shi daman me tausayin Marayune, ya taso cikin gata ya rasa Mahaifi sannan ya dandana dacin wannan rashin Mahaifin shiyasa idan yaga Maraya yake tausaya masa to sedai ita tausayin nata a na daban ya fado masa. Surutu Habibu yaci gaba dayi shidai jinsa yake amma babu tabbacin yana fahimta dan zuciyarsa tana ga son sanin Halin da Humairan take ciki, ta dena kukan ko tana ci gaba dayi?

Sallamar Mama ce ta cece shi daga dan banzan surutun Habibu, har qasa ya durqusa ya gaidata Mama ta amsa tana tambayarsa daga ina haka da yamman nan, qeyarsa ya sosa dan besan me zece mata ya kawo shi ba. Saboda yanayin aiki be fiya samun damar leqa Maman ba sedai kamar in Mansur ya yi saqon da dole shi ze je da kansa in ba haka ba kuwa ko Alkhairi yayi niyyar yi mata kai tsaye Habibu yake kira ya bashi gashi yanzu ko sati biyu ba'ayi da zuwansa ba ya sake komawa dole Maman tayi mamaki ai.

Sallama Humairah tayi ta shiga falon, ya daga kai ya kalleta ta dena kukan amma fuskarta a daure ta wuce can kusa da Maman ta zauna
"Yawwa Habibu ka kyauta. Yanzu saboda Allah daman da nace maka da an fara Rijistar Jamb ka gaya mun ko baka gari zansa akai Humaira tayi shibe kaqi fada? Se yanzu a gidan Hajiya Asabe nake ji wai gobe za'a rufe. Ai kuwa yanzu zaka tashi ka kaita tayi" Mama ta fada se Habibu yayi saurin cewa

"Nifa Mama ban san anfara bane kuma ma wannan yarinyar nagaya miki tayi qanqanta da zuwa Jami'a wannan shekarar gata da shegen sanyi a haka zatayi karatun"

"Firinji ce qarewar sanyi. Na gama ganoka dai baqin ciki kakeyi baka shiga Jami'a da wuri ba tazo ita zata shiga da quruciyarta to koma menenr yanzu ka tashi ka kaita kar dare yayi ai ance ana samun Cafe yanzu" Mamanta sake fada tana hararar sa, Habibu ya kumbura baki yana hararar Humaira dake masa dariya daga nesa Mama ko se sababi take tana gayawa Khalil yanda Habibun baya so Humaira ta tafi Jami'a.

Kamar wanda aka fizgi maganar daga bakinsa yace
"Ta shirya ni se na kaita yanzu tayi".
Da sauri ta daga kai ta kalleshi, Mama ko ta washe baki tana cewa
"Aa daga zuwa ziyara se na hadaka da aiki shidin dai shi ze rakata ko baya so"

"Aa Mama babu komai ai daga nan gida zanje ba wani guri ba se na kaitan tunda kinga baya son zuwa kar su tafi yayi ta yi mata fada a hanya ko ya sakata cike abinda bashi take so ba tunda beyi niyya ba" Khalil ya fada se Mama tace
"Ai kuwa kamar kasan qudurinsa kenan, ina jinsu tace ita harkar zane zane take so wai bazatayi ba kamar shi zeyi mata karatun. Ni na rasa wannan hali na Habibu a inda ya dakko shi wallahi"

"To haka kawai yarinya duk kin wani fi sonta akan kowa" Habibun ya fada cikin qunquni yana miqewa jin Khalil yace ze kaita. Tashi yayi shima yana cewa
"Ta sameni a waje idan ta shirya" yabi bayan Habibun suka fita.
A jikin motarsa ya jingina a zahiri kallon Habibu dake masa hira yake amma a badini ya lula cikin tunanin abinda yayin.
Wai meya shiga kansa ne da yasa yake wasu abubuwa daya kasa gane kansu?

Hangota yayi ta fito daga gidan sanye da Dogon Jilbab kalar dark blue daya qara fito mata da hasken Fatarta haka tsahonta ya fito sosai gabansa ya fadi, saurin bude motar yayi ya shiga yana cewa Habibu
"Shigo muje"
"Aa Yaya

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login