Showing 366001 words to 369000 words out of 429394 words

Chapter 123 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

949

ba Se Maman ta shiga share hawaye tana cewa
"Na sani amma Alhaji kamata yayi mu bar komai a hannu Allah muci gaba da nema mata shiriya dan ni na fara yarda kwakwalwar Umaimah ba'a saiti take ba mutum me cikakken hankali baze ringa abubuwan da takeyi ba"

"Oh kema tayi nasarar yaudarar zuciyarki kenan to bari kiji lafiyarta qalau tana kuma sane da duk abinda takeyi. Saboda tasan ta sabayi tana sha shiyasa bata shayin yin komai amma ki sani ni tsakanina da ita babu duka babu zagi ba kuma zan mata mugun kalami ba sedai yanda take zuba iskancinta haka nima zan hukuntata cikin ruwan sanyi har seta ladabtu. Har yanzu Umaimah bata san da tayi ba daidai ba balle ta nuna nadamarta kina Jin inkarin da takeyi na mun tsaneta a zatonta tsana ce tasa ake mata abubuwan da ake matan amma kwakwalwarta bata bata lissafin me tayi ko me takeyi da ya saka a tsane tan ba? Tsayin shekara guda tana zaune a cikin gidan nan ko gaisuwarta ba ma amsawa bansani ba ko ke amma nidai rana daya yarinyar nan bata tareni ta bani haquri akan qin amsa gaisuwarta ba saboda abin be dameta ba a maimakon haka ma seta dena gaba daya se yanzu data ke neman sassauci ne ta dawo da gaisheni kinga ashe da hankalinta tunda tasan idan tana da buqata ta kwantar da kai to muci gaba da tafiya a haka daga nan har ran da qasa zata rufe idon daya daga cikin mu muddin bata hankalta tasan tayi badai dai ba ta nemi afuwa akan hakan bazan rangwanta mata ba dan ba ita kadaibace yar banza in fact a gurina ta gaji kafiyar tata kinga bata fini iyawa ba" Abbaya fada daga haka ya dauki ruwan shayinsa yaci gaba da kurba. Kasa ce masa komai Maman tayi se hawaye da take sharewa lokaci lokaci, ita ba wai tana nemawa Umaimah sassauci akan wani abu bane amma maganar abinci takeyi be kamata ace za'a horata da Yunwa ba ai ko ayyukan gidan idan bata qoshi ba ba zata iya ba sannan wani ciwon ze iya kamata.

Yana lura da hawayen da takeyi kuma abin ya dameshi amma baya so ta bari rauninta ya rinjaye ta su kasa Nunawa Umaiman kuskurenta. Cikin yanayin rashin jin dadi yace
"To yanzu da kike wannan hawayen na menene me kike so ayi?"
"Nidai ka janye Allah ya isan da kayi mata akan abinci ka bari taci gaba da cin komai kamar sauran yan uwanta" Maman ta fata cikin kuka kamar wata yarinya se abin nata ma ya bashi dariya ya murmusa yace
"To yanzu so kike na dauki asarar abincin data mun kenan a zubar dashi a shara wannan ai Almubazzaranci ne"
"Ni ba haka nake nufi ba yanzun ma ai tana ci jiya shi taci yanzu ma gashi can taci tana amai ai kaga taji maganarka koda ace zata ci gaba da ci harya qare amma kayi mata lamuni idan ta dafa wani abun taci ba iyakar wancan ba" Maman ta sake fada se ya nisa yace
"Shikenan taci darajarki amma seta biyani kudin shinkafata dan ba zan dauki Asaraba in yaso tayi duk yanda zatayi da ita kirawo mun ita" seta miqe ta fita, Umaimah na nan zaune a qasa tana numfarfashi tunani takeyi yanzu da tana gidanta abinci dai se wanda ranta ya raya zataci ko basu da abu duk inda yake Khalil ze tafi ya nemo mata danye ko dafaffe muddin tace tana so amma yanzu a cikin gidan ubanta yunwa na neman ta halakata.

Dakya ta iya tashi tabi bayan Maman, tayi tsuru tana sauraron Abban da yake cewa
"Mamarki ta nema miki afuwa akan abinci naji kuma nayi amma akan sharadi se kin biyani kudin abinda kika lalata sannan karki kuskura ki zubar ki san dai yanda zakiyi dashi"
"Na yarda wlh Abba zan biyaka" ta fada cikin rawar murya se yayi murmushi kawai yaci gaba da cewa
"Sannan abubuwan da kikeyi na ganin dama inaso kisan cewar dolenki ne kiyi bawai kamar yanda kike dauka ba karki kuskura na sake maimaita miki maganar nan a cikin gidan nan" ya zaro dubu biyu ya miqa mata yace
"Ki bayar a siyo miki Cefane Miyar Taushe zakiyi da dare idan na fita zan aiko da Qashi a qara da Nama" seta tsaya ta kasa karba ya watsa mata kudin baki na rawa tace

"Abba ai yau girkin Anty ne bana Mama ba"
"Dana tashi baki Umarni kinji nace girkin uwarki kadai zaki ringayi? In kinga dama kiyi idan kuma kinga akasin haka karkiyi ita Saratun ma bata nan Uwarki da sauran yan uwanki su zauna da yunwar dan ban yarda wani ya girka abinci cikin gidan nan ba idanba ita ba kuma ki hado lissafin kudina ki kawo mun yanzu ina jiranki" Abban ya fada a fusace kan ta na qasa tana Hawaye ta tabbata dai ta zama boyi boyi kawai a gidan bata da hutu daga girki se shara da wanke wanke. Cikin kuka ta kalleshi tace
"Toh dan girman Allah Abba bada itace ba wlh har cikin kwakwalwata nake jin hayaqinga idona duk ciwo sukeyi ka barni na ringa Amfani da Gas din"
"Ban yarda ba sedai idanda kudinki zaki ringa zuba Gas din" ya bata amsa kai tsaye har tana zabura kuwa tace
"Na yarda sannan Abba Shara ma zan samo Almajirai zan ringa biyansu sunayi "
"Ai shikenan kiyi duk yanda yayi miki" ya sake fada yana wani murmushi tareda girgiza kai, su zubasu gani ai duniya tafi bagaruwa iya jima daga haka ya sallameta ta fita tana jinta sakayau ko babu komai an rabata da wahala tunda ya yarda ta samu mataya.

Indomie ta debo a store ta samo Almajiri ya siyo mata sardine ta dafa abarta taci tayi nak har wani sabon qarfi takeji saboda sassaucin data samu a wautarta. Ta dumama Dafadukanta tsaf ta bawa Almajirin tace ya fita da ita ya rabar sannan ta ce masa ya ringa zuwa kullum safe da yamma ze ringayin shara da wanke wanke suka tsadance yanda zata ringa biyansa ya zama girki kadai ne aikinta. Cike da kuzari ranar ta ringa aikinta tayi musu Dafaduka da rana amma ba irin waccen ba tana saukewa ta mayar da Ruwan Tuwo haka ta tuqa musu shi sama sama duk dan kar hannunta yayi kanta danma shinkafar me laushi ce kuma tasha ruwa zata kwashe a kula Mama tace mata karta kuskura, dole ta dakko Leda ta malmala shi yanda akeyi ita dai Maman kallonta kawai takeyi dan gaba daya rayuwar Umaiman tausayi take bata. A maimakon ta roqi Mahaifinta ta bashi haquri yayi mata afuwa saboda shedan na mata kururuwa tana ganin ta tara Abin duniya ai shikenan yau da gobe dai tafi qarfin wasa ko nawa take ganin tana dasu wata rana zasu qare.

Haka rayuwa taci gaba da gangarawa Umaimah, Yasir tasa ya kira mata Me POS din qofar gidansu tunda an hanata Fita ta bashi ATM dinta ya duba mata balance tunda babu waya, dubu dari uku da Hamsin da biyar take dasu a cikin account dinta na UBA, dayan first bank dinta bata da ATM tunda yayi expire bata sake wani ba ta san ma kuma ba wasu kudine a ciki ba sunyi yawa sukai dubu Hamsin dan a nan take Saving kudi kuma su ta tattara ta biyewa Safina suka ringa rabawa Malaman qarya gashi yanzu bata ga tsuntsu bata ga tarko. Tas tace ya cire kudin ya bata ta ajiye su, ta debo akwatunanta na dakin Mama a cikin kayan ma ta samu kudade irin wadanda take ajiye wa cikin drawer kaf suka hado mata komai nata Mayukan shafawarta da yawa se zubar dasu tayi dan sun lalace ta debi abubuwan da zatayi amfani dasu yauda kullum ragowar ta hadesu ta rufe tunda ba fita takeyi ba.

Kwanci tashi Asarar me rai se gashi tun ba'aje ko ina ba Al'amura sun fara yi mata tsanani, kudin da take gani a hannunta suka sa ta sake miqe qafa tana yanda taso suka tasamma qarewa dan a cikinsu take hidimar komai da wadda ta zamar mata dole da wanda ta dorawa kanta ta siyan Gas da biyan Almajirin da yake mata wanke wanke da shara ga ciye ciyen banza da wofi baki ya saba da dadi kullum tana hanyar aiken Yasir siyan shawarma da Icream ko Kaza gashin Inji wadda ta sabaci a gidan Khalil a zahiri idan ka ganta zaka dauka bata da wata damuwa amma a badini ba haka bane, a sannu rashin Khalil yake dukanta kullum cikin zuba idon ganinsa takeyi yazo da niyyar maidata se gashi babu wata alama da take nuna faruwar hakan dan daga shi har yayanta babu wanda ya sake tako qafarsa gidan har gara takan ji a bakin Nuratu ko Maman Asad an kai musu yaran Musamman Nuratu da take nacin su abin ya qara bata mata rai wato ana kaisu gidan yan uwanta se ita da take uwarsu ce ba za'a kai mata su ba duk tsiya dai ba'a isa a canzawa Tuwo suna ba suna nan a matsayin yayanta kuma ko bajima ko ba dade zasu nemeta idan ba'a kawo su ba.

Ba'a cika wata shida data kama ayyukan gida ba kudi suka qare Almajiri ya gudu saboda daman ba abinci ake bashi ba kudi take biyansa yaci wata biyu bata biyashi ba sedai ta hadashi kanzon tukunya tace yayi haquri in ta samu zata biyashi daya gaji ya fece shikenanta sake shiga ukun data fi tada dan yanzu ga aiki ya mata karo ga qangin talauci dan kudin da zata siyi sabulun wanka ma Wahala yake mata a da kuwa duk wata Khalil yana sako mata Shower gel din da take amfani dasu tunda Iman ta bar hannunta kuwa ya janye tallafi a farko bata damu ba dan gani take kamar tana da abinda ze ci gaba da riqeta se yanzu ta gane karin maganar da Hausawa suke cewa Zara bata barin dami tunda gashi sake dawowa square zero.

Rayuwa tayi mata gwatson kenwa, idan kaga yanda Umaimah ta koma a shekara daya da fara Zawarcin gaske se ka tausaya mata kuma ka sake gasgata Al'amarin Ubangiji dakan sauya abu a sanda yaso. Ta yi wata irin rama da baqi babu rashin Abinci amma ta fita a hayyacinta kana kallonta kasan bata da nutsuwar zahiri data zuciya a koda yaushe idan ba aiki takeyi ba zaka sameta ta zauna tayi shiru tana tunani, a yanzu kam ta gama yarda da cewar Khalil ya barta tunda har ze iya daukar tsayin shekaru biyu cif ba tareda ya waiwayeta ba tabbas ya zareta daga rayuwarsa. A kullum dare kwana takeyi cikin kuka da juyayi, nadama mara amfani ta dirar mata akan abinda ta aikata har yayi sanadiyyar barinta da Khalil. Me yasa batayi haquri ba? Me yasa bata karbi qaddara a yanda tazo mataba ta gaza fuskantar duk wanda ze tausheta a baya ya nuna mata tayi haquri me yasa basu fito sun bayyana mata makamanciyar wannan rayuwar da take fuskanta a matsayin abinda zata tarar sakamakon butulcewa? Ta biyewa kururuwar shaidan da zigar qawayen banzan da tsayin lokacin nan babu wadda ta waiwayeta balle harta san halin da take ciki koda yake duk tarin qawayen nata da daman ita take bauta musu ita suke mora babu wadda ta bi sahun sanin inda take tsayin shekara guda da rasa wayarta. Tayi mamaki kwarai da ace Rufaida bata nemeta ba, daman batayi tsammanin Safina ba kodan kalar rabuwar da sukayi a Asibiti amma Rufaida fa a baya baya dabda Al'amura zasu rikice mata ta dawo sun qara dinkewa amma ace tajita shiru bata zo inda take ba tunda dai tasan gidansu ai ya kamata ta tun tuba taji tana da rai ko ta mutu.

Babbar damuwarta irin yanda Iyayenta da yan uwanta gaba daya suka banzatar da ita, irin yanda suke mu'amalantarta na mata ciwo amma ba laifinsu bane a yanzu ta fahimci tarin wautarta a baya da abubuwan da tayi ta kuma ji irin zafin da sukaji a lokacin data banzatar dasu itama ta daukaki wasun su suka zame mata komai yau gashi a sanda ta shiga halin da take buqatar dan uwan da zata jingina dashi tayi kuka ta rasa badan bata dasu ba sedan kunya da nauyin abinda ta aikata musu a baya baze barta ta iya tun karar su ba. Tana kallo su Nuratu zasu zo gidan su qule da Mama a daki suna hira cikin nishadi da jin dadi ita tana rabe a tsakar gida ko tana aiki tsakaninta da Maman umarnine na yin abu idan ta sakata aiki dan a tsahon lokacin nan bata taba ce mata Umaimah karkiyi ba, ta rasa damar shiga dakin Mamanta tayi hira da Ita Antyn ma da take ta tata tun wancan lokacin ta watsar da ita ta dawo tsakaninsu ga Yayanta da suka mayar da ita tamkar Tabarma Yanda Sharifa da Firdausi suke tata mata rashin mutunchi a gidan kuma bata isa tayi magana ba dan akwai ranar data Mari Firdausin Abba da kansa yayi mata kaca kaca har yana fadin idan tana da kunya har taji Haushin wani dan ya mata rashin kunya kota manta sanda taringa kallon Idon Sa'ar Uwarta kuma Matar data tsugunna ta haifa mata Miji ta ambato iyayenta ta zaga har akwai rashin kunyar da za'ayi mata taji haushi? A ranar tayi kuka tamkar hawayenta ze qare ta shiga rudu da Dana sani kuma se a ranar hankalinta ya dawo jikinta ta shiga tariyo zamanta da Khalil da irin mugayen ta'adundata ringa aikatawa.

Ta ringa hakaito tarin qaunar da Khalil da yan uwansa suka nuna mata domin babu wanda zata cire a ciki duk sun sota, mugayen halayanta suka sanya su yi mata tawaye kuma duk da haka Khalil da Hajiyar sa basu barta ba, tana iya tunawa har a daren da Khalil ze saketa dukda hauka da Tijarar da takeyi Hajiya bata fasa yi mata uzuri ba ta shafawa idonta toka ta manta Alkhairan matar a gareta tayi mata zagin da idan da ita ta kirki ce ko wani taji ya kwatanta yiwa Hajiyar se inda qarfinta ya qare amma a gaban Danta da iyayen da suka haifeta bata dubi Alfarmarsu tayi musu kara kodan Haifarta da sukayi suka bata tarbiyya ba ta watsar tayi abinda taga dama toh waima banda son zuciya irin tata ta ina Khalil ze sake waiwayarta bayan duk abinda tayi masa hatta ubansa dake kwance cikin kabari besan an aureta na seda ta ambato ta zaga to ya dawo gareta kuma a wanne matsayi idan dai da kunya ai itama ba zata yarda ta sake hada ido da wani daga cikin Ahalin Khalil ba dan bata da kwarin guiwar da zata kalle su ba kuma tasan da irin Kalaman da zatayi amfani gurin wanke kanta ba.

A hankali ta yada duk wasu makaman da take taqama dasu ta fuskanci rayuwa da abinda take tafe dashi ta kuma yarda da cewar lokacin girbar abinda ta shuka a baya ne ya zo mata. Duk wanda ya santa a shekara uku baya idan ya ganta a yanzu baze ganeta ba saboda yanda ta koma. Bayaga aikin bauta da takeyi domin a yanzu Umaimah da bawan da aka siya banbancinsu kadan ne, a rana bata samun hutu na cikakkun awanni hudu, tun Asuba idan ta farka ta fara gyaran gida da dora abincin safe data gama aka karya zata yi wanke wanke ta maida na rana duk a qoqarinta na kiyaye duk wani abu da ze qara mata laifi a gurin Abba da Mama da yanzu take neman hanyar wanke kanta a guri su sannan duk inda Qarfe shida take ta sauke abincin dare. Da itacen data qi jini take aikin tunda bata da Asi yanzu kuma komai ruwa ko iska haka zatayi aikinta ita da Gas dinsu sedai Kallo dan sau da yawa idan aka samo danyan itace Mama takance ta dora a Gas dinse tace Aa, muddin ba Abba ne ya bata umarnin taba masa abu ba ba zatayi ba.

Sosai take shan wahalar rayuwa ta jeme ta fige idan ka kalle ta se ido kawai babu wannan gayun bare ta samu damar zuga iskancin data saba to dame zatayi gayun ma suturu dai gasu nan tana dasu bila Adadin amma babu damar sakawa dan kayayyakinta gaba daya yanzu sun mata yawa saboda rama. Man shafawarta Vaseline ne Habiba se Sabulun Give da Abban yake bata dubu daya duk wata wai ta siyi sabulun wanka, wanki da man shafawa kamar wata yar tsana babu zancen tutare daman Alumun take gogawa a hammatarta kayanta kuwa qaurinitace ya isheta ba seta qara dawani turare ba koda yake a hakan ma ya mata bata tsammaci zata samu ba tunda Mama da take zaton zata fishi laushi abinda bata so bata bata a haka take jalauta rayuwarta duk buqatu a cikin dubun nan zatayi wanda ya zama dole, hatta da Pad data ga cewar tana cinye mata fiye da rabin dubun a hakanma kuma leda dayar na wadatarta takeyi ba seta yankewa kanta amfani da ita, ta samu wani zani a kayanta ta yayyankashi tayi qunzugu wadatattu. A ranar data fara amfani dashi tayi kuka tamkar ranta ze fita da tana wankewa, ta tuna a gidanta drawer guda take da ita ta pad hatta baqo idan tayi buqatarta ta kamashi Pack haka take kyatarta kuma yar waje me kyau ma ba made in Nigeria ba take amfani dasu amma wai yau itace take amfani da qunzugun Atanfa a gidansu tabbas a tsoraci rayuwa.

Cikin wannan qangi da matsatsi taci shekara uku babu kuma wani sauyi ko sassauci kullum tana cikin gida tana aiki zata iya cewa ma ta manta da kalar qofar gidansu ita abu daya da zata iya cewar na jin dadi daya sameta shine fara kawo Yaranta gidansu da akayi tun shekara daya data wuce dukda zuwan nasu wuni ne basu taba kwana ba sannan su kansu yanda suke Mu'amalantarta abin na matuqar duk zuciyarta ranar da suka fara zuwa batayi tsammanin tayi kewarsu har haka ba se a lokacin tana tsakar gida tana shara suka shigo su ukun cikin kyakykyawar shiga Bibi da Iman sunyi Anko da

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login