Showing 135001 words to 138000 words out of 429394 words

Chapter 46 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

1020

yanzu haka cikin karbar gashinta yake idan har haka Hadiza takeji a kansa idan ya barta beyi mata Adalci ba.

Umaimah kanta ta lura da rashin walwalarsa data tambaye shi yace mata bayajin dadi ne ga kuma ayyuka da suka yi masa yawa ta ringa mitar ai shi yake dorawa kansa me yasa duk Architects din da suke a kamfaninsu ace duk wani babban aiki shi ze ringa kula dashi ai se a bawa wasu dama. Sanda take maganar kallonta kawai yayi, shi kam Umaimah ta dena bashi mamaki yanzu dan duk abinda tayi yana tsammanin zatayi wanda ya fishi, yanzu ita ba Jin dadinta bane ace Allah ya daukaka shi cikin daruruwa shi aka zaba Aa mita takeyi akan me yasa akayi hakan toh Allah ya rufa Asiri, shidai Tsuntsun soyayyar sa beyi masa Adalci ba daya rasa inda ze sauka se akan wannan butsuwar yarinyar.

Be samu zama da Jalila ba se bayan sati daya ranar Weekend yacewa Umaimah ta shirya suje gidan dukda yasan ba zuwa zatayi ba latsine, ya rasa me yasa yanzu take ja baya da yan uwan nasa wanda sam farkon auransu ba haka bane sosai suke shiri take daukarsu tamkar su Yaya Naziyya amma tunda ta haihu abubuwa suka chanza, shi kansa gidan Hajiyar da take yawan zuwa ta rage sedai ta kirata a waya su gaisa wannan dai babu fashi kullum ta Allah seta kirata.

Umaimah ko daya gaya mata zasuje din kaitsaye tace bazata ba saboda akwai sunan Mariya maqociyarsu da za'ayi a ranar Amaryace matar qanin Mijin Maman Hibban da sun fara zama a wata unguwa barayi suka damesu shine ya gina filin jikin gidan Maman Hibban din inda sukayi Suna suka tare a anan.
Ya gama shirinsa tsaf ze fita tana zaune a palour kanta ne yake sara mata haka a kwanakin take yawan fama da ciwon kai wani lokacin harda jiri ta gayawa Khalil yace yawan kallon waya da takeyi gashi bata samun isashshen bacci ta raba dare Online su suka saka shiko ya dena mata magana duk yanda tayi daidai ne tunda tana masa abinda yake so idan ta gama can taje ita ta sani.

"Baka bani kudin barka ba toh zaka fita" Umaimah ta fada jin yana mata sallama, se ya kalleta yace
"Kudin barka kuma? Ina kudin da kike kaiwa can gidan duk sati da kikace kuna tarawa ne saboda irin haka idan hidima ta tasowa wani se a bashi a madadin matan unguwa?"

Baki ta tura tace
"Toh ai wancan na gidauniya ne wannan kuma personal ne da zan bata"
"Ai Namiji kika ce ta haifa ki duba cikin rigunanku ki kai mata ko ki dauka a kudin dana baki jiya ni banda kudi yanzu" yana gama fada ya saka kai ya fita yana mamakinta. Jiyan nan dubu talatin ya bata wai zata siyi kayan gyara, sannan duk satin duniya se ya bata dubu biyu ta zubin gidauniya data ce banda idan ya samu kudi haka kawai ma bata yakeyi ko idan zata fita unguwa duk suna ina da seya bata kudin wata barka ai bashi ya aiketa ba.

Da dai Umaimah bazatace ya bata kudi ba duk abinda yaga dama ya bata zata karba tayi godiya wani lokacin har tace ya rage saboda tana tausayinsa amma yanzu ta zama yar fashi daga zaune. Bill ne take masa harda na banza, ana zaune lafiya zata qirqiro abu tace tana so idan yaqiyi kuma ta ringa fushi da baqin rai kenan da mita har se ya mata abinda take so yanzu a ritsin nan Iphone 13 ta saka seda ya siya mata shi yana fama da X tun kafin auransu be chanza ba ita kuwa 12 take riqewa rana daya tace duk qawayenta 13 ce dasu dole ya karbi ta hannunta ya cika aka bata wata.

Umaimah kuwa harara ta rakashi da ita babu arziqin a dawo lafiya tunda ya hanata kudin barka. Shifa yace dan ita yake nema a da tausaya masa takeyi ganin yana da dawainiya dayawa akan sa amma tunda Rufaida ta wayar mata dakai ta dena. Ita ta koya mata dabarun karbar kudi a hannunsa dukda kota karba ba wata tsiyar take dasu ba sedai rantawa qawaye da zubin Adashi se siyi banza siyi wofi abin kirki kadai da zata ce tana siya shine kayan gyaran jiki wannan ko bata wasa dasu dan da jikin take yaqarsa tayi iskancinta son rai kuma taci riba.

Kiran wayarta ne ya dakatar da ita ta janyota, Rufaida ce tana dagawa tace
"Madam kin shirya mu shiga gidan sunan kuwa?"
"Na dauka seda yamma ai" Umaimah ta bata amsa se tace mata
"Aa zamu shiga yanzu mana muga koda abinda zamu kama musu"

"Gaskiya sedai kije ni se zuwa yamma bana jin dadi kaina yana ciwo" Umaiman ta sake fada cikin jimami Rufaidan ta mata sannu tareda cewa bari ta shigo toh. Basufi minti goma da waya ba taji bugun qofa taje ta bude mata ta shigo ta zumbulo Hijabi da gani ko wanka ba tayi ba, seda suka zauna take tambayarta
"megidan baya nan naga babu motarsa".

Baki Umaimah ta tabe tace
"Ya tafi gidan Anty Jalila"
"Kice yau seta Allah ko ba ita ce tazo kwanaki da qanwar Mijinta ba?" Rufaida ta fada tana gyara zama Umaimah ta girgiza kai alamar Aa kafin tace
"Ba ita ba wannan Yan biyunsa ce ba Anty Amina ba ita ce babbarsu"
"Au wai yan biyune, toh Allah ya fishsheki dan kinsan idan ka hadu da yayyen Miji mata se a hankali musamman keda ake ganin kina ciki daula yanzu se kiji zantuka kala kala".

"Uhm" kawai Umaimah tace tayi shiru, hudubar Rufaida ta rigada ta gama tasiri a zuciyarta ita ta nuna mata tunda yayyen Khalil matane bazasu sota tsakani da Allah ba zasu ringa kishi da ita suna ganin Dan uwansu na bauta mata yana mata abinda su basa samu a gidan auransu dalilin da ya saka taja baya dasu dukda ko kallon banza babu wadda ta tabayi mata a cikinsu, yanzu hatta da Habiba da take yar gidanta ta rage kiranta tazo gidan acewar Rufaida zata ringa kwashe sirrinta tana kaiwa gida ita kuma taga hakan ze yuwu.

Nan suka zauna basu shiga gidan sunan ba se bayan la'asar Rufaida ta koma tayo wanka itama ta shirya bayan Hauwa ta dauki Mu'ayyad ta tafi dashi gidansu seda aka yi Isha'i suka baro gidan sunan ta shiga gida har sannan kuma Khalil be dawo ba.

Khalil
Seda ya fara biyawa gidan Abokinsa Mukhtar da yake shirin angwancewa nan da sati uku, fenti akeyi, ya duba masa aikin suka dan taba hira kafin ya wuce gidan Jalila.
Cikin murna ta tareshi dan ya dade rabonsa da gidan nata, ita kadai ya tarar se Almajirinta yana mata wanki a tsakar gida suka shiga ciki ta kawo masa ruwan Lipton da Dumamen tuwo miyar Kuka yaji man shanu.

"Kai amma Allah ya tsundumaki a Aljanna kamar kinsan na kwana biyu banci tuwo ba" ya fada sanda ya bude kwanon.
"Ai tun da kace mun yau da safe zakazo, banyi niyyar tuwo ba jiya saboda kai nayi nace dan qanina nasan ba lallai Maman Mu'ayyad nayin tuwo ba balle ka samu dumame".

Hannunsa ya wanko a Kitchen ya saka tuwon a bowl hade yake da miyar ta dumama irin yanda yake so yayi bismillah ya fara ci ita kuma ta tsiyaya masa baqin shayin daya sha kayan qamshi a kofi.
Seda ya cinye tas yasha shayin yayi hamdala, shi ya kai mata kwanukan kitchen ta rigada tayi wanke wanke dan haka ya dauraye wanda ya bata ya kife mata su a kwandon daya gani cikin sink ya futo da gorar ruwa a hannunsa.

"Ashe dai har yanzu kana aikin gida" ta fada cikin tsokana ya zauna yana murmushi yace
"Nasan mitarki idan na ajiye ban wanke ba har na tafi kina mun surutu"
"Kasan haka muke da Abbansu tun be iya wanke wanke har seda ya saba yanzu da sun bata kwanuka zece a wanke se kaji Zee tana ayi wanke wanke kafin Mama ta fara mita" suka saka dariya gaba daya.

"Ina yaran nema naji gidan shiru" ya tambayeta bayan daya zauna tace
"Kamal da Asiya sun tafi Tahfiz, Nuradden kuma yana Jalingo kasan Hajiya da Didi kuma qanwarsa ta kai su gidan kitso jiya wai sunyi dare suka kwana a gidanta inaga se anjima zata dawo dasu"

"Wai har yanzu Nuraddeen be dawo ku haqura da yaron nan kawai ku bar musu shi mana" Khalil ya fada tayi murmushi tace
"nima haka nace jiya da yake zancen ze kira Hajiyar ya gaya mata an dade da komawa makaranta nace ai sun sani ka barshi kawai yayi zamansa nan da can ai duk daya ne toh kasan shi da qulafucin Yaya bedai ce komai ba kuma be kirata ba yana dai mitar wai Nura nada wasa baya sonkaratu idan ba an takura masa ba acan in ya samu sake sangarcewa zeyi"

"Haka dai ze haqura ya barshi da ya samu kakannin ma masu so su riqe jikan, nan Hajiya data dauko Inteen kina ganin yanda suka qare" Khalil ya fada suka fashe da dariya gaba daya. Seda suka lafa Jalila ta kalle shi tace
"Toh ya ake ciki ranar mun fara magana a waya?"

Tattara hankalinsa yayi akanta yace
"Wato wata yarinya ce muka hadu da ita kin gane, harga Allah tana burgeni kuma ina sonta amma kuma ni banyi tunanin nan kusa zata kawo maganar muyi aure ko wani abu ba kuma ita bala'in sona takeyi, nidai in taqaice miki magana yanzu kinsan dai matsayin da nake ciki a yanzu bazance zanyi aure ba saboda kowa seya tambayeni dalili idan kika duba aurena shekara biyu kwata kwata ni kuma bani da wani dalili me qarfi dazance gashi ya saka zanyi aure".

Shiru Jalila tayi tana kallonsa har ya kai aya kafin taja numfashi tace
"Ita yarinyar yaushe kuka hadu, kuma tsahon wane lokaci kuke tare?"
"Bamu wani dade ba wata uku zuwa hudu kenan da haduwarmu lokacin da naje aiki Lagos din nan, dukda dai mun taba haduwa a nan Kano amma dai Officially mu fara magana da ita yanzu za'ayi 3 months" Khalil ya bata amsa tayi shiru tana kallonsa, so takeyi tace masa lokacin da Umaimah taqi binsa Lagos kenan kuma ta tambayeshi wace irin alaqa ce tsakaninsu dukda bata zargin qanin nata amma tasan abinda Umaiman tayi masa yana iya sakawa shedan ya zugashi ya fada abinda ba halinsa ba. Itama ta samu labarin ne a bakin Khalifa kuma ya roqeta akan dan Allah karta gayawa Kowa dan Yaya Khalil yaja masa kunne kawai ya kasa hadiye maganar ne yasa ya gaya mata dan ita ana sirri da ita ba irin su Yaya Jamila faransai bace.

"Kinyi shiru kina kallona kamar wanda nayi miki qarya" Khalil ya fada se tayi murmushi tace
"So nake na auna soyayyar da kakeyi mata da irin wadda na gani a idonka sanda kake gaya mun ka hadu da Umaimah"

"Babu hadi Jalila babu macen da zata kamo qafar Umaimah a zuciyata" Khalil yayi saurin tareta a zuciyarta tace
"Ta gano lagon ka shiyasa take garaka kamar kwallo a fili kuwa seta gyara zamanta tace
"Toh tanada wannan matsayin ya akayi har idonka ya iya hange hange ka samo wata ka fara so, kuma a yanda kake jaddada soyayyar nan tata ace a ayan shekarun nan zaka mata kishiya Khalil?
Idan har da gaske ka daukeni yar uwar da zamu kashe mu rufe ka gaya mun gaskiyar meye damuwarka, meye dalilinka na son qara aure? Ni kuma zanyi maka hukunci bisa adalci in sha Allah dan bazan so ka tauye kanka ba haka itama Umaimah bazan bi bayanka kayi mata rashin Adalci idan har ya zamana son ranka ne kawai".

Shiru Khalil yayi yana nanawa maganarta a zuciyarsa, yanada yaqinin Jalila zata riqe masa sirri idan ya gaya mata amma yana tsoron ta farayiwa Umaimah wani kallo na daban a matsayin me musgunawa dan uwanta, yasan zata qullaceta dan Jalilan nason duk abinda yake so tana kuma qin abinda yake bata masa.

"Kayi shiru dan qanina ko da akwai matsala ne" ta fada cikin tsokana ya dago ya harareta tayi dariya tace
"Sarkin son girma duk tsiyarka dai minti biyar ba wasa bace" dole yayi murmushin shima ta sake cewa
"Yawwa ina jinka kayi magana mu samu mu san ta inda zamu kamo bakin zaren maganar nan"

"Kina ji Jalila ina son Umaimah kuma bani da wata matsala da ita, damuwata guda daya ce kawai yanayin aikina da bana zama guri daya a koda yaushe ana turani garuruwa nayi ayyuka kuma ina yin kwanaki wani lokacin ma satittika ni kuma ina da sha'awar duk ina zani na tafi da Matata, matsalar anan ita kuma Umaimah bata son tafiya.
Duk sanda wata tafiya ta taso se rayukan mu sun baci kafin ta bini, kinga last tafiyar da nayi Lagos har na gama zamana na dawo bataje ba acan nema na hadu da Hadiza dan a lokacin fushin da nake ciki na yanke shawarar aure kawai zan qara na auro wadda ko bangon duniya nace zanje zata bini"

Yaci gaba da bata labarin yanda ya hadu da Hadiza da irin soyayyar fa sukayi har zuwa matsayin da suke yanzu akai na zancen turowa da tayi masa. Ya rufe da cewa
"Banaso haqqinta ya kamani dan dagaske yarinyar tana so na ni kuma bansan ya zanyi ba yanzu.
Tun bayan dawowata na tuntubi Hajiya da maganar dan naji ta bakinta tayi futufutu tace babu wannan maganar ba yanzu ba har gaba babu ita.
Toh ni maganar Hajiya ma da sauqi nasan idan na lallabata tana iya yarda, Umaimah nada bala'in kishi irin wanda bakiyi tunani ba, idan zancen auran nan ya fito na tabbata babu sauran zaman lafiya tsakanin mu".

"Hmmmm" Jalila taja dogon numfashi tareda sauke taguminda tayi tana kallon Khalil tace
"Ni har na rasa ta ina zanfara ma, idan na fahimceka abinda yasa ka fara kula Sabuwarka saboda rashin Umaimah a kusa ne bari na fara da wannan bangaren in har kana ganin cewar Umaimah bazata haqura ta ringa binka duk inda zakaje ba kana da hujjar da zaka qara aure kuma duk wanda ka gayawa dalilinka baze hanaka ba kodan gudun fadawa halaka.
Amma idan shawara kake nema se nace maka qarin aure ba shine mafita ba ka zauna da ita kuyi magana ta fahimta ka nuna mata buqatarka da abinda bijirewa hakan ze iya janyowa idan har bata gyara ba daga nan kana iya daukar mataki na gaba sannan ita wannan Hadiza kace kowa sunanta ba son ta kakeyi ba, Umaimah ta riga ta siye filin a ganina ka saurareta ne kawai a lokacin saboda fushin Umaimah inda dagaske ka gantan kake sonta zuciyarka bazata kawo maka wani tunani ba balle har ????? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ?  kaji shayin tunkarar kowa da maganar auranta.

Kuma koda ace ka aureta be zama lallai ka iyayin adalci a tsakaninsu ba, idan auran kake so dagaske ka bari ka samu wadda soyayyarta tayi takara data Umaimah a zuciyarka idan ba haka ba yanda kake Son matar nan kake tsoronta duk wadda ta shigo gidanka bayan ita wahala kawai zata sha".

"Kema bakya goyon bayan maganar kenan?" Khalil ya tambayeta fuska babu walwa kafin tayi magana yaci gaba da cewa
"Ni wallahi tsoron hakkinta ya kamani nakeyi na san soyayya nasan zafinta, bakiga irin Kukan da takeyimun ba jiya tana nanata tana sona naji tausayinta sosai"

"Tausayinta kakeyi ba Son ta ba Khalil, idan kuwa hakane ka barta kayi mata Addu'a Allah ya bata wanda ya fika dan bata da gurbi a zuciyarka Umaimah ta gine duka filayen sedai idan rusau za'ayi" Jalila ta fada cikin tsokana a zuciyarta tana sake auna maganar Khalil din, ita dai a iya tata Basirar abinda ta gani kenan, ba son hadiza yakeyi ba tausayinta yake kuma fushin Umaimah ne ya saka shi harya fara kulata, ko a yanzun bata raba daya biyu bata masa rai tayi shiyasa har yake tunanin yayi auran.

Tattaunawa suka cigaba dayi akan Abubuwan da suka shafesu har suka gangara batun gidansu daze siya da yanda yake so yayi dashi, be bar gidan ba se gurin qarfe uku na rana shima saboda Mansur ya kirashi yana so su hadu ya tafi bayan ya cikata da Alkhairin dayaje mata dashi tanata godiya, suna son dan uwan nasu saboda yanda yake sonsu.

Maganar da sukayi da Jalila ta saka ya qara ja baya da Hadiza kuma ya yarda dagasken ba son ta yakeyi ba tausayine da kuma huce takaici da yaso yayi da ita amma dukda haka yana tausaya mata, kullum cikin rarrashinta yake da gaya mata cewar ta fawwalawa Allah idan hat ya qaddara zasuyi aure zasuyi a sanda yaso.

Data matsa masa akan Yayanta yace yana son ganinsa ranar ya haqura yaje, be boye masa komai ba ya gaya masa uzurinshi ya kuma fahimce shi yayi musu fatan Alkhairi idan Hadiza matarsa ce Allah ya tabbatar, bayan ya gama da Yayan ya turo masa ita sukayi magana, kamar ze zubda Hawayen tausayinta saboda yanda duk ta rame dalilin damuwar da ta saka kanta a ciki. Haquri ya bata tateda lallashi, yace mata baze ce ta jirashi ba, amma idan da rabon aure a tsakaninsu yana fatan Allah ya matso musu dashi kusa sannan ya roqeta da suci gaba da gaisawa idan tana ganin babu matsala tace zatayi tunani haka suka rabu rabuwar da yake ganin sunyi ta kenan shida ita.

Ciwon kai da jirin da suka matsawa Umaimah ya saka dole sukaje Asibiti wata ranar Litinin, bayan likitan yayi mata yan tambayoyi ya auna jininta ya rubuta mata magunguna akan taje tasha idan bata samu afuwa ba su sake komawa. A hanya Khalil ya ringa mata fadan rashin bacci da wuni da takeyi akan waya dan hatta idonta jini ya kwanta shiyasa likitan be kawo tunanin kowanne ciwo ba yace rashin bacci ne ta ringa samun isashshenhutu suna tafe ta tunzura baki gaba saboda fadan da yake mata kai tsaye gidan su ya kaita, idan da Umaimah tasan can ze ajiye ta yasan bazata yarda ba dan tunda ta gudo kamar yanda Anty ta fada bata sake komawa ba.

A tsaitsaye suka gaisa yayiwa Mama bayanin bata da lafiya daga Asibiti suke, ya qarasa da cewa
"Dan Allah Mama ki saka mata ido ta samu tayi bacci karta zauna danne dannen waya"
"Uhm abin nata har ya kai ya

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login