Showing 405001 words to 408000 words out of 429394 words

Chapter 136 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

1037

zaki bamu taki gudummar gurin tabbatar da kambun mu".

Kai da gyada masa kawai dan ta kasa magana. Ya bude Drawersa ya ciro Littafin UmdatulAhkam tuni daman sauran yan Ajin kowa ta fito da nata suka shiga bitar inda suka tsaya kafin ya dora musu sabon Karatu. Yana gamawa wani Malamin ya sake shiga a haka har qarfe daya basu samu hutun ko minti biyar ba dan da wani ya fita wani ze shiga duk kuma wanda ya shigo seya tambayeta sunanta Malamin qarshe dayake da surutu yace ta dage Niqab din tasha iska dan kusan duk yan Ajin suna saka Niqab din amma kowacce ta daga nata se zasufita suke saukeshi, shima dai kai ta girgiza masa Alamar Aa. Da yake bema tambayeta sunanta ba yace
"Tohz, kurma ce kenan", maganar ta bata haushi amma ta dake da lokacin baya ne seta maida masa da martani in ma bata ce uwarsa ce kurmar ba amma yanzu kura tayi lafiya.

Da aka tashi tareda monita suka fito tana ta janta da hira har suka fita saga makarantar tareda wasu yan Ajin. Masu Motoci suka ragewa wanda suka saba tafiya tare hanya masu hawa na haya suka tafi su kuma na kusa suka daba a qasa. Kusan su bakwai suka jera acikin yan Ajin nasu, Malama Aisha take ce mata
"Kema gidanki nan kusa ne Ashe"
"Eh" ta bata amsa, layi daya tsakanin gidansu suka rabu Malama Aishan ta shiga gidanta dake bakin hanya, Umaimah tasan Matar gidan dan tana Amarya sun dan yi hulda suna haduwa a gidan Maman Nana kafin tayi aure ta bar unguwar kenan kishiya aka mata. A cikin layinsu suka rabu da sauran mutum biyu da suka taho tare ta shiga gida tana Mamakin ganin daya ta shiga gidansu Maman Nana dayar kuma ta miqe.

Sallar Azahar kawai tayi ta karbi aikin Abincin da Anty ta fara tana cewa ta barshi ita data kwaso gajiyar makaranta amma ta dage setayi. Seda ta sauke na dare tayi wanka taci abinci kafinta zauna bitar karatun da akayi musun. Ranar da wuri ta kwanta tunda tasan yanzu hidima ta qarun mata akwai zuwa makaranta a haka lokaci yaci gaba da tafiya harta share sati biyu a makarantar kuma Alhamdulillahi tanajin dadin karatun sosai har sannan kuma babu wanda ya taba ganin fuskarta a ajin, tsakaninta da kowa sallama ce bata magana dan ko Malama Aisha da suke zama benci daya gajiya tayi da janta da zance ta haqura, idan ba Umaiman ce ta tambayeta abu ba itama seta kama kanta. Tana jin yan ajin na gulmar wai tacika girman kai bata kula kowa. Zance har sauran Ajujuwa cewar an kawo wata sabuwar Daliba kullum fuska a rufe kuma bata magana da kowa. Ita dai ba abunda ya shafeta dasu musamman data godewa Allah babu yan unguwarsu da yawa a Bangaren Safen nasu, yara ta yamma sukeyi saurab Matan unguwar kuwa yawanci ta Asabar da Lahadi suke irin tasu Mama.

Wannan Matar data ga ta shiga gidansu Maman Nana mabata sake ganinta ba tun zuwan farko, a bakin Malama Aisha taji cewar Bari tayi bata da lafiya shiyasa bata zuwa dan har yan Ajin sunyi qungiya anje dubata da tace mata ko zataje tace Aa kawai se daga baya ta sake jin maganar a bakin Anty ashe Amaryarsu ce, da yake itama Maman Nanan sun babe tuni tun farkon dawowarta gida ita ta ringa qarawa wutar gulmarta fetur a unguwa har tana fadar ita bata taba dauka ma airan Umaiman ze jima har haka ba'a sakota ba saboda halinta, ta ringa cewa yarinyar da take da fuska biyi, a gidanta take zuwa tayi shigar banzarta idan zata fita yawon barbada inta dawo taje can ta canza labari yayita yawo a unguwa data san Umaiman taji tun daga nan ta dena shiga gidansu kwata kwata ta dauke qafarta shiyasa ma Umaimah bata san an cika she mata kishiya ta uku ba kenan sun zama su hudu.

Anty ta aiki Firdausi takaiwa Maman Nana wata Riga ta gyara mata Zip, Maman Nana na chanza zip din ta shiga tambayar Yarinyar wai Umaimah tana nan kuwa tace mata eh, Samira Amaryar su na daga qofar Kitchen tana duba girkin data dora, sunan Umaiman ya tuna mata da sabuwar yar Ajinsu, bata taba jin sunan ba se a kanta ranar se yanzu da taji Maman Nana ta ambata. cike da son Gulma bayan Firdausin ta fita ta matsa gurin Keken Maman Nana dukda ba shiri suke ba take ce mata

"Niko sunan da nJi kin fada kamar na santa"
Maman Nana ta galla mata harara dan tafi jin zafinta duk cikin kishiyoyin da aka mata. Seda yaga mamorarta ta kusa qarewa yaje ya dauko musu yarinya me shegen kadifiri Sa'ar Nanarta rana daya ya aurar da Nanan ya qaro Amarya shi kuma gashi yanda yake lelenta baya ko jin kunyar idonsu itama ta samu guri tayita zuba musu iskanci a gida shiyasa basa zama inuwa daya. Tsaki Maman Nanan tayi tace
"Kika santa a ina? Matar da tun kan ki isa aure take kulle a gida babu inda take zuwa".
Samirah tayi murmushi tace
"Wlh Maman Nana, wannan data fita ba yar gidan Saratun Alhaji Sabo bace? To itama waccen haka naji sunanta Umaimah Sabo, ajin mu daya a Islamiyya wata doguwa siririya ko zuwana na qarshe tare muka jero kuma gidan naga ta shiga har na ringa tunanin ko Amarya aka musu saboda nasan Yammata biyu ne a gidan ko?"

Maman Nana ta aje Almakashi saboda jin gulma harda gyara zama tana cewa
"Doguwa Siririya? Kai Umaimah ba siririya bace amma qila rama tayi dan na fi shekara uku banganta ba tun ina shiga gidan amma bari na tambayo Nafisa dan ko shekaran jiya ta shiga ta karbo Atamfofi gurin babarsu" ta miqe jiki na rawa ta shige dakin ta biyun su, bata jima ba ta fito tana tafa hannu tace
"Aiko itace, dan Nafisa tace data shiga ta ganta da Hijabin makaranta ta dawo ikom Allah an gama kulletan kenan ta fara fita? Yo ko ta fita ko karta fita dai tambari ta rigada tayiwa kanta wlh, Allah dai ya wadaran dai naka ya lalace".

Samira ta sauke tunkunya ta dawo tana cewa
"Me tayi da ake boyeta? Badai wani ta kashe ba? Dani daman yanda take ta fama da Hijabi nata yafi na kowa tsaho kofa qafarta ba'a gani ga Niqab har aka tashi bata daga shi ba har wani Malami seda ya mata magana duk a wani darare take ina lura da ita kamar mara gaskiya ashe da walakin dan Allah wata kashe Maman Nana?"

"Mijinta ta kashe mana" Maman Nana ta fada, Samira ta saki Ludayin miya ta dafe qirji, Haulatu ta ukunsu dake daki tayi saurin fitowa jin abinda Maman Nanan ta fada tace
"Ke Maman Nana kiji tsoron Allah ta kashe Mijinta a ina?"
"Yo abinda ta masa menene marabarsa da kisa Haulatu? Ta kashe masa kayan aiki meyayi saura bari fa kiji" ta juya kan Samira ta shiga labarta mata qarya da gaskiyar yanda akayi. Samira ta ringa tsuma jikinta na rawa, Allah Allah take litinin tayi taje makarantar da ta kusa wata bataje ba tunda tayi Bari ta fake dashi taqi komawa dan daman Mijin ne ya sakata dole ba so take ba musamman da sauran ta Asabar da Lahadi suke zuwa ita kuma cikin sati.

Watanta daya Umaimah tana zuwa Islamiyya cikin lumana Kishiyar Maman Nana na komawa labari ya canza dan randa ta koma a ranar ta bajewa yan Ajinsu labarin wacece Umaimah wanda ta tattaro daga bakin Kishiyoyta.
Daga yanayin kallon da yan Ajin suka ringa mata daya banbanta dana kullum tasha Jinin jikinta, ta zauna a sit dinsu Aisha bata zo ba danta bashida lafiya haka ta gama darasin ranar a takure tana yin yanda maganganu suke tashi qasa qasa gaba daya seta tsargu dukda babu wanda ya kira sunanta ko ya saka da ita amma ta kasa nutsuwa. A haka ta rarrafa aka tashi ta kama hanyar gida tunda abokiyar tafiyar tata bata zo ba.

Washe gari kuwa ba iya kar yan Ajinsu kadai ta ga suna binta da kallon qurillah ba harda sauran mutante, abin yayi gaba, gani kawai ta ringayi ana shigowa Ajin kamar wani gidan Zoo duk kuma wadda ta shigo saitinta zata kalla ta kama baki ta juya. Wani rukuni da suka shigo a qarshe kafin Malamin da zone musu darashi ya shiga har kanta suka qarasa, wata daga ciki datafi kowa zaqewa taja tsaki tana cewa
"Ai dole mutum ya ringa saka Niqab yana rufe fuska tunda bashi da gaskiya, to se kuyi hankali kudai yan Aji kar abinya motsa ayi muku aika aika a cuceku kun san da tsofaffin yan daba aAjin" ta sake jan tsaki wadanda suke ta qananan maganganu a Ajin suka fashe da dariya. Suka hada ido da Matar gidansu Maman Nana take gabanta ya fadi saboda irin murmushin da tayi mata ta tabbatar da cewar ita ta kawo gulmarta da har tasa ta zama abin kallo kenan.

Ranar bata iya fahimtar abinda aka koya musu ba, Allah Allah tayi a tashi ta tafi gida, sun fito a hanya wasu Mata uku yan Ajinsu suka tareta. Kai tsaye daya ta kama Niqab din fuskarta ta fizge Daya daga ciki tace
"Ke kuwa Barira ya haka? Ya zaki cire mata abu haka kawai?"
"So nake naga fuskar munafuka, nifa tunda na fara ganin matar nan daman jikina ya bani Bata da gaskiya ashe kuwa qasurgumar yar Ta'addace tayi badda kama take rufe fuska to Asirinki ya tonu kaf makarantar nan babu wanda be san aika aikar da kikayi ba kika saukewa Mijinki kayan aiki tir da halin ki wlh" wadda aka kora da Barira ta fada har tana tofar da yawu qasa. Dake cikin hargagi take maganar se gashi hankalin masu wucewa yakai kansu suka fara tsayawa ana tambayar meya faru take kuwa suka shigar fadar abinda suka sani akan Umaiman.

Mata suka zagayeta, wadanda suka santa suka shiga Mamakin jin itace dan da yawa dauka sukayi ko garin ta bari tsahon lokaci tubda ta denaZobo babu Wanda ya san ya take ciki. Abin mata,a maimakon su tsawatar da tozarcin da ake shirin yi mata se suka hadu sukayi mata caaa da yawa so suke suga fuskarta tunda sunji labarin so suke suga idanunta kawai yanzu. Umaimah ta riqe Niqab dinda qamqam tana durqushe a qasa saboda yanda takeji kukan ma ya kasa zuwar mata. Zuwan Malam Najib Malamin Ajinsu ya ceceta, shi ya watsa taron dandazon Matan yace ta tashi se sannan hawaye ya balle mata ta shiga kuka tamkar ranta ze fita ba kuma taga laifin kowa ba sai kanta ita tayi abinda ya janyo har aka tireta haka.

Haka ta koma gida tana kuka kamar me, Mama bata bi takanta ba Anty ce ta ringa lallashinta da tambayar meya faru amma ta kasa ce mata komai. Washe gari bata tashi da niyyar fita makaranta ba amma Mama tace babu fashi setaje. Ta fasa mata kuka amma tayi mirsisi.
"Duk abinda kika gani kekika jawa kanki dan haka seki nemi jarumtar tarar kome zaki gani" Maman ta fada mata tayi ficewarta daga dakin haka ta shirya ba yanda ta iya ta tafi, a Ajin ranar ma seda suka sake tireta suka ringa jifanta da maganganu marasa dadi ta kwantar da kanta a Desk har sukaci suka cinye bata tankawa kowa ba. Kamar yanda Mama ta fada ita ta jawa kanta dole ta nemi qarfin guiwar tarar abinda ze sameta. Haka ta ringa rayuwa a makarantar cikin tsangwama da takurar dalibai, duk kashedin da shugaban makaranta yayi akan abinda aka matan basuji ba danhar suspending Barira da qawayenta akayi amma hakan besa Matan makarantar sun sarara mata ba. Kadan ne suke tausayinta irinsu Malam Aisha da ta tsaya ta zama bakin Umaiman, duk wadda ta fada mata maganar banza ita take maida musu da yake me bakice kuma ta iya tijara se gashi tayi maganin da yawa saga ciki musamman yan Ajin da suka addabi rayuwar Umaiman.

Abin ya munana ya zarce makaranta dan labari sabo ya koma a unguwa data fita an ringa nunata ana tuno ai ga abinda tayi. Majalissun Samarin unguqarsu suka samu nayi, sun kuma dana mata tarko jira kawai sukeyi lokacin da zata afka ciki yayi.
Wannan sabon yanayin ya saka damuwar da take ciki qara nunka tada saboda a baya iya damuwar yan gidansu ce yanzu kuwa tsangwama take fuskanta sosai daga gurin mutane tayi kuka akan haka harta haqura, ta saki zuciyar ta dole ta tunkari koma menene ba zata cigaba da buya tana gujewa Laifukanta ba Niqab dinma ta dena sakawa.

Wannan kwarin guiwar data bata kanta da kuma tasirin addu'ar da takeyi babu dare babu rana yasa ta samu sauqin Al'amura. Taci gaba da zuwa Islamiyyarta masu gulma da zundenta har sun gaji babu dai me kulata in ka cire Malama Aisha da tsirarun yan Ajinsu wannan be dameta ba karatunta takeyi dan shine a gabanta ba kuma neman qawa takeyi ba dan ta shata ta warke.

An samu dogon hutun yammakaranta, babu tsammani sega su Mu'ayyad an kawosu da Jakar kayansu abinda ba'a tabayi ba ko na kwana daya tunda ta bar gidan Ubansu. Zuwan yaran ya sake rage mata kewa da gaske dukda ta wani bangaren zuwan nasu Fami ya zamar mata na abinda take qoqarin shafewa daga rayuwarta. Tunda Bibi ta qyalla ido taga wayarta data sake ajiyewa dan ba abinda take da ita. Ba me kiranta babu wanda take kira social media kuwa bata gabanta ma yanzu kullum sedai kawai tayi mata chaji ta ajiye amma tunda su Bibin suka zo ta samu wayar shikenan ta banu ta mayar da ita kamar tata. Kullum seta kira Dadynsu idan suna wayar sedai Umaimah ta tashi ta fita saboda abinda takeji. Iya kallon Mu'ayyad ya isheta tashin hankali, a shekaru sha biyun da yake gaba daya ya rikida ya zama Khalil, kamanninsa, tafiyarsa, maganar da komai nasa na Khalil ne.

Idan yana cin abinci zama take ta zuba masa ido dan hatta yanda yake riqe cokali da tauna abincin sak Khalil, lokaci da yawa seta juya gefe ta share hawaye, babu abinda ya ragu daga ranta na daga soyayyar Khalil sedai ma abinda ya qaru son zuciyarta ya rabata dashi gashi suna raye cikin duniya daya amma yafi qarfinta. Idan suna waya da yaran se taji kamar ta kwace taji muryarsa, haka wani sa'in kasa riqe kanta takeyi ta kirashi amma kafin ya dauka seta kashe shi dan bata san me zata ce masa ba. Tana so suyi magana, ta roqi yafiyarsa amma ta gagara hada wannan jarumtar, a haka hutu ya qare yara suka koma gidansu. Ranar da zasu tafin da kansa yazo daukarsu tareda Humaira data qara zama wata hamshaqiyar Mace. Tana cikin irin matan da shayarwa take karba suyi kyau su cika ga jin dadi da zaman cikin raba ya qarawa farar fatarta kyau da sheqi duk inda ta wulga daukar ido takeyi.

Yanda ta ringa fara'a tana gaida Umaiman ya soketa ta ringaji da biyu take mata haka, ta gama hade musu kayansu tana jiyo tashin hirarsu a falon Mama Bibi ta shigo tana tura baki ta fada jikinta, murmushi tayi kawai tun safe take rigimar ita ba zata tafi ba anan zata zauna seda Mama ta binciko Dorina ta ajiye kafin ta shiga taitayinta. Iman ta shigo tareda Aryaan Umaimah ya kalleshi fari tas kamar ka tabashi jini ya fito a haka zaka dauka da Mamansa yake kama amma ita tana kallonsa ta hango kamanninsa da Khalil sedai banbancin launin fata ya boye wasu. Tayi masa murmushi kamar yanda shima yakeyi Iman na kallon Bibi tace
"Dady y????""""""" "
" " "
""""""""""""""""""" "!"""#"$"%"&"'"(")"*"+","-"."/"0"1"2"3"4"5"6"7"8"9":";"<"=">"?"@"A"B"C"D"E"F"G"H"I"J"K"L"M"N"O"P"Q"R"S"T"U"V"W"X"Y"Z"["\"]"^"_"`"a"b"c"d"e"f"g"h"i"j"k"l"m"n"o"p"q"r"s"t"u"v"w"x"y"z"{"|"}"~""?"ace kizo mu tafi"
"Ni bazan tafi ba" ta fada a tsiwace Umaimah ta daki bayanta ta zabura dan taji zafi ta kalleta tace
"Wuce ku tafi, daman karki fasa halinki kinji ko" hawaye ya zubowa yarinyar se kuma Jikin Umaiman yayi sanyi, duk cikinsu ita ce me qulafucinta sauran basu wani damu da rashinta a gidan ba ko sun damu basa nunawa ita kadai take damuwa da son ta koma gidansu.

Hijabinta ta zura dogo jin sun fito daga dakin Maman. Mu'ayyad ya shiga ya fara daukar musu kayansu yana fita dasu ta fito masa da ragowar qofar dakin ta tsaya. Kanta na qasa tana jin suna sallama da Mama, bata so ta dago balle taga abinda ze sosa mata rai, dariya da kuma muryar Khalil dataji dab da ita ta sakata dagowa ba tareda ta shirya ba. Yana riqe da Abid yanayiwa Humairan magana fuskarsa a washe ita kuma tana dariya wani abu ya dirar mata a zuciya amma tayi qoqari ta hadiye jin Humairan nayi mata sallama ta amsa yanda be kulata ba haka itama ta dauke kanta har suka fice daga gidan kafin ta koma daki tayi shiru.
Wunin ranar haka tayi shi babu dadi, ga kewar yaranta ga tasowar tsohon tsumi, duk yanda taso tayi baccin a daren ya gagareta. Ta tashi tayo Alwala tayi salloli, qarfe uku da wasu mintina haka kawai ta dauki wayarta ji takeyi tamkar idan bata kirashi ba zata iya madewa hannunta na rawa qirjinta na bugawa ta dannan kiran muryar matar kamfanin Mtn ta shaida mata da cewar layin a kashe yake, seta sauke ajiyar zuciya me nauyi ta kifa kanta tsakanin cinyoyinta hawaye suka shiga yi mara tsere. Ta dade tana kukan daga qarshe ta lallabi kanta tayi haquri.

Babu zato Abba ya bata offer aiki a qarqashin Ma'aikatar sadarwa ta Jaha. Ranar rasa abin cewa tayi se kuka da godiya kawai dan abin yazo mata a bazata, bata san da zancen neman aiki ba bata ma taba zaton za'abarta tayi aiki ba se gashi Abban da kansa ya nema mata seda komai ya kammala kafin ya sanar dasu. Inda gizo yake saqar rashin sanin ta inda zata fara, se take ganin kamar ba zata iya ba amma da Abban ya zaunar da ita ya sake yi mata nasiha tareda gargadi seta samu nutsuwa a ranta. Kafin ta fara zuwa aikin seda Salman ya sake koya mata abubuwan computer dan tace ta manta komai abin Mamaki kuna daya fada mata zata tuna yanda akeyi kodan tana buqatar aikin ne yasa kwakwalwarta tayi qoqarin tuna duk abinda ta sani a

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login