Showing 279001 words to 282000 words out of 429394 words

Chapter 94 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

993

sake shiga dakin dazu ya gama buruntunsa ya fito da wani kwando a hannunsa. Gurin da yake zaune ya koma ya shiga ciwo fararen robobi qanana yana ware kowanne da yan uwansa seda ya gama tsaf kafin ya bude jakar dazu ya ciro wata takadda. Sticker ce a jiki ko waccean rubuta yanda ake amfani da maganin ya ringa daukar roba daddaya yana mannawa yana tarasu a gefe seda ya gama ya sake tashi ya mayarda ragowar kayan ya dawo da Allo da tawada ya zauna ya fara rubutu, befi layi biyu ba yayi ya dago yana kallonta yace
"Ya sunanki?"
"Umaimah" ta bashi amsa kamar me ciwon baki ya rubuta ya sake tambayarta sunan Mijinta ta gaya masa, seda ya gama tsaf kafin ya kwalawa Amaryarsa kira ta fito jikinta na rawa tayi musu sannu ta durqusa a gabansa, ruwa yace ta kawo a kwano bayan ta kawo ya miqawa Umaimah Allon yace ta wanke, kamar wadda yake controlling haka ta karba ta wanke ya karbi kwanon a ciki wata yar jarka ya dure rubutun ya hada cikin sauran kayan daya ware kafin ya zauna yana kallonta ya shiga daga robobin yana cewa

"Wannan ko wanne da yanda zakiyi amfani dashi a jiki ki kula, kada a samu kuskure, sannan na wannan" ya ciro wani qulli daga Aljihunsa ya miqa mata yace
"Turarene a tsakar gida ake yinsa duk kuma wanda ya shaqi hayaqin bakinsa zai rufe ruf daga fadar abinda bakyaso. Ki turarashi a inda duk wani me fada aji akan al'amarin auran yake shikenan kin gama dasu, sannan wannan" ya sake zaro wani qulli a farar leda sabanin na farko da yake a baqa ya miqa mata yana cewa
"Ki samu kan Tinkiya, Tinkiya Mace ba Rago ba kiyi farfesun sa ki zuba wannan garin maganin a ciki, duk wanda yaci zaman lafiya tsakanin keda shi har abada babu wani sabani da ze saka shiga tsakani, duk wasu dangin Miji da suka saka gaba ki dafa ki basu suci an gama magana".

Ita dai Umaimah juya abubuwan takeyi a hannunta kawai amma tunaninta yayi nisa da inda suke, 'akwai aure,akwai mutuwa ga kuma mutuwar aure duk akan wa?' Abinda take ta tunani kenan, tana ji Safina na zabga masa godiya ta bude jakarta ta ciro kudaden da sun haura dubu dari ta ajiye masa ya miqe yana ce musu suci abinci kafin su wuce sannan ya juya ya fice daga falon bayan ya sake kallon Umaiman. Ita dai bata iya shan koda ruwa ba Safina ce ta tsakuri Abincin saboda Azalzalar Umaiman suka tafi. A hanya suna tafiya Safina na sake jaddada mata da tayi amfani da Abubuwan nan kamar yanda yace

"Ki kwantar hankalinki qawata kinsan fa binciken nan nasu sau da yawa basa ganin daidai se kiji zancen wani ya shiga na wani ta yuwu can wata yayiwa Istaharar tun dazu se a akanki Labarin ya fito" Safina ta fada ganin Umaimah ta zurawa hanya ido bata magana tunda suka fito. Ita kanta ta tsorata da jin zancen mutuwa daya kawo, a iya sani ta da Malam Sha yanzu kuwa be taba fadar abu be tabbata ba (wa'iyazubillah) toh babban abin fargabar shine waye ze mutu? Sanin wannan kuma se Allah. Haka suka qarasa gidan Safinan, Umaimah ta dauki motarta dan data Safina suka fita, bata zauna ba ta wuce gida faran faran babu sallar Azahar balle La'asar duk a yawon gidan Malam ta riske su.

Sanda ta isa gida Khalil be dawo ba. Dakinta ta wuce ta adana kayan data shigo dasu kafin ta shiga bandaki tayi wanla hade da alwala har zuwa sannan kuzarin jikinta be dawo ba. Sedata rama sallolin sannan ta kulle qofar dakin da muqulli ta dauko jakarta ta zazzage kayan a kan gado. Daya bayan daya ta shiga duba su, wani a abinci wani abin sha harda na dafa shayi se nata na amfani wasu a ruwan wanka gana tsarki da hayaqi duk dai gasu nan kala kala. Zuciyarta ta kasu biyu akan amfani da kayan ko akasin haka kuma kowanne bangare ya kasa rinjayar dan uwansa dan haka ta hade kayan ta maidasu jakar gaba daya. Kallon robar rubutun daya ce ta zuba masa a ruwan sha tayi, seta dauka ta riqeta a hannunta, dakyar ta haye saman saboda nauyin da jikinta yayi kai tsaye ta wuce inda Dispenser take ta kalli ruwan da yake ciki ya wuce rabi dan haka beyi mata wahalar dagawa ba ta cire shi, rubutun ta juye a ciki, tana so ta dandana taji ko ya canza taste amma bata san na menene ba, haka ta mayar da robar kai kafin ta wuce dakin Khalil din ta shiga gyarawa.
"Shi Aikin Asiri da kike gani se kin hada da kissa yake ci da wuri" abinda Safina ta gaya mata dazu da suna hanya kenan ta kuma jaddada mata data taushi zuciyarta ta nuna komai ba komai ba kawai ta zura ido taga ikon Allah.

Tsaf ta gyara masa dakin daman falon a gyare yake ta kwalawa Ruqayya kira akan ta kawo mata garwashi. Seda ta turare dakin da hayaqin da Malam din ya bata kafin ta shiga bandaki ta kashe wutar tayi flushing gawayin da ragowar maganin kamar yanda ya fada kuwa hayaqin bashida wari ko qamshin komai, yanda kasan bata saka komai ba se dan qaurin wuta dan haka ta zuba turare a bunner ta kunna bayan ta fesa Room freshener sanna ta koma qasa. Kunun da bata sha da safe ba ta sha yanzun dukda kwata kwata bataji yunwa badamur da take ciki ta cushe mata ciki, Ruqayya na kitchen tana hada abincin dare, Tuwo takeyi da Miyar Kuka kamar yanda yake a Time Table din abinda zasu dafa. Daki ta koma ta kwanta lamo, tsoro takeji haka nan zuciyarta taqi aminta data cutar da Khalil dinta amma ya zatayi? Bata da wata mafita idan ba wannan ba da bakinsa ya tabbaatar mata da aure zeyi ya hadata da wata a cikin zuciyarsa ya kuma raba musu kansa a shimfida abinda ba zata taba lamunta ba ko bayan ranta bata fatan Khalil ya sake auran wata mace, so takeyi ya dawwa babu aure har ya tarar da ita su sake ci gaba da zama tare a Aljanna.

Wannan tunanin ya saka ta miqe, Robar abinda yace ta zuba masa a Miya ta dauka dana shayi. Suna da banbancin kala dan haka ta cire takaddar jiki ta miqe ta tafi Kitchen din. A bakin qofa suka hadu da Ruqayya da ta dakko Fulasandata zuba abincin Khalil zata kai kan Dining, Ciki Umaiman ta wuce, kaitsaye ta bude butar shayin da Ruqayyanta dora ba tareda tunanin komai ba ta zuba abinda zata zuba ta mayar ta rufe haka ta zuba na miyar shima bayan Ruwayyan ta ajiye, har zata shiga daki ta tsaya ta kwalawa Ruqayyan kira ta fito daga Kitchen din da sauri
"Gobe idan Allah ya kaimu zan aikeki Abbatuwa da Safe, karki manta da kin tashi koda ni na manta ki tunamin" ta fada mata Ruqayya ta amsa da
"Toh Hajiya" kafin ta juya ta koma Kitchen din a ranta tana tunanin me yake faruwa kuma dan tunda Umaiman ta shigo taga yanayinta ba yanda take ba.

Kwanciya tayi a dakin sanyin jikinta ya ninka na dazu, sosai take zargin kanta da rashin kyautawa amma kacokan ta dora laifin akan Khalil, shiya ja duk abinda ya sameshi shine Sila.

KHALIL
Cikin matuqar bacin rai ya kama hanyar Qunchi dan har ya manta da Anwar zasu tafi seda yaci rabin hanya sannan ya kirashi yana tambayar be fito bane har yanzu yana ta zaman jiransa. Haquri ya bawa Anwar din kan cewar yayi gaba ya taho kawai, yana ganin Kiran Humaira amma ya qi dagawa, baya so ya sauke fushin da ba nata ba akanta shiyasa kawai ya tura mata saqo cewar yana tuqi idan ya tsaya ze kirata.

Gaba daya ransa babu dadi yayi aikin daya kaishi, se yamma Lis suka gama suka kamo hanyar Kano. Anwar ne yake tuqi shi kuma yana zaune a kujerar gefe ya jinginarda kansa baya yayi shiru yana tunani. Tunani barkatai suke yawo a kansa wai har se zuwa yaushe Umaimah zatayi hankali? Ya tambayi kansa. A kullum girma suke warawa shekaru na dada yawa amma ita tamkar baya takeyi kaifin tunani da hangen nesanta yana dada raguwa Kishi ai ba hauka bane da har ze saka tayi wasa da rayuwarsu, yanzu abinda tayi dazun da ace yazo da tsautsayi ko basu mutu ba ai zasu wahala musamman ita da tak da qarin wani nauyin a jikinta amma sam ita kamar mara tunani abinda yazo mata a zuciya kadai takeyi bata hangen abinda hakan ze iya haifarwa.

"Mutumina ka rage tunanin nan haka, kowa yana da damuwa idan mukace zamu saka a rai muyi ta tunawa qila kama tafe a hanya sedai kaga mutane kawai suna ta faduwa damuwarsu ta kashe su" Anwar daya gaji dayi masa magana ta yaba shi yana fada. Ajiyar numfashi yayi kafin ya tashi zaune da kyau yana cewa
"Damuwar ma kala kala ce Anwar, kai dai ka godewa Allah kawai da be jarabceka ta fannin aure ba, kaga duk wani jin dadin rayuwa to Macece cikonsa idan kuma har ka rasa nutsuwa a gurinta wlh ko kafi qaruna wadata da iko seka tawaya ta bangaren nutsuwar zuciya Allah dai kawai yasa mu dace".

Wayarsa ya zaro a Aljihunsa ya kunna dan yana isa ya kasheta saboda baya son Humaira tayi ta kira shi kuma baze iya magana da ita a cikin fushi ba. Tana gama kunnuwa kuwa saqonta ya shigo, qorafi takeyi akan yace ze kirata idan ya isa kuma ta sake kira wayar a kashe
"Ka kirani da ka kunna wayar idan ba haka ba babu ruwana da kai, I love you Yayana" ta rufe saqon dashi. Be san sanda ya saki murmushi ba babu bata lokaci kuwa ya danna mata kiran kamar tana jira ringing daya ta daga wayar da sallama kafin ta dasa masa kukan shagwaba. Seda ya kwashi wasu mintina yana aikin rarrashi tareda kare kansa akan dalilin daya saka be kiratan ba kafin ya samu ta haqura bayan ta kafa masa sharadin daya shiga Kano seya je gurinta shine hukuncin hanata magana da shi da yayi wuni guda.
"An gama my Boss lady, amma idan nazo me zaki bani kinga dai na gaji da yawa ki taimaka ko dan hug ne da kiss na samu mana" ya fada cikin sigar tsokana kafin ya kai qarshe kuwa har ta kashe wayar ya zareta daga kunnensa yana sakin dariyar dabe shirya mata ba. Kunyar ta tana burgeshi duk sanda yake son ya tsokaneta da yayi mata irin wannan maganar zata dauki fushi ita ala dole ya kauce hanya. Be gama dariyar ba kuwa saqonta ya shigo tana cewa
"Na fasa karkazo, kuma kayi iatigfari tunda aini ba matarja bace kake gaya mun wannan maganar".

Sake tuntsurewa yayi da dariya har yana dukan?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? gaban motar, Anwar ya kalleshi da murmushi yace
"Gida biyu maganin gobara mutumina"
"Fadi ka qara Abokina musamman ace ka samu danyan jini duk wata damuwarka ta yaye wlh" ya bawa Anwar din amsa yana sake kiranta amma taqi dagawa. Haqura yayi dan daman baya so yaje din ne shi yasa yayi mata haka se ya kunna Datarsa ya shiga WhatsApp, hotuna ya gani Jalilah ta tura masa ya bude yana ganin abinda yake ciki ya zaro ido tareda dafe bakinsa saboda mamakin abinda ya gani. Motarsa akayiwa haka? Bashida buqatar tambayar wa yayi dan yasan yar dabar daya ajiye a matsayin mata shi kansa zata iya masa haka ba motarsa ba se ya kashe Datar kawai ya fita daga WhatsApp din yana qoqarin hana bacin ran sake dawo masa.

Daya isa gidan ma kallo daya yayiwa motar ya hadiye wani abu me daci ya wuce, da Hajiya tayi masa maganar ma kai tsaye ce mata yayi
"Kiyi mun Addu'a Allah ya maidamun da mafiyinta" yayi shiru.
"Amma Babana haka zaka zuba mata ido ta ringa barnatar maka da dukiya babu gaira babu dalili?" Hajiyar ta sake fada seya miqe yana murmushi yace
"Wancan karon fa Hajiya ke kikayi mun fada akan me zanyi fushi saboda na rasa wani qyale qyalen duniya, wannan ma ba rabo bace shi yasa hakan ya faru da ita. Gobe kawai zan kora company suzo su dauka su bani abinda ya samu dan banida kudin da zan iya gyarata gara kawai na siyar yanzu dai ni ya maganar da mukayi jiya kin kira Baba Abu din?" Ya canza maganar da wata. Seta sauke numfashi tana kallonsa. A idonsa ta karanci bacin ransa amma ya danne ya nuna komai ba komai ba. Numfasawa tayi tace
"Na kirashi yace babu damuwa ze samu sauran kawun nanka suyi magana se suji sanda ya kamata suje din kuma gurin wa zasuje"

"Kuyi magana da Maman kawai Hajiya ita zata gaya miki duk ma inda zasuje, sannan dan Allah ina roqon Alfarma idan sunje karsu bari a saka lokaci me tsaho Hajiya, duk abinda za'ayi karya wuce wata biyu" ya fada kansa a qasa kafin ya miqe hahiyar tace
"In sha Allahu, Allah dai ya tabbatar mana da Alkhairi sannan kayi haquri da abinda ya faru Babana taci Albarkacin zuri'a".
Murmushi yayi mata ya fice daga part din ya wuce nasu.

Yana shiga dakinsa yaji kansa ya sara, ya dafe kan yana kiran sunan Allah ya zauna a gefen gado yana jin bugun zuciyarsa yana qaruwa, a hankali ya tashi ya fita palour, ruwa ya tsiyaya yasha dan ya fi ta'allaqa bugawar kan da gajiyar da yayi ga bacin ran da yake ciki Allah yasa ma ba jininsa ne ya hau ba. Seda yayi wanka yayi sallar Magriba kafin ya zauna cin Abinci. Kallon tuwon yana jin yunwa amma gaba daya abinci ya fita a ransa bacin rai ya cika masa ciki taf kuma bayaso ya fitar dashi anyi masa ne da gayya dan yayi magana shi kuma ya qudurce baze ce mata komai ba ze tarata yana kuma dab da ramawa. A hankali yayi bismillah ya fara cin tuwon, kadan yaci ya ture ya tsiyaya shayi a cup ya koma cikin falon ya zauna. Yana fara sha aka kira sallar Isha seya ajiye ya fita, Umaimah dake tsaye bakin qofarta tun zaman Khalil din tana ganin fitarsa ta fito daga dakin. Cup din shayin ta dauke ta wuce kan Dining ta maidashi cikin butar shayin kafin ta dauka ta kai kitchen. A sink ta korashi, ragowar wanda bata saka komai ciki ba ta dumama ta maida masa dan tasan be gama sha ba ta sake dakko flask din miyar shima ta zubarda ta ciki ta maida wata ranta duk a dagule.

A falon tayi sallah ta zauna a gurin harya shigo, kallo daya yayi mata ya wuce gurin Dining din ya tsaya yana kallon kayan dake gurin. Yana da tsananin lura da abu, ko takadda ya ajiye aka canza mata mazauni yana ganewa dan haka nan take ya fahimci da an canzawa kayan yanayi. Butar shayin ya bude dan ya tabbatar da zarginsa ilai kuwa yaga yawan wanda yake ciki ya zarta wanda ya bari kamar ma be taba ba. Kallon Umaimah dake h
Jan carbi yayi ya girgiza kai a ransa yace
"Idan ma kasheni kike so kiyi nayi shahada ke kuma kiji da dakon haqqina" ya maida murfin ya rufa ya haye sama yana jin wani iri a jikinsa. Gaba daya ji yayi ya kasa nutsuwa se kawai ya dauki muqullin motarsa ya fita. Ya fahimci Umaimah tayi nisa ba yanda ya santa bace a baya, wannan Umaiman ta yanzu zata iya aikata komai akan cikar muradinta.

Asibiti ya wuce, be samu nutsuwa ba seda akayi masa gwaji aka tabbatar masa da babu wani abu me kama da guba a jikinsa kafin ya sauke a jiyar zuciya a ransa yana zargin kansa da yi mata rashin Adalci. Me yasa ze zargeta akan abinda bashi da tabbaci? Ta yuwu an maida wanda ya zuba ya fara sha ne ciki shi yasa yaga shayin ya qara yawa sannan an kwashe plate din daya bata dole zata gyara zaman kwanukan. Yasan ma Ruqayya ce tayi amma zuciyarsa ta tafi ga zargin Umaimah tayi masa wani mugun abu. Hakannan yakeji be kyauta mata ba, can qasan ransa wata soyayyarta ta qara motso masa yana tafe a hanya yana tunani Ya sani Umaimah tana sonsa kuma tabbas se ana son mutum ake kishinsa kenan soyayyarsa ce ya janyo take aikata duk wadan nan abubuwan idan har ya karbeta a yanda take zasu zauna lafiya ya yarda ya kuma karbi laifin akan cewar shi yake tsokanota a koda yaushe har take sauka daga layi tayi abinda kowa yake ganin bata kyautawar.

Wasu tunani barkatai suka shiga gewaya masa kwakwalwa, yanda kasan wanda Iska suka shiga haka ya kama hanyar gida jikinsa na rawa dan so kawai yakeyi yaje ya bata haquri ya kuma gaya mata duk abinda ya fada mata dazun wasa yakeyi tayi haquri su zauna lafiya. Daya isa gidan ta koma daki ya murda qofar yajiya a kulle, a hankali ya shiga bugawa, kusan minti biyu yana bugu bata bude ba jikin qofar ya tsaya ya shiga kiran sunanta nan ma shiru haka ya haqura ya wuce sama ransa duk babu dadi. Raba dare yayi yana tunanin halin da take ciki, daga qarshe dayaga ya kasa bacci ya miqe yayiwo Alwala, yana tayar da sallar dakyar ya kai raka'a biyu yana sallamewa bacci me nauyi ya kwashe shi a gurin.

*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* =?L?
Page 64

Hasken ranar daya galle masa ido ne ya farkar dashi ba tareda ya shirya ba. Dakyar ya iya bude idanunsa da sukayi nauyi yanda kasan wanda ya kwana be runtsa ba, yabi dakin da kallo, hasken daya gani ya tabbatar masa da cewar safiya ta rigada tayi cikin hanzari ya miqe yana istigfari wayarsa dake kan mudubi ya janyo ya duba lokaci qarfe bakwai harda minti Arba'in seya ajiyeta ya shige bandaki da sauri a ransa yana mamakin meya shiga kansa haka?

Da wayonsa baze tuna ranar daya rasa sallar Asuba ba, koda

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login