Showing 75001 words to 78000 words out of 429394 words

Chapter 26 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

977

ba'a jiki ta ba kai gani take kamar ya qarata ma ai kuwa bazata yarda ba dole ta dauki mataki akai tunda akan gaskiyarta take da idonta ta ganshi da karuwar kuma tayi magana ya hakke mata kamar wata Baiwarsa Allah yana kallo kuma seya saka mata.

Sanda ta fito Khalil ya dade dayin bacci abinsa tana tafiya kamar yar kaciya ta bude ledar magungunan da aka bata ta dauki Paracetamol tasha, seda ta qara hada shayi me kauri tasha kafin ta koma kan doguwar kujerar dake dakin ta kwanta tana jin jikinta kamar ana kwankwatsata tsabar yanda ko ina ya dauki ciwo.

Da Asuba daya tashe ta dakyar ta miqe shi kuwa har yayi shirin masallaci ya fice abinsa ya barta da matsar kwalla saboda yanda jikinta ya sakeyin tsami ga azabar zafi da takeji a qasanta se kawai ta zauna a gun ta shiga rusa kuka. Seda gari yayi haske ya koma dakin har sannan zuciyarsa babu dadi, idan ya tuna kalmar karuwa da take jinginashi dashi se yaji sam Umaimah bata dace da zama matarsa ba, bata ganin mutunchinsa bata qimanta shi duk menene ya jawo hakan.

Sanda ya shiga dakin beyi niyyar kukata ba amma ganin yanda fuskarta ta canza ta kumbura ya bashi tsoro dole ya qarasa kanta yana kallonta da alama ko sallar batayi ba tana nan yanda ya barta, murya a daure yace mata

"Baki tashi kinyi sallah ba ko?"
"Bazan iya tashi ba dan Allah ka kaini Asibiti jikina, marata ko ina ciwo yake mun inaga ma mutuwa zanyi" ta fada cikin kuka, seya kama hannayenta da niyyar miqar da ita ta fasa qara saboda azabar zafin da taji, da sauri ya durqusa a gabanta yana kallon yace

"Kwanta mu gani" ya fada yana qoqarin daga dogon Hijabin jikinta, bata da qarfin hana shi ba yanda ta iya ya bude jikinta ya kunna fitilar wayarsa ya haska, saurin kawar da kai yayi wani irin tausayinta ya tsirga masa. Sosai yaji mata ciwo dukda ba likita bane shi amma yasan wannan raunin ko ba'a dinke taba dole se an mata yan dabaru zata dawo dai dai, kallonta yayi yanda ta rufe ido tana tsiyayar da hawaye bayan duk ita ta jawo komai, bata jin magana ya rasa wace irin zuciya Allah yayi mata da sam bata san daidai ba se rashinsa.

A akwatinta ya dauko doguwar riga mara nauyi ya zura mata tana kuka dukda yanda ya ringa lallaba mata jiki kamar me taba kwai ya dauketa a hannu ya fita da ita, kafin su isa Asibitin seda yaji kamar shima ya fasa kuka saboda yanda ta gigita masa kwakwalwa da kokekokenta da ya tabbatar bayah na ciwo harda na jidalinta.

Sunyi sa'ar tarar da likita macece on duty a Asibitin daya kaita jiya ta ringa surfa masa bala'i kamar zata dake shi sanda ta duba Umaiman dan ita a zatonta ma Amarya ce daren farko, Alluran rage zugi da ciwo tayi mata ta bata wani magani na shafawa tace ba se tayi mata dinki ba ta dage da shiga ruwan dumi ta kuma ringa cin Nama me romo da fruits gurin ze warke kar kuma ta kuskura ta koma masa se taji jikinta ya dawo daidai so samu ta dauki kamar wata biyu tayi jinya shidai Khalil jinsu kawai yake tana wa Umaimah huduba a ransa yace
"Ba'a koya mata abin tsiya bama tayi inaga an bata lasisi".

Ranar haqura yayi da fita site ya kira ya bada uzurin Madam bata da lafiya, dukda be sakar mata fuska ba amma ya tsaya ya bata kulawa sosai dan motsi idan tayi seya tambayi me take so idan zata shiga bandaki kuwa daukarta yakeyi ya kaita ya kuma tsaya seya tabbatar da ta gasa jikinta kamar yanda Likita ta fada sannan ze rabu da ita.

Duk yanda Umaimah taso da ta samu kansa abin yaci tura dan ta fahimci fushin nasa me girma ne dan ba ita kadai ba ko kiransa akayi a waya daga yanda yake magana zaka fahimci yana cikin damuwa. Tayi nadamar abinda tayi ko babu komai da yanzu bata karbi sakamon wannan Azabar da take ciki ba abinda ko daren farkonta baya fuskanta ba gashi babu wannan sakin fuskar da tarairayar data saba dasu duk abinda yake mata kamar wanda akayiwa dole.

Da sukazo kwanciyar bacci ma kan kujera ya kwanta ya bar mata gadon, tayi masa magana ya mata banza seta saki kukan da dama yana maqale a wuyanta ya kuwa shareta data ishe shima ya saka Airpod ya toshe kunnensa dan kanta tayi ta gaji bacci ya kwasheta.

Khalil kuwa wani irin kallon takaici yabita dashi, a cikin halayenta yana daga abinda yake qona masa rai bata san idan tayi kuskure ta bashi haquri ba. Duk sanda abu ya hadosu sedai idan ya gaji da fushinsa ya sakko ko tayi ta rara gefe sa shagwabarta ta banza har ya sakko amma dai ace ta bude baki ta bashi haquri bata iya ba.

Shi gaba daya ya rasa ma inda ze sakata ne, bata da ladabi sam be kuma san yanda ta dauki rayuwar aure ba amma ze koya mata hankali, daga yanzu baze sake bari wata yaudararta tayi tasiri akansa ba, dole ta koyi ladabin idan ma bata dashi dan baze yarda su dora rayuwa a haka ba.

Washe gari jikin nata yayi sauqi dan haka ya fita gurin abinda ya kawo shi, honeymoon dai ya koma zamandoya da manja dan haka suka cinye kwanakin da zasuyi idan ya fice tun safe se dare ze dawo, kuma haka zaau zauna magana idan ba wadda ta zama dole ba ko tayi masa baze amsa ba. Tun Umaimah na daukar abin wasa har yazo ya fara damunta.

Koda suka dawo Kanon ma bata chanza zani ba sema qara tabarbarewa da zaman nasu yayi dan gaba daya ya fita a sabgarta takai ta kawo ko gaishe shi tayi sedai ya daga mata hannu wanda daman ba kullum ba ne take gaisuwar yanzu nema da aka shiga wannan yanayin take neman abinda ze sa suyi magana ta dage da gaisuwar.

Daman tunda suka dawo ya raba musu daki, acewarsa likita tace ta samu hutu sosai shi kuma baze iya jurewa suna kwana gado daya ba dan haka ta koma dakinta tayi jinyar, girki ma ya sauwaqe mata abin kari da kansa yake shiga kitchen ya dafa idan yaje aiki yaci na rana acan wata rana yayiwo take away idan ze dawo ko ya biya gidan Hajiyarsa yaci wadda ita a zatonta laulayinciki ne ya saka Umaiman bata iya girji dan haka idan yaje seta zubo musu ko haka kawai ma ta dafa abun kwadayi ta bawa Habiba ta kai mata.

Wasa wasa sun kwashe sati kusan uku a cikin wannan halin, tun Khalil najin wani iri akan matakin daya dauka musamman idan yaga ta zauna tayi shiru har ya zamana abin ya zamar masa jiki ya fara sabawa da rayuwarsa shi kadai.

Umaimah kuwa gaba daya ta fita hayyacinta musamman da laulayi yayi mata dirar mikiya ga rashin kulawar datake fuskanta daga bangaren Khalil gaba daya se abin ya hadu yayi mata yawa. Wauta da rashin wayo irin nata sun kasa barinta ta hango kuskurenta ballantana ta gyara sannan ta gaza gayawa kowa a nata shirmen zata iya fuskantar matsalarta ita kadai sedai abin ya zama ana bata goma biyar bata gyaru ba.

Wata safiyar Laraba ta tashi bata jin dadin jikinta, a kwanakin daman gaba daya qarfin hali kawai takeyi ita ba zazzabi ba ba wani takamaiman ciwo ba amma jikinta sam baya mata dadi se taji kamar tayita ihu ko zata ji sauqin abinda yake damunta gashi babu abokin hira ballantana ta fada masa damuwarta ya tayata koda kalamai masu dadi ne taji sanyi.

Tun asuba data idar da sallah bata koma ba saboda tana son magana da Khalil din gida take so taje dan tunda suka dawo bata fita ko ina ba. kusan kullum bata sanin fitarsa, data dan koma baccin safe sedai ta farka taga ya fita ko ta tarar da saqon kudin cefane ya ajiye mata a palour dukda itama ba girkin take ba yayime yayime kawai take taci.

Tana zaune ya fito daga dakinsa cikin shirin fita tsaf dashi kai bazakace yana da wata damuwa ba. Ta bishi da kallo dakyar ta iya tausar zuciyarta ta gaishe shi ya amsa mata a taqaice yana nufar qofa seta bi bayansa tana cewa

"Magana nake so muyi"
"Toh yanzu kuma? Gashi sauri nakeyi na kusa makara ko zaki bari sena dawo idan ba na sauri bane" ya fada yana qare mata kallo dan qarara ya hango ramar da tayi se dai ta qara haske da kyau.

Yamutsa fuska tayi tana kallon gefe tace
"Ni gidan mu nake so na tafi bani da lafiya ni kadai na san me yake damuna kar nazo na mutu a gidan nan babu wanda ya sani tunda ba'a damu dani ba"

"Me hali baze chanza ba" Khalil ya fada a zuciyarsa yana maimaita kalamanta a ransa da sam babu ladabi ko tausasawa a cikinsu a fili kuwa ya gyara tsayuwa yace mata

"Wa kika gayawa baki da lafiya kuma waye be damu dake ba?"

"Kai mana, daga fadar gaskiya gaba daya ka dena kulani ka fita harkata a gidannan sena shafe kwanaki magana bata hadamu dakai ba, nidai na gaji wallahi gida zan tafi gara naje inda ake sona ba zan zauna a inda ake zaman gaba dani ba" ta fada cikin karyewar murya tana shirin sakar masa kuka.

Tafiya yaci gaba dayi yana cewa
"Idan izinina kike tambaya banyarda ba idan kuma kinga zaki yi gaban kanki ne to ki tabbata idan kika tafi bazan biyo bayanki ba" ya kunna motarsa kafin ya qarasa ya bude get ya fita da motar ya dawo ya rufe har sannan tana tsaye tana hawaye.

Yana fita ta juya dakinta da gudu tana kuka, kaya ta shiga hadawa dan ita tafiya zatayi da gaske bazata zauna ba gara can a kirashi ya fadi abinda yake nufi da ita daya jingineta ita da babu a gidan matsayinsu daya.

Khalil kuwa yana fita gefen hanya ya samu ya faka motarsa ya dora kansa akan sitiyari, Allah ya sani yana son Umaimah son da shi kansa besan iyakarsa ko a yanzu daya nesanta kansa da ita shi kadai yasan irin azabar kewarta da yakeyi.
Dakyar yake iya bacci, ya tabbata ya fita shan wahalar wannan yanayin da suke ciki amma so yakeyi su dawo kan saiti suyi rayuwar aure kamar sauran ma'aurata cikin girmamawa da mutunta juna.

Baze dauki salon data zo dashi ba na zama kamar wasu haduwar bariki ya zaman bata shayin ta zageshi kota gaya masa duk maganar data zo mata amma yaga alamar sam bata da niyyar gyarawa sema qara batawa da take so tayi, ba kuma yaso ace har ta kaisu gaban magabatansu yanaso su koyi sasanta duk wani sabani daya gifta a tsakanin mu to yaya zeyi? Ya tabbatar yanzu tunda ta quduri niyyar tafiya koda yace be yarda ba sedau wani ikon Allahn amma mawuyaci ne ya koma gidan ya tarar da ita

Ji yakeyi kamar ya koma ya sauke nasa fushin ya lallabata amma yana tsoron abinda hakan ze haifar masa a gaba idan ta miqe akan sedai shi yabi ta ze sha wahala dan ba ita kadai ba hatta da yayan da zasu haifa a gaba se hakan ya shafi tarbiyyarsu, dole ya danne duk wani tasirin da take dashi a zuciyarsa ya kunna mota yaci gaba da tafiya amma ya qudurce idan ya dawo ya tarar da ita zero zaunarda ita ya nuna mata kuskurenta tunda ta kasa fahimta da kanta.

Umaimah kuwa kaya ta shiga hadawa da gaske tana kuka, kiran wayarta da akayi ya dakatar da ita ta daga ganin Anty Hafsa ce take kira ta shaida mata zata zo gidan tana hanya.
Jefa wayar tayi taci gaba da hada kaya gara ma tazo su tafi kawai ta huta da nemo Adaidaita. Tsaf ta cika akwatuna biyu da duk abinda tasan zata buqata ta kaisu palour ta ajiye, a gurguje ta watsa ruwa ta saka doguwar riga bata nemi abin kari bama taci a gida ta zauna a palour zaman jiran Anty Hafsa tana jin an buga Get kuwa ta fita da saurinta ta bude.

"Wadannan akwatunan fa Umaimah ko balaguro zakuyi tunda daman ke ba'a sanin tafiyarku balle dawowa" Anty Hafsan ta fada tana kallon akwatunan data jera, kamar tana jira kuwa ta rushe mata da kuka tana cewa

"Na gaji Anty gida zan tafi Khalil ya deba sona ya rigada ya samu abinda yake so ya hadani da kaya shine ze fara nuna mun halinsu na maza".

"Subhanallahi me ya faru? Dama kina da wata matsala ne da kikayi shiru tuntuni baki fada ba har ta kai ga kice zaki koma gida" Anty Hafsa ta fada cikin tashin hankalin irin kukan da taga Umaiman tanayi.

Dakyar ta tsagaita nan ta shiga labartawa Anty Hafsan abinda ya faru zuwansu Kaduna har zuwa yanda sukayi dashi yau da safen, ta rufe da cewa

"Daga na nuna masa nasan abinda yakeyi naganshi da karuwa shikenan ya dauki gaba dani ya fita sabgata, ina tunanin ma idan ya fita can yawon biye biyensa yake tafiya babu abinda ya shafeshi dani bare yasan damuwata".

"Ba shakka Umaimah duk inda ake neman yar bura uba mahaukaciya kin kai har kin wuce, aini wallahi be burgeni ba dabe dawo mana dake a kakkarye ba. Kamata yayi ace ya sauke miki kafada ya karya miki qafa daya sanda kika ce ya dakko karuwar su kwana tare. Banda ke bakida hankali baki san abinda yake miki ciwo ba ki kalli tsabar idon mijinki ki kirashi mazinaci koda ace da gaske ne ballantana tsabar hauka da baqin kishinki da kika dorawa kanki ne, anya kina tsoron gamuwarki da Allah Umaimah?

Toh bari kiji tun kinada sauran lokaci ko tuba kibi Allah ki kuma nemi yafiyar sa. Islamiyyar da kikayi bata amfane ki da komai ba tunda baki koyo ilimin sanin darajar miji da yanda ake zaman aure ba, idan kuma baki tuba kinbi Allah ba zaki tashi a tutar babu, ki qare rayuwa bakiji dadin zaman aure ba dan babu dan iskan da ze zauna dake kina zaginsa yanda kika ga dama idan be ringa cin ubanki ba to kuwa zakiyi rayuwar qunci da baqin ciki kamar yanda kikeyi yanzu sannan kije lahira walakiri yaci ubanki ki tafi wuta ba fata nake miki ba.

Allah ya taimakeki ya baki miji me sonki da yake ke ba yar arziqi bace ashe abin tsiyar da kike shuka masa kenan yana shanyewa ina ma ace banzo ba ki debi kayan nan kije gidan na tabbata dayau se anyi miki dakan hatsin matan qauye yanzun ma kuma daga nan gidan zani na zayyanewa Mama duk abinda ake ciki gara ta sani a san ta inda za'a taroki danna fuskanci baki da hankali ko kadan".

Tas ta silleta tayi fada tayi masifa kafin ta dora da nasiha da lallashida bata dabarun yanda zata riqe mijinta bata hanyar hauka ko rashin hankalin data daukarwa kanta ba.

Da kanta ta tayata suka gyara gidan tsaf dan shara tunda aka shiga wannan hali idan bata gaji da zaman tunani ba bi ba batayi, cikin kayayyakin gyaranta ta harhada mata wasu tasha tana cewa
"Dan uban likitan da tace ki kwashi wata biyun idan ta kashe miki aure mijinta zata baki ki aura ko ke kuma ga sauna da yace ki koma dakinki kika kwashi kaya ziqau ziqau kika tafi Allah ya ganar dake dai Umaimah.

Seda tayi mata lafiyayyen girki bayan data sakata tayi wanka ta sheqa kwalliya suka shirya komai tsaf sannan tace mata

"Ki dauki waya ki kirashi yanzu kisan yanda zakiyi duk abinda yakeyi ya baro ya taho gidan nan, idan yazo saura ki sauka daga layin dana doraki, ki sauke kanki ki bashi haquri ki nuna masa kin gane kuskurenki ba zaki sake maimaitawa ba ba kuma wai ya zama iya fatar baki ba Aa har zuciyarki nake so ki yarda kinyi kuskure kuma kodan gaba ki kiyaye, ki sani duk abinda kika aikata masa na rashin kirki kanki kikayiwa saboda shi Allah babu ruwansa ze kamaki da laifin qin yiwa miji biyayya. Gara ace shi ya cuceki se Allah ya saka miki da ace ke ce kika cuce shi kikai kanki wuta a banza, kuma idan na koma zanyo miki aiken ingantatt??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????un magunguna dana samo a gurin *SUMAYYA'S HERBAL APHRODISIACS AND COLLECTION*, idan kika gwada magungunanta babu ke babu sake siyan duk wasu jigari jigarin magungunan mata da baki san dame aka hada su ba.

Jikin Umaimah yayi laqwas, Anty Hafsa bata tafi ba seda ta kirashi a wayar tana numfashi kamar wadda ake yankawa wai cikinta, Khalil dake Tsakiyar aiki a wani Site babu shiri ya kamo hanya dan daman gaba dayan ranar tana maqale a ransa yana ta tunanin ta tafin ko tana nan.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* =?L?
Page 23


Cikin yan mintuna ya isa gidan a ransa yana ta taraddadin abinda zeje ya tarar, meya sameta? Shine tambayar da yake tayiwa kansa har ya qarasa qofar gidan ya kashe motar ya barta a waje tunda sake fita zasuyi ya kaita Asibiti.

Turus yayi yana qarewa yar madaidaiciyar harabar gidan kallo, ko ina yayi qal hatta da interlocks din dake shimfid sunsha wanki da kallo daya zaka musu ka hango tas din da sukayi. Qara bude hanci yayi yana shaqar daddadan turaren wuta dana Airfreshner ga kuma sanyayyar iskar yamma se suka hadu suka bada wata Atmosphere me sanyi da sanyaya zuciya.

Be qarasa suman tsaye ba seda ya shiga palour, tana zaune akan kujerar dake fuskantar qofar shigowa. Riga da skirt ne na wani Yellow Lace irin yellow nan me kamar butter da yayi bala'in karbar fatarta da bata da haske sosai ta kashe daurin gaban goshi irin yanda yake sonsa wani kallo ta watsa masa tana raurau da ido kamar me shirin yin kuka be san sanda ya dage zuciyarsa da hannu biyu ba ya lumshe ido saboda yanda kallon nata ya tasirance shi.

Cikin wata irin tafiya taso babu inda baya motsawa a jikinta tana zuwa ta fada jikin

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login