Showing 336001 words to 339000 words out of 512766 words

Chapter 113 - Asanadin Makwabtaka Book 3 Hausa Novel Complete

Unknown   

27 Dec 2024

1630

matsayin ya taimaka man" d'an murmushi Aunty tay tace "in ma don hakan ne ai ba laifi bane sau nawa dama ake aure ba soyayya duk yawancin iyayenmu ba haka sukai auren ba kuma suka zauna lafiya, yanzu aure nawa ne akai a turbar soyayyar yazo ya lalace mudai fatan mu ai ya ruk'e mana ke da kyau ne kiji dad'in Auren, wani Maganar soyayya in kunyi auren kun yi in ma bai iya ba sai ki koya mashi abun ai duk mai sauki ne balle ma wllh irin wad'annan mutanen sun mugun iya love ki bari ayi Auren zaki ban labari dama yanzu ai bazai sake maki ba tunda yana ji da shegiyar izzar tsiya, ke ni ki bari indai damuwar ki ya furta yana son ki ne nayi maki Alkawarin sai furta wannan Kalmar ya zame mashi tamkar cin Abincin shi, yadda zai ci Abinci safe da rana da dare to ina mai tabbatar maki haka zai rink'a fad'in I love you Fauziyya",

duk da yanayin da take ciki saida ta d'an yi dariya Aunty ta k'ara cewa "Allah kuwa, ke baki ga yadda mijin Zarah ba ya shigo hannu sai faman rawar k'afa yake akanta ko ba'a fad'a ba daka gani kasan ta kama shi gamm to shima hakan zamu kama shi wuyarta dai ayi Auren hakan ba wani abun wahala bane wllh" d'an ta6e baki Fauzy tay tana d'an murmushi,

"Yanzu ya kika ce Your Excellency, a kira Zarah d'in ko mu fad'i mata abubuwan da muke so mu sani game dashi d'in?" wani kallo Fauzy tay mata tana yar dariya kafin a hankali ta d'aga mata kai alamar eh, da sauri Aunty ta kai hannu ta 6akar mata shoulder tace "su Excellency ana so ana kaiwa market" dariya Fauzy ta saka tana fad'in Allah ita ba wani son shi da take.

Fatuu zaune a parlor tana kallo tana sanye da doguwar riga Boubou ta lace cikin kayan data ba Kb ya d'inka mata daga baya akai mata d'inkunan da Hajiya tace , bata dad'e da fitowa daga Kitchen ba tayi ma Haisam Abinci da yake tunda yazo ita ke mashi Abinci har ce mata yay ta bari a rink'a yi acan part d'in Hajiya ita ta huta amman tak'i, wayarta dake a gefenta ce ta fara ringing ta kai hannu ta d'aukko, ganin mai kiran nata yasa tay d'an murmushi ta kai hannu tay picking,

"Aunty Mareeya ina wuni, barka da juma'a" ta fad'a bayan data yi sallama, amsa mata tayi ta tambayi ya suke harda unborn tana yar dariya tace mata duk lafiya lou suke ga unborn d'in ma yaji suna waya yace/tace a gaishe ta, dariya Maganar ta bata tace to tana amsawa ai in Allah ya yarda biyun ne duka ita dai Fatuu murmushi kawai tayi,

"Yauwa Zarah nace don Allah ko mijin ki na nan?" Fatun tace "a'a Aunty yau da safe ya tafi Kano yin wani aiki amman dai a yau zai dawo yace man in sha Allahu da Magrib jirgin su zai sauka" jinjina kai tay tace to Allah ya dawo dashi lafiya bayan ta amsa tace "Amman Aunty lafiya dai ko?"

"lafiya lou yar gidana sai ma Alkhairi in sha Allahu...." nan ta kwashe komai game da zuwa neman Auren Fauzy da za'ai da kuma yadda sukai da Fauzyn, tsananin mamaki ne ya bayyana akan fuskar Fatun gaba d'aya ta washe baki tana dariyar farinciki tace "Amman Aunty wllh naji dad'in wannan labarin wayyo Allah na, muna ta jiran ya furta yana son ta ko sun fara soyayya suyi aure ashe mai gaba d'aya zai yi.." Aunty ta amshe "Wllh haihuwa da hanji ba" dariya Fatuu tasaka nan ta fad'i mata abubuwan da take so ta tambayar mata Haisam a d'okance tace to in sha Allahu yana dawowa zasu yi Maganar Allah dai yasa suji Alkhairi Aunty tace "Amin ya Rabbi yar gidana shine abun da zamu yi fata kam" bayan sun gama wayar ta tambayi ina amarya Fauzy,
yar dariya Aunty tay tace "ga abu nan tayi wuri wuri Sameer yayi mata bazata" Fatun nata dariya tace a bata, bayan ta amshi wayar tsokanarta Fatuu ta shiga yi ita dai sai uhhm take daga baya ta hau yin Addu'ar Allah ya tabbatar masu da Alkhairi.

Bayan Magrib Haisam ya dawo bai dad'e da shigowa ba aka fara kiran sallar isha ya tafi Masallaci, bayan ya dawo toilet ya nufa yayo wanka ya zura jallabiya sannan ya fito don yaci Abinci da tuni Fatuu ta jera mashi akan c-table don in shi kad'ai zai ci yafi son a d'aura mashi anan, Serving nashi ta shiga yi saida ta tabbatar yaci ya k'oshi, tana k'ok'arin kwashe kayan Abincin ta kai Kitchen ya mik'e yace ta bari ya kai tace mashi tana son had'o masu Fruit salad ne, kallonta yay yana d'an murmushi yace zai had'o masu ta zauna huta, hura mashi kiss tay ta kashe mashi ido yay yar dariya, nufar Kitchen yay bayan ya d'auki tray d'in kayan ta d'an d'aga murya tana fad'in "Hubbyna I love you" kai ya jinjina mata ta k'ara fad'in "bazan iya rayuwa babu kai ba" tana fad'in hakan taji yace shima haka sosae yadda yay Maganar ya bata dariya, yana gab da shigewa cikin Kitchen d'in ta k'ara d'aga murya tace yabi a hankali kar ya yanke hannu Baby zai yi kuka in ya yanke, jinjina kai yay saida ya d'an juyo suka had'a ido ya sakar mata k'ayataccen murmushi tare da d'an girgiza kai ganin abunda take mashi da baki ya juya ya shige, after some minutes sai gashi ya dawo hannun shi ruk'e da acrylic bowl ana hangen fruit d'in, dayan hannun shi ruk'e da bottle water ya nufo ta suna ta sakar ma juna murmushi, a gefen ta ya zauna ya mik'a mata tasa hannu biyu ta amsa ta furta "thank you so much Daddyn Baby" hannu ta kai ta d'auki spoon d'in ciki ta fara sha tana yi tana bashi shima a baki can taga ya kawo hannu ya d'ago da k'afafunta ya d'auro su kan cinyoyin shi ya shiga matsa mata su sai murmushi take tana cigaba da sha shima tana bashi, yana ta matsa mata k'afafun idanun shi akan Tv yana kuma amsar fruit d'in in ta kawo can ya juyo yace mata tasha kada ya shanye ma Baby abu tay dariya, bayan ta shanye akan c-table ta d'aura bowl d'in ta d'aukko bottle water d'in, bayan tasha ta rufe ta maida kan c-table d'in,

"Hubby" yaji ta kira shi ya d'aga gira kafin ya juya ya kalleta, ce mashi tay dama so take ta tambaye shi yasan da zancen zuwa nema ma Sameer Auren k'awarta Fauzy, yanayin fuskar shi ne ya canza da alamun rashin fahimta ya tambayi wane Sameer tace mashi cousin brother d'in shi, shiru ya d'an yi idon shi a kanta yace bai fahimce ta ba, bayanin Maganar zuwa nema mashi auren Fauzy ta yi, sosae mamaki ya bayyana akan fuskar tashi yace mata shi bai san da Maganar ba ai tace mashi aikuwa d'azun Aunty Mareeya ta kirata take mata Maganar, jinjina kai yay yama kasa cewa komai sosae kan shi ya d'aure don abu ne da bai zaton ji ba,

"Ka yi mamaki ko?" Fatuu ta tambaya a hankali ya jinjina mata kai, tambayarta yay yadda akai suka san juna nan ta kwashe komai ta fad'a mashi harda wayar da ya siya ma Fauzyn tace ita ta mantane shiyasa bata fad'i mashi ba wllh, d'an tsoki yay ya furta "Sameer...." Shiru yayi Fuskar shi da d'an murmushi, sosae yaji mamakin yana son Auren Fauzy duk da yasan hakan ba wani abu bane in Allah ya k'addaro itace matar shi saidai shi yasan waye Sameer fiye da kowa bai ta6a tunanin zai iya Auren yarinya kamar Fauzyn ba sanin irin matan da yake tarayya da su,

"Wai suna son sanin game da shi ne don ita ko cewa yana sonta bai ta6a yi ba fa kawai dai suna d'an gaisawa yana yi mata Alkhairi kuma sai kwatsam suka ji zancen neman auren ta",
Yana murmushi yace "Yana sonta ne shiyasa yake mata hakan kawai bazai fito bane ya fad'i mata" gyad'a kai Fatun tay idon shi akanta yace mi suke son sani a tare da shi ne, ce mashi tayi kamar ya halin shi yake,

"Ok, what I know is that baya da wani hali mara kyau da za'a k'i auren shi Saboda shi" ya k'arasa yana d'an girgiza kai,

"amman ita wai tana zargin wasu abubuwa a tare da shi" tambayarta yay kamar mi take zargin, shiru Fatuu tay hakanan sai taji nauyin fad'in Maganar ya fahimci hakan ya d'age mata gira yace ta fad'i mashi duk abunda ya sani bazai 6oye masu ba,

"D....dama wai cewa tayi taga ya sha giya" da k'yar ta k'arasa ganin yadda ya kafeta da ido, yana jin abunda ta fad'a ya d'an waro ido mamaki ya bayyana akan fuskar shi ganin haka yasa ta zaro ido,

"A yaushe ne taga Sameer yasha wannan d'in?" da mamaki ya tambaya, wani abu Fatuu ta had'iya tana faman kikkafta ido tace "ai ba wai ta tabbatar bane fa, dama da ya je da ita gidan da na fad'i maka lokacin da sukai karon nan wayar shi ta fashe...to a nan ne taga wai ya bud'e Fridge ya fiddo kwalba irin ta giyar kuma bayan ya zuba a cup ma taga kalar kamar ita" ta k'arasa tana d'age baki, maida bayan shi yay ya jingina da kujerar fuskar shi a d'an kwa6e ita kuwa sai faman zare ido take can ya k'ank'ance ido yace "Kin koya mata taga mutane na shan lemu tace giya ko" hannu ta kai da sauri ta rufe baki ta hau girgiza kai yace mata eh mana, cire hannun tayi cikin yar rawar murya tace wllh ita fa ba ruwanta itace ta fad'i mata haka kuma ita ai bata ma ga abun ba ko, d'an ta6e baki yay yana murmushi can yay sigh yace "to bai shan giya inada tabbas akan hakan don shi yama tsane ta abunda taga yasha favourite drink d'in shi ne" da sauri ta jinjina kai yay mata wani kallo mai kaman harara tasa dariya, ce mata yay sai mi suke son sani,

"To zan fad'i maka amman fa kar kace ni nace abunda aka fad'i ana son sani ne" murmushi yay ya d'aga mata kai, "tace wai taga yaje wani wuri da suka baro gidan kuma wurin wai kaman Club ne" d'an lumshe ido yay ya d'aga mata kai "Yeah, yana zuwa Club" shiru tayi tana kallonshi don ba iya abunda suke son su ji ba kenan,

"da wani abu ne game da hakan" ya tambaya had'i da d'age mata gira, in ina ta fara "w..wai ita a tunanin ai ba abun Arziki ake yi a can ba, t..to shine wai...take ganin kaman yana...." dakatawa tay gaba d'aya ta waro ido yana dai ta kallonta taji yace uhum alamar taci gaba, "to na dai fad'i maka ai abunda ake son sani ne ba ana nufin yana yi ba" yana murmushi yace ai ta fad'i wannan ko yana jin ta, ce mashi tay wai ko yana neman Mata ne, ganin yayi shiru yasa tace mashi ya gane abunda take nufi har saida Maganar ta d'an bashi dariya,

"baya wannan, I'm absolutely sure about that, saidai he's touching women" waro ido Fatuu tay ya d'an jinjina mata kai yaci gaba "iya ta6a mata yake am very sure akan hakan don tun muna School abroad ina mashi fad'a akan hakan yace man ya bari amman kuma daga baya sai ya cigaba, kinsan hakan yanzu wasu basu d'auke shi komai ba suna d'auka wayewa ne duk da wanda yake Muslim yasan hakan is forbidden kuma babban laifi ne kamar dai yadda akwae abubuwa da yawa da ba kyau kuma ake yi" ajiyar zuciya Fatuu ta sauke da yanayin damuwa tace "to amman kasani ko yanzu ba iya hakan yake ba yana....." Shiru tayi ta kasa idasa Maganar, da murmushi akan Fuskar shi yace mata yana da tabbacin bai yin sex don yana da ilimin Addini sosae da bazai bari yayi hakan ba shima ta6a matan da yake kawai biye ma zuciya ne kuma harda Matan da ke yawan bibiyar shi sun k'ara taimakawa wurin sashi hakan, jinjina kai Fatuu tay ya kai hannu ya shafo gaban kan shi, yar ajiyar zuciya Fatuu ta sauke,

"Yanzu kana ganin hakan ba matsala bane?" Shiru ya d'an yi idon shi akan Tv kafin ya juyo kanta "a wurina hakan bazai zama problem da zai sa ak'i auren shi ba, Sameer mutumin kirki ne sai kayi mu'amala shi zakai understanding hakan duk da nasan yana da wuyar a saba da shi amman yana da Quality da mace za tayi Alfaharin samun shi as a husband" wani k'ayataccen murmushi Fatuu ta saki tare da kashe mashi ido d'aya ta furta "Kamar kai kenan" shiru yay yana kallonta da murmushi, "ina Alfaharin samun ka matsayin mijina Hubby" ta furta idanunta a d'an lumshe calmly ya furta shima hakan duk suna murmushi har lokacin kuma k'afafunta na akan jikinshi yana mammatsa mata,

"in dai tana son shi ina bata shawarar tay accepting na shi, shi matsalan dana fad'a tare dashi zata iya hana shi tunda yana sonta ba kamar kuma in sun zama d'aya" d'aga gira tay tace yana tunanin hakan is possible,

"yeah, ga misali nan akan mu" wani kallo tay mashi da rashin fahimta tace amman shi ai tasan bai abunda Sameer d'in yake ko, shiru yay yana mata wani kallo mai wuyar fassaruwa yanayin fuskar shi kamar zai murmushi itama murmushin take taji ya furta "ina nufin kaman yadda zaki iya hana ni abu koda ni ina so in baki so zan bari" wani kalan murmushin dad'i tayi had'i da lumshe ido tace "ai ba abunda zai maka wanda ni bazai mun ba, duk abunda kake so nima ina son shi Ya Handsome dina" yar dariya yay ya furta mata ya gode,

"Amman wai shi Sameer aikin mi yake?" gyara zama ya d'an yi kafin ya fara magana "yana da aiki mai kyau, shi Aerospace engineer ne" d'an yamutsa fuska tay ta maimaita sunan aikin nashi da ta maimaita tace "mi kenan?" Ce mata yay daga sunan tay guessing tayi shiru tare da d'an k'ank'ance idanunta tana son ta canka,

"Aerospace...Kaman ana nufin aeroplane ko?" ta tambaya tare da d'age baki, still da murmushi akan Fuskar shi yace "Yeah Kusan haka, shi engineer ne yana aiki da wani company a K'asar U.k, suna k'era jirgin sama ne bama shi kad'ai ba da wasu abu da suka danganci sama kaman satellites and rocket" zaro ido Fatuu tay a d'an rud'e ta furta "rocket kuma! ba itace mai kaman katuwar bindiga ba da in aka harba bullet d'inta ke fita kaman bomb ya tafi shuuuu yaje ya tarwatsa wuri??" dariya ta bashi yadda ta zaro idon yace mata eh shi wannan missile kenan shima rocket d'in ne, "Yanzu su ke had'a su?" Kai ya jinjina mata alamar eh kafin yace amman shi Sameer yafi experience sosae ta bangaren had'a jirgi don ya k'ware a kan haka shiyasa har wasu companies suna gayyatar shi aiki kaman a France da Germany, har nan US akwai wani Company da yake zuwa aiki a Washington, a nan Nigeria ma yana aiki da Ministry of aviation shiyasa akwai lokacin da yake d'an zama a Nigeria amman yafi zama a UK" jinjina kai ta shiga yi jin irin aikin da Sameer d'in yake can ta furta amman dai tasan yana samun kudi Haisam d'in yay yar dariya yace mata sosae,

"To amman kai ma kana samun kud'i kaman shi" wani kallo yay mata ta waro ido da sauri tace itafa hakanan ta tambaya tunda taga shima a K'asar wajen yake aiki, kawai sai gani tay yay d'an murmushi yace "tunda ina aiki ai dole in samu kud'i ko kawai kice kina son ki ji ni da shi waya fi samun kudi right?" Ya d'age mata gira ta d'an tura baki had'i da girgiza kai, sigh yay yace "kowa da kalar aikin shi so dole salary ya bambanta amman ta wani bangaren Kusan duk damar mu d'aya ne da shi kuma aikin namu suna da alak'a tunda duk sun danganci technology ne don akwae abubuwan da company d'in mu ke yi wanda suke amfanin da shi and nima kuma ina zuwa wasu Wuraren aiki saidai shi ya riga ni fara aiki abroad Saboda ni farko dana gama first degree na anan nayi aiki shi kuma tun daga School Company d'in suka zo suka d'auke shi nima tun lokacin an so a d'auke ni amman Dad ya hana don yana jin haushin yadda duk suke d'auke Mutanen mu masu hazaka a cewar shi hakan ne ya hana tamu K'asar cigaba kuma hakan ne, bayan naje yin Master's degree d'ina nan suka matsa na fara yi masu aiki amman dana gama sai Dad yace in dawo gida nan zan yi aiki lokacin sai na nuna masa interest dina kan yin aiki da su Saboda ina son bud'e Company shine ya amince amman sai na fara aikin anan, a lokacin nayi missing Hajiya sosae don tunda na tafi Karatu na bar wurinta haka dana dawo na fara aiki a Abuja sai dai in kawo mata ziyara har na sake komawa degree na biyu a lokacin tana kewa na sosae duk da bata fad'a man amman na sani duk na kawo mata ziyara in zan tafi sai naga idanunta sun canza ga kuma rashin mijinta da a lokacin yana damunta sosae wannan dalilin ne yasa na buk'aci canza wurin aiki nazo in zauna tare da ita......." dakatawa yay yana numfashi a hankali idon shi akan Fatuu da itama nata idanun na acikin nashi,

"........ashe zaman nawa wani babban Alkhairi ne zai same ni na had'uwa dake Baby, tunda kika shigo rayuwata farinciki na ya k'aru

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login