Showing 237001 words to 240000 words out of 429394 words

Chapter 80 - Halin Kishi Book 1 Hausa Novel Complete

17 Jan 2025

981

son zuwq Abuja sedai su dawo suyi ta bata labari amma koda wasa bata taba zuwa ba. Bata jin magana Baba Badaru kuma baya daukar nonsense dan ko gidansu yazo daga gaisuwa gudu takeyi karma ta tsaya tayi shirme a gabansa yaci ubanta shiyasa ko yaransa babu wata shaquwa tsakaninta dasu bama zata iya cewa ga Adadinsu ba dan ba shiga abinda ya shafesu take ba tana gudun masifar Babansu shine yanzu zece ta bishi salon ya kasheta acan sedai ya aikowa yan uwanta jana'iza tab.

"Yanzu dai ayi haquri gaba daya dan laifi Umaimah bata kyauta ba amma shima Khalil yayi laifi. Me yasa ze saka yaidara a cikin lamarin ai ba ga Umaimah ba ko a gurin ubangiji beyi daidai ba hakan ma da yayi yasa Allan ya nuna masa wayonsa baze bashi kwangilar ba sannan dan ta zama sila hakan bashi ze bashi damar ya taba lafiyarta ba, ko dan gaba karka sake, idan tayi maka abu da bazaka iya jurewa ba ka kawota gaban magabatanta su tsawatar mata amma koda wasa karka sake cewa zaka taba lafiyar jikinta" Alhaji Abubakar kawun Khalil ya fada kafin ya dora da cewa
"Yanzu dai magana ta wuce Alhaji muna sakw baku haquri komai ya wuce ke ki bawa mijinki haquri sannan ki shiga ki hado kayanki mu tafi dare yanayi"

"Ai Yaya Badaru ya gama magana Alhaji, kuyi haquri kuje kawai, idan aka kwana biyu zuciyoyi suka qarayin sanyi seta dawo amma yanzu idan akayi haka tamkar an shiga haqqin yaron ne, kowa yasan abinda akayi masa babu dadi kuma yana da buqatar a bashi lokaci ya samu nutsuwa" Baba Liman ya fada nan su Alhaji Garban suka dage akan lallai fa se an basu bikon Umaimah sun tafi da ita.

"Kayi haquri Khalil dan girman Allah wallahi sharrin zuciya ne amma nayi alqawari bazan sake ba" Umaimah dataga Lamari yana qara rikicewa ta fada cikin matsanancin kuka, fata take yace ya yarda ta bisun dan abinda Baba Liman ya fada kenan se anji ta bakinsa amma yayi mirsisi ya zubawa qasa ido yaqi ce musu komai,

"Babu shakka, Khalil ma kike kiransa kai tsaye saboda kin rainashi ko" Baba Munzali ya katseta se tayi saurin cewa
"Abban Mu'ayyad na tuba bazan sake ba, na yarda daga yanzu in na kuma duk hukuncin daka ga dama ka yanke akaina amma yanzu ka yafe mun dan Allah". Cikin tashin hankali take dan idan yace baze tafi da ita ba bata san inda zata tsoma ranta ba. Zancen tabi Baba Badaru ma baze yuwu ba dan ko duniya zata taru bazata gidansa ba wallahi kuma idan ta zauna a cikin gidan nasu ma tamkar ta fito daga rana ne ta fada wuta dan Shirun da Abba yayi yana kallonta kawia ta tabbata idan be hada mata jikinta da duka ba to qila wuqa ze saka ya yankata balle labari ya isa kunnen Mama kai ita bata shirya fuk wani tashin hankali ba gara ta bishi suje can zata jure duk abinda zeyi mata har ya haqura ya sakko daga fushin.

"Ya isa haka, ina ganin magana tana hannun Khalil yanzu, idan ya yarda ya dauketa su tafi idam kuwa ba haka ba babu me tilasta masa akan ta koma. Zata cigaba da zama anan har zuwa sanda shi dakansa ya gamsu ya nemi ta koma din" Abbada tunda aka zauna bece komai ba yayi maganar ganin takaddamar taqi qarewa. Khalil ya daga kansa ya kalli Abban wanda shima shidin yake kallo. Iyayen Umaimah na daga abinda yasa yake daga mata qafa a lokuta da yawa dan mutanen kirki ne, a yanzun ma ta sake cin darajarsa dukda hakan ba yana nufin ya yafe mata bane Aa ze haqura ta koma ne saboda ya ragewa Abban radadin da abinda take aikatawar yake haifar masa wanda kwayar idonsa take gaza boyewa. Ya tabbatar idan aka auna jininsa a yanzu ya hau.

Rintse idonsa yayi cikin wata murya yace
"Na yarda ta koma amma..."
"Karma ka bata bakinka Yi shiru Halilu kaidai Allah yayi maka albarka ya qara maka hasken zuciyar musulunci, yanda ka iya shanye wannan baqin ciki Allah ya saka maka a mizani dan abinda kadai zan iya cewa kenan, Amma Alhaji sefa kunyi haquri dan ba zata biku yanzu ba saboda dole zamu sake yi mata fada a matsayin mu na iyayenta, idan Allah ya kaimu gobe da kaina zan rakota har gidan mun gode Allah qara Arziqi, ke tashi muje" Baba Abdullah daya miqe yana nade babbar riga ya fada.

Umaimah tayi wuri wuri da ido take murna ta koma mata ciki, jin Khalil ya yarda ta koma ga kuma wani sabon zance a gun baba Audun seta bare baki zata kuma rusa wani kukan ya daka mata tsawa yana cewa
"Na rantse da Allah ko ki tashi ko yanzu nayi ball dake a gurin nan, qarqari akai mi gidan yari na shekara na fito dan ba dauruwa zanyi ba" yanda yayi maganar kuma taga a gun babu wanda ya ce komai ya saka ta miqe jiki na rawa tana waiwayen Khalil da taqi kallon sashin da take.

Gabaya tasata, tun daga qofar falon yake antaya mata maruka a fuska da qeya har suka isa falon Mama, Mama da Anty na zaune kowa ta rafka tagumi dan Umaiman ta fado tana ihu.

Cikin rashin Jin dadi kawunan Khalil sukayi sallama da kowa suka tafi, Alhaji Abubakar ya ringa sababi wai ya wulaqanta su ya nuna basu isa ba, sun bashi umarni yaqiyi shidai Khalil ransa fes ya biya ya sauke kowanne a gidansa kafinya wuce gida yana zuwa ya tarar da Hajiya na jiransa, a taqaice yace mata kawai gobe Umaiman zata dawo, taja doguwar Hamdala ya tsaya yana kallonta kawai kafinya girgiza kai ya yi mata seda safe ya fita. Kwana yayi yana ayyana ta yanda ze iya manta abinda ya faru yaci gabada rayuwa da Umaiman.

Har ga Allah ba rasa kwangilarda yayi ne yafi damunsa ba, tunanin irin rainin da Umaiman tayi masa da harbata shayin tayi masa duk abinda taga dama. Idan har zata iya aikata haka bayan tasan cewa ze taba rayuwarsa ya taba aikinsa gababe san me zatayiba, dole ya dauki mataki kafin ranar nadama mara amfanita riskeshi. Tunanin hukuncin da zeyi mata ya huce kawai yakeyi amma har bacci ya kwashe shi be samu ba.

UMAIMAH
Seda Baba Abdullahi ya kumbura mata fuska da marukan daya ringa zabga mata tamkar Allah ya aiko shi kafin ya kalli su Mama da sukayi cirko cirko suna kallonsu aka rasa wadda zata kai mata taimako yace
"Ki gayawa wannan mahaukaciyar yar taki ta yanda kika hadu da ubanta".

Kallon rashin fahimta Mama tabi shi dashi, Baba Abdullahi da seka rantse shine ma Khalil din saboda yanda ya ara ya yafa a masifance yace
"Eh Malika, ki sanar mata da yanda akai kika auri Ubanta, koda yake bazata fahimta ba idan ke kika gaya mata, bari ni nayi mata gwari gwari ta yanda zefi shiga kwakwalwarta" ya juya kan Umaimah data dafe kunnuwanta da takeji kamar sun toshe yace

"To bari kiji, Hajiya Lawisa ta qaraye ai kinsanta Uwar Mijin Naziyya yayan maza muke da ita kuma itace Asali wadda suke soyayya da ubanki Sabo, sanda ya baro qaraye ya shigo birni Alhaji Madaki Mahaifin Malika gatanan data haifeki shine ya zamar masa ubangida, ya koya masa neman kudi har ya dorashi akan harkokin dukiyarsa da sharadin ze auri yarsa, bazawara ce ma a sannan baya sonta amma ya yarda kuma haka akayin ya koma gida ya fadawa iyayenmu ya fasa auran Lawisa duk da dadewar da sukayi suna soyayya haka kowa ya dauki qaddara aka barshi ya auri yar ubangidan nasa itama Lawisan kuma a cikin Abokanansa da sukaje daurin aure daga Birni Allah ya fitar mata da Miji tayi auran.

Sanadin auran uwarki duk muka baro qauye muka dawo nan masu boko suka kama masu kasuwanci suka kama da ba'a aure dan wata biyan buqata da yanzu ba a haifeki ba shegiya me kalar ibilisai kinzo kin gallabi kowa se kece zaki hana saboda baqin ciki da kyashi ya cika miki zuciya to ai kin kyauta, kuma yanda kika rusa kwangilar nan kikayi masa baqin cikin samun wasu a gaba in sha Allahu seya janye miki tallafi" Baba Abdullahi ya fada yana kai mata wani marin ta goce kafin ya gallawa Anty da Mama da suka zama hoto harara yaja tsaki ya fice daga gidan.

Muryoyin ragowar sukaji da suka fito suna musanyar sallama, suna tsaye kamar mutum mutumi Abba daya raka yan uwansa ya dawo jiki a sabule ya leqa falon Maman.
"Ki sameni a daki ina son magana dake" ya fada mata kafin ya juya Anty taja numfashi ta fesar kafin tace
"Bari naje na kwanta Allah ya tashe mu lafiya" ta fice daga dakin tana tariyo maganganun Baba Abdullahi da bata tabajinsu ba. Iya saninta Abban ya sanar mata da auran soyaya sukayi da Malika daman dai tasan yar ubangidansa yanzu kuma taji wata cakwakiya ashe shine dalilin da ya saka Sam Hajiya Lawisan basa wani shiri da Mama dukda bata nunawa Naziyya komai amma fa idan suka hadu ko a taro ne tafi yi da Anty akan Maman da suke matsayin surukai.

Mama ko tamkar wadda aka watsawa ruwan sanyi haka taja qafafunta da sukayi sanyi tabi Abban ba tareda ta bi takan Umaimah dake nan tsugunne tana kuka ba. Wannan cin mutunchi na Abdullahi har ina? A gaban kishiya yayi mata tijara, wai ma me Umaiman tayi daya juye kanta ake mata wannan tonon sililin?

Sanda Abba ke labarta mata abinda Umaiman ta sake aikatawa kuwa kasa motsi tayi a gurin banda binsa da kallo ba abinda takeyi dan ko tunani ta kasayi a kwakwalwarta.
"Wallahi Malika saboda kunya kasa cewa komai nayi se su Badaru ne sukayita fadace fadacensu. Yanzu ace Umaimah bazata bar rayukan mu su huta ba kullum ta Allah da sabuwar rigimar da zata janyo mana?
Nidai na yanke shawara zan kira yaron nan daga baya, ya fadi gaskiya karya ji kunyar mu idan har yana ganin da cutarwa a cikin zamansu ya sawwaqe mata kawai kowa ya huta tunda dai ita bata san inda yake mata ciwo a rayuwarta ba, gara ta dawo ta zauna kawai kafin wata rana ta dakko abinda zata saka a hada harda mu a kulle".

Hannu Mama ta saka ta share hawayen dake mata tsere akan fuska amma suka qi tsayawa, cikin sheshsheqa tace
"Alhaji na gaji da Halin Umaimah na gaji ban san wace irin yarinya bace ba, Allah ya gani iyakar iyawa babu ta inda na banbantata da yan uwanta a gurin tarbiyya, raino daya nayi musu harma nafi lura da saka ido akan al'amuranta. A kullum na???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? daga hannu kafin na roqawa kaina komai sena roqawa Umaimah amma na sani Allah ba mantawa yayi dani ba yana sane kuma in sha Allahu jarabawar da yayi mana akanta zata zamo mana kaffara" ta qarasa tana sakin wani kukan me nuna zallar zafin da zuciyarta takeyi. Cigaba tayi da magana tana cewa

"Yanzu Abdullahi seda ya qare min tanadi tas akanta kafin ya fita, a gaban Saratu yake fadar cusa maka ni akayi saboda na rasa ma'auri baka sona ka aureni a bazawara ya gama fadar maganganunsa ya fita duk saboda Umaimah, shikenan saboda na haifeta bazan samu nutsuwar zuciya ba? Kullum tazo gidan nan cikin fargaba nake se naga ta tafi salin alin sannan hankalina yake kwancita har se yaushe? Se yaushe zamu huta da matsalolin Umaimah?".


Kuka take sosai Abba ko ya rafka tagumi ya kasa rarrashinta, seda tayi me isarta kafin ta miqe tayi masa saida safe, kai kawai ya iya daga mata danshi kansa zuciyarsa a dagule take da zeyi kukan ma daya ji dadi.

Koda ta koma dakin inda ta bar Umaimah nan ta tarar da ita. Kallo daya tayi mata ta wuce cikin dakinta kai tsaye Alwala ta daura ta shinfida Sallaya ta fara jera nafiloli. Kwana tayi tana sallah ko kadan bacci be ziyarci idonta ba, toh ta ina zatayi bacci bayan Allah ya hada ta da yarinya irin Umaimah?

Da Asuba Umaimah da tayi kwanan zaune ita ba sallah ba ba salati ba tana ta faman sharar hawayen da bazasu magance mata komai ba, dakyar ta iya miqewa saboda yanda qafafunta suka haye saboda zaman da tayi ta ringa dafa bango harta shiga dakin Maman. Alwala ta dauro, Mama data idar da Raka'atanul fajr tabita da kallo harta fito daga bandaki ta nemi gefe kusada Maman ta zauna dan ba zata iya sallar a tsaye ba. Seda suka idar da Asuba kafin ta kalli Maman cikin muryarta da bata fita saboda kukan data sha ta gaisheta.

Da "Lafiya" ta amsata batareda ta kalleta ba taci gaba da lazumin da takeyi, Umaimah ta sunkuyar da kai hawaye suka kawo a idonta cikin muryar kuka tace
"Dan Allah Mama kiyi haquri wallahi...."
"Dan Allah karki dameni bakiga abinda nakeyi bane? Tunda ke daman sallar kadai kikeyi bakya addu'a se ki tashi ki bani guri nikam inada buqatu da yawa gurin Allah karki dameni" Maman ta katseta ba tareda ta bari ta fadi abinda take so tace ba. Se kuwa ta saki kukan da take qoqarin hana fitowarsa, a fusace Maman ta juya tace mata

"Tashi ki bar nan kafin na saba miki"
"Dan Allah Mama ki tsaya kiji, wallahi Allah bayin kaina bane, Safina ca ta bani shawara kuma tace mun ta tabayin hakan itama shi yasa nayi amma ban zata abin zeyi zafi da yawa haka ba" Umaimah ta fada cikin kuka tana matsawa gaban Maman.

Carbin da take ja ta kai mata duka dashi ta goce dukda haka ta sameta a hannayenta data saka ta rufe fuska dukan ya shigeta kuwa sosai
"Badai ke kince bakya jin magana ba? Bazaki bar zukatan mutane su huta daga tashin hankalinki ba ko? Ai shikenan kici gaba da daukar hudubar mutane suna ingizaki kina rashin hankali, Qawaye ko? gaki gasu Umaimah wata rana se sun kaiki kurkuku sun ja miki daurin rai da rai sannan zaki dawo shikin hayyacin ki shashasha kawai" cikeda takaici Maman tayi maganar tana miqewa dan barin mata dakin tunda ita taqi fita. Palour ta koma, tana jiyo Umaiman na kuka daga ciki.
[8/18, 9:52 PM] KYAUTA: *TASTED & TRUSTED*
*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATUN SAIWOWIN MUTANAN CHADI DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZAR AMARE, MASU JEGO DA WADDA TAKE SON GYARA KANTA*.
*AN GWADA ANGA INGANCINSA SHIYASA NA KE TALLATA MUKU DA K'ARFIN GUIWATA*.
*ABIN BIRGE WA DA WANNAN SAIWOWIN ZAKI YI AMFANI DA SU SAMA DA SAU DAYA.*
*AKWAI FULL PACKAGE, AKWAI RABI, TA YADDA KOWA ZAI IYA SIYA*.
*SANNAN BABU BAURI NA TASHIN HANKALI.*
*DA KANKI ZAKI DAFA ABAR KI, KOMAI ANA SAKA WA A CIKI*.
*SHIN KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR, KO KUWA KE CE KIKE SON GYARA KANKI?*.
*KAYANA NATURAL NE DOMIN SAIWOWI NE DA AKE HAKOSU A DAJIKAN CHADI. BAYAN SAUKAR DA GAMSUWA HAR YAQI SUKE YI DA DRYNESS DA KUMA INFECTIONS.*
*AKWAI NA TSUGGUNO DA YAKE HA'DE MACE TA MATSE.*
*AKWAI HADADDUN DAKA NA SHA DA MADARA KO NONO WANDA BABU ALGUS*.
*SANNAN AKWIA GADALIN MATA NA ASALI, WANDA SHA YANZU NE MAGANIN YANZU DA IKON ALLAH*
*AKWAI MAGANIN SANYI SADIDAN*.
*DUKKANSU TESTED & TRUSTED NE*.
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU*
*08032773332*
*DOMIN KARIN BAYANI, SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*.
*NATION WIDE DELIVERY* .

*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* =?L?
Page 56


Abba yayi sallama ya shiga falon ta amsa ya nemi guri ya zauna kusada ita. Bayan sun gaisa yake ce mata
"Malika kinga idonki kuwa a dare daya har kin zabge dan Allah ki cire damuwa daga zuciyarki, ita rayuwar mumini bata cika dole se ana jarabtarsa dan gwada imaninsa dan haka mu mayar da komai ga Allah kuma mu ci gaba da neman taimakonsa shi kadaine ze iya mana".

Hawaye ne suka fara sakko mata cikin tsananin tausayinta ya kama hannyenta biyu yana cewa
"Ki dena kuka, wadannan hawayen suna daga abinda yake qara dagula rayuwarta kiyi shiru kici gaba dayi mata addu'ar da kikeyi kullum in sha Allahu wata rana se labari kiyi haquri". Haka ya ringa lallashinta yana gaya mata kalamai masu dade harta samu ta tsayar da hawayen wanda sosai nauyin da qirjinta yayi mata ya ragu, a kullum Addu'arta Ubangiji yaci gaba da bata juriya akan al'amuran Umaimah karta kaita bango tayi mata baki.

Seda Abban yaga ta samu nutsuwa kafin ya miqe yace zeje ya duba Saratu, Mama ta rakashi da ido, shikansa tasan qarfin hali kawai yakeyi. Yana fita ta mayar dakai taci gaba da jan carbinta.

A tsaye ya tarar da Anty Saratu tana cire Hijabi alamar lokacin ta idar da sallah. Ya nemi gefen gadonta ya zauna, seda ta ninke hijabin kafin itama ta zauna tana gaishe shi.
"Jiya har nayi bacci shiru baki shigo ba" ya fada kasancewar ita ce da girki, seta yi murmushi kadan tace
"Ina nan jiran baqinka su tafi bansani ba bacci ya kwashe ni".

Kallonta yayi shima yayi murmushin, Saratu kenan bata san Mama ta gaya masa a gabanta Abdullahi yayi mata tijara ba. Yasan zancen ne bata so a tayar dashi shiyasa tayi masa alaye da cewar bacci tayi se ya miqe yana cewa
"Idan da akwai dumame ki kawo mun yanzu zan sha magani, jiya ban samu naci abinci da daddaren ba" ya juya ya fice daga dakin. Kallon tausayi ta rakashi dashi, tun jiya Salman ya labarta mata abinda ya faru ta dade tana ta''jibin taqadaranci irin na Umaimah tana kuma tausayawa Mama dan itace babbar abar tausayi ma sama da Abban. Dan ma shidin ya kasance me shiga lamuran iyalansa shinr sauqin da take samu, da ace tayi katari da irin iyaye Mazan nan da sanda yaro yayi abin kirki yake nasu, duk wata rigima ko damuwa ta yaro uwarsa ta shafa qila da yanzu qasa ta dade da rufe idon Maman dan ba zata iya da baqin cikin Umaimah ita kadai ba.

A iya zamansu sama da shekaru Ashirin idan ka cire sabani na yau da kullum da dole a same shi tsakanin mutane idan aka zauna bazata ce yau ga wani mugun abu da Maman ta tabayi mata a matsayinta na kishiyarta ko wani ba a zahiri, haka har badininta zata iya

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login